Showing 6001 words to 7525 words out of 7525 words

Chapter 3 - DIJEN ƘAUYE COMPLETE

Unknown   

29 Aug 2026

5

"toni !toni

ai har yanzu zafi fa nakeji.

Yayi kas!da murya yace "oh my zinariya baxan miki da karfi bafa, kinji.

Tayi lakwas alamun dai ta mika kai.

Nan nabarsu nafuce don su samu damar ci gaba da sabgar ma.aurata.

👍🏼😅

Akofar gidan Abdulhakim yayi f

arking din motar tasa yadire dije yana ce mata "zandawo nadaukeki da yamma Zinariya ki kular min da baby.

Ta rausayar da kai tace "yaya kabari sai dare mana kazo kadaukenin.

Ya girgiza kai yace "yanzunma dan zamuje meetting ne shiyasa nakawoki amma d

a babu inda zanje kinsan da direct gida zan mayarki bana so kidawo daga awo kitafi wani waje nafiso yanda aka luguiguita min babyn nan ace kinje gida kin kwanta kin sami hutu to amma yau kin dage wunin na mubina nane kinaga ita Abdul baya barinta yawo ko.

Tayi murmushi tace "ai ita kaga tayi nauyi da yawa kuma ita kadaice nikuwa kaga.

Shishsh!!yadora yatsansa akan bakinsa yana fadin "don't tell dis kema ke kadaice ai.

Tace "Ni,imar fa?

Ya mata wani kallo wanda ita kadai tasan ma.anarsa

Baika

ra cewa komai ba dai yaja motarsa yai gaba ita kuma tashige gidan

Tana shiga tahau tsokanar mubina "me tirtsin ciki gatanan tafe...

😃



Mubina datake jabe akan doguwar kujera da tsohon ciki tayi murmushi tace "wato naxama abin tsokanarki ko khadija.to

ai naga kema dai cikinne dake kuma dole zakizo gurin dan nasan nan da wata hudu kinyi nauyi kamar ni.

Dije tace "Allah mubina bana fatan cikina yakai naki girma.kinganki kuwa? Tab walh kinyi muni cikin yafi komai girma ajikinki shi ake fara hangowa kfn

aganoki sannu kinji ta gidana.

Mubina tace "to kekuwa nashiga EDD nafa harna kara kwana biyu.

Dije ta kama baki tace "tab kice yau ko gobe dai.

Mubina tace "yanxu ko anjima dai ko.

Dije takama baki tana dry "wai yakaga mubina zata haihu,

m

ubina tace "ainafiki juriya yarinya kinmanta yanda kk rude ganin zaki rasa mijinki Aiwalh gara da mukai mk haka gashi munga tsagwaron soyayyar da kk boye aranki.

Dije tahau dariya tace "ai walh kun shammaceni dayawa.

Mubina tace "amma dai mun iya had

a plan ko?

Dije tace "gaskiya kun iya tunda har kuka hana mijina shan Acid ba.

Mubina tasheke da dariya tace "bawani Acid daxaisha malama shima duk unset ne yafadane kawai dan yaji tabakinki.

Dije tace "toni koma dai miye anriga anwuce gurin tuni.

Mubina tace "hakane kam ta yaya Abdallah ina Ni,ima?

Dije tace "Tana gida daga

Awo nakefa yabiyo dani yawuce meetting

Mubina tace "to yayi ta yaya Abdallah kije kicin ki debo abinci ko.

Dije tace "keni cikina acushe yake banajin yunwa ruwa k

awai zansha.

Dije ta mike ta nufi furji ta bude ta dauko faro me sanyi ta tittila a cup tadawo ta zauna kusada mubina tafarasha

Sun wuni tare suna hirarsu ta kawaye anata hira ana tuna da ana dariya aiko dai mubina saiji tayi kamar ana zungurarta mar

arta ta daure tam! Ciwo yataho gadan gadan nakuda tayi sallama

Dije rudewa tayi jikinta yahau bari don bata san ya zatayi da mubinar ba

Kiran Abdulhakim tayi awaya har sau biyu bai dagaba suna meetting da wasu turawa a kamfaninsu wayarsa na silent

Momy ta kira ta shaida mata

Ai tuni momy uwa ta gari ta taho gidan mubinar da drevernsu yadaukesu sai asibitin da mubinar ke awo.

Cikin minti talatin Allah yabudi ido lafiya mubina ta zankado jaririnta katoto me kama da ubansa

Yaro fari kal kyak

ykyawa ubansa futuk

Dije tayi ta kallon yaron ckn so yabata sha.awa sosai taringa shafa cikinta tana addu.a aranta Allah yasa itama ta haifo me kama da Abdallah

dan hakan shine cinyewa gun mace awannan zamanin kahaifo babies me kama da ubansa

Me je

go lfy take dan haka aka sallamosu suka koma gida

Saida momy ta gyarae yarta tayi mata wanka ta gyara babyn sannan ta koma gida amma ta turo mata yar tsohuwar da take mata aiki iya zulai

Sai magriba suka fito daga meetting din abin yabaiwa su Abdul d

a Abdallah mamaki ganin test din Dije awayarsu wai Mubina ta haifi namiji

Adokance suka tafi gidan suna murna na samun wannan karuwa

Abdulhakim yaringa kallon dan ckn so wai yanzu wannan kyautar Allahn nashine?yaringa sumbatar yaron yana godiya ga Al

lah sannan yasa mubina agaba yana fada mata kalaman soyayya. "Nagode Mubee na kinbani farin ciki sunan mahaifina zansaka mahmud kizabi wanda za.a ringa ce masa nagodewa Allah dabaisa alokacin da dady yabanike na bujireba ashe akwai rabo atsakaninmu ina son

ki My mubee Allah yakara mk lfy da nisan kwana agaba ki haifo mini "ya"ya tara insami goma ma aduniya.

Tarufe fuska tana murmushi tace "Amin Abban Abulkairi.

Itako dije jikinta yagama sanyi ganin yanda ake nakuda tabbas mata suna kokari

Amota suna

tafe Abdallah yana tayi mata sambatu "My Zinariya kyanta ki haifomin namiji kema kinji walh babyn nan yasamin son da namiji araina plz Khady na

Ido kawai tabishi dashi batada bakin magana tunda sambatu yakeyi

Yama mance ba itace zata bashi namijin

ba Allah ne

Da taga da gaske yk ne sai tace dashi "Yayan love kayi addu.a Kawai.

Yace "yakamata kiyi scaining ko ?

Ta girgiza kanta "basai nayiba yaya mubarwa Allah lamarin kada muyi masa shishshigi.

Ya gyada kai kawai.

******

Wata hudu da

haihuwar mubina knn Abulkairi yayi wayo alokacin Dije ta haihu Allah cikin ikonsa ta haifo tagwaye duka maxa kuma batasha wani wahala ba wajen labour ckn mintina twins suka zo duniya

Yara gwanin sha.awa kowa sonsu yaringayi tun daga asibitin farin jinin

su ya watsu farare tas kamar "yayan larabawa sunyi kama da babansu shikansa Abdallah saida yaringajin wani annashuwa aransa yaita godiya ga Allah aransa da bayyane

Aranar suna kuwa canza musu suna yayi yasakawa hassan suna Abdulhakim little hussain

kuma jiniour Abdallah

Haka yaran suka taso da farin jini sosai Ni,ima ma tana nuna musu kauna me aikinta ke daukosu takawo matasu kokuma dijen takai matasu har part dinta su

Wuni tare

Alokacin kuwa da suka isa yaye momy ce ta karbesu ta yaye su ag

idanta

Dije hankali yakwanta mijinta na nuna mata soyayya gashi inda yakara burgeta yakara saka sonsa aranta Abdallah mutum ne domin yaje can kauyensu yahada matasan garin da basuda aikinyi yabasu aiki a gidan gonar dady da aka yanki gefe yayi floti b

iyu aka bude kamfanin shinkafa gashi yaja wuta garin yayiyyi rigiyoyin burtsatsai da fanfuna ko ina kayi saidai kaji ana shi masa Albarka tabbas kayen marina suna alfahari da Auren dije da Abdallah

Don Yamayar da kauyensu

Birni ya haskaka musu karkar

a koina fitilune ahanyoyin da ake shirin futar musu da tituna

Su littel da junior sunada shekara uku daidai dije ta haifi "ya mace wanda ita kuma kama tayi da ita futuk daka ganta kaga "yar fillo zam.

Abdallah yaso yasaka wa diyar tashi Sunan mar

gayya Zannura to sai Dije tace itakam magaji da rai zatayi Ni,ima take so asakawa Babyn

Baiki tatan ba tunda Abin alherine hakan Ba.a boye mataba kumma Ni,imatullah akece mata

Ni,ima naji da takwara sosai agunta take wuni wani sa,ilin ma intaji shi

ru kafin akawota da kanta take dingisawa taje ta gano takwara

Bayan shekara biyu Dije manyan mata ana zaune ana koyawa Ni,ima baby fullanci Abdallah yashigo da twins sukayo kanta suka daneta "momy oyoyo mundawo sannu da gida.

Ta hade rai tana turarsu

"kada ku ballani mana meye hakan.

Littel Yahade rai yace "gaskiya momy muma kiringa koya mana fulatancin nan kullum saidai muji kina yiwa baby bandamu.

Abdallah yakaraso ciki yana musu dariya dijen ma dariyar takeyiwa littel ganin yana nuna kishins

a karara akan Baby Ni,imar wacce bakinta ma baibude sosaiba

Abdallah ya daga mata gira "kibashi amsa mana kinyi shiru nima ina kishi da hakan fadane banyiba yarigani ne kawai.

Tayi dariya tace "to ya kuke so inyi daku nagadai kaima gaba kake sasu kan

a koya musu turanci ko gayyata ta bakwayi toni meye aibuna da abin kishi dan na koyawa diyata fulfulde.

Abdallah yace "mudai munji munki wayon dole muma ahada damu akoya mana ko mu rigime tunda ai babyn ba yarenta bane yaren mamantane.

Dije tayi dar

iya tace "Amma dai kasan itace asalin *"YAR FILLON* KO? KAMMANNI sunnuna komai nata na Dijen kauyene.... yatoshe mata baki "kul! Dijen Abdallah kike ba dijen kauyeba plz mubar maganar nan ma mudawo ta batun abinda nake muradi agunki yaushe zanbaki ajiyata

ne?

tayi kamar bata fahimtaba tace "meke nan?

Yashafa cikinta "Inaso ahaifarmin Zannura ne

ta kanne ido daya tace masa"kasha kuruminka takusa zuwa ma.

cikin murna yace "da gaske?dama nabayarma ashe ba.a gayan ba. Yakai mata sumbata agoshi

ta

nuna masa yaran dake gefe suna sabgarsu tace "Dadyn love yara fa ka ankare plz.

ya fakaici idon yaran ya sunkuceta yayi bedroom dinsa da ita ……………

🖐🏻👏🏻😃

asha love lfy masoya Allah yabar so da kauna Dije da Abdallah.

*Auntyn Sayyad

a da Shahida ce*

👌🏼

1
2
3

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login