Showing 78001 words to 81000 words out of 237425 words

Chapter 27 - ZAKI COMPLETE

ga kayan aiki a take aka hau bata taimakon gaggawa, shi kuma ya kasa tsaye ya kasa zauna sai da ya ga an fito da ita daga dakin an kaita wani dakin an sak

a mata oxygen an saka mata wata allura a hannu, komai likitocin ne suka mata ba kamar nan da ake cewa mutum ya dauki mai jinya yaje ya kaishi a masa hoto ba, su da kansu suka dorata a wani gado suka kaita wani dakin aka dauki hoton jikinta gaba daya sannan

aka dawo da ita wani likitan ya shigo ya debi jininta ya fita. A lokacin ne Aliyu ya samu natsuwa har ya kira Mama Fulani da Ammy da kuma Momy ya fada musu kamin ya kira familyn Rahma su ma ya fada musu. Zauna yai kusa da ita ya kai hannunsa yana shafa fu

skarta dayan hannunsa kuma cikin hannunta yana murzawa a hankali, kallo daya zaka masa kasan yana cikin tashin hankali rudani da tsoro a lokaci daya.

Ba ayi minti talatin ba sai ga Mama Fulani da Ammy a asibitin sun zo, hankalin Mama Fulani ya fi tashi

fiye da na Ammy ita kuma ba dan Rahma ba sai dan Aliyu da ta san zai tashi hankalinsa saboda Rahma, domin shi Mama Fulani take kallo ba Rahma ba.

“Jiki ai da sauki”

Mama Fulani ta fada.

“Eh da sauki gaskiya tun da yanzu sun saka mata oxygen zata

samu saukin numfashin, kuma sun mata hoto ko minene za su ga ni ai”

Ammy ta ce.

“To wai miya faru ne da ita?”

“Wallahi ban sani ba, ina komawa gida na same ta a dakinta kwance kasa ta dafe cikin tana daukar numfashi”

“Allah ya sauwake"

“Ami

n”

Ya amsa yana picking din calling don da Mommyn Rahma ke masa, cikin sautin kuka ta ce.

“Fada min addreshin asibitin ga kanwata nan da take Abuja zata zo ta duba mana jikinta”

“Jiki da sauki fa ta samu bachi ma”

Haka ya fada sannan ya fada m

ata inda asibitin take ya kashe wayar, sai ga wani likita ya shigo ya ce duk su fita basa son ganin kowa akan marar lafiyar, daman a ka'idar asibitin ba a aje mai jin marar lafiya su suke masa komai ba a kwana a asibitin da sunan jinya suna da nurses da su

ke kula da marar lafiya da ko mai jinyar ba zai iya kula da shi haka ba. Gaba daya suka fito daga dakin suka bi bayan baturen likitan zuwa office dinsa domin ya fada musu yana son magana da iyayenta ko mijinta, a lokacin da suka shiga office din sai suka s

amu ba likita daya ne a ciki ba, likita biyu suka tarar yan Nigeria bayan wannan baturen da suka shigo tare da shi, a bayan teburin likitocin an laka wani katon majigi mai kamar kwanfuta an laka wasu hotuna a jikin abun. A visitors chairs suka zauna shi ku

ma likitan ya nufi inda computer take ya cire hotunan jiki ya dauko wasu ya laka da wani dan pen na hannunsa ya nuna musu inda matsalar Rahma take yana musu bayani da halshen nasara. A bayanin da likitan yai da wanda sauran likitocin sukai babu wanda Aliyu

ya fahimta, ba dan baya jin turancin ba, sai dan jin abun wani banbara gwai, wai kodarta ta kone as how kodar mutum zata kone? Ba ma lalacewa ba? And duk duka yaushe aka saka mata kodar da za a ce ta kone? Gaba daya rikecewa yai ya tashi ta sauri ya fice

daga office din ba tare da ya jira likitan ya gama bayanin ba.

Ammy ba ta wani dade asibitin ba bayan likitan ya gama musu bayani suka fito suka samu Aliyu tsaye a waje duk ya bi ya rike kamar ba shi ba, shi kansa ya san Allah kadai ya iya haka, ace ko

da ta kone, gashi kodar ce daya ta rage mata wacce aka dasa mata sai kuma ace ta kone, kamin ma ya samu wata aiki ne, and ba zai zama ace ko da yaushe sai an dasa nata koda ba idan an samu wata rana ba za a samu ba. Mama Fulani ce ta tsaya da shi tana ta b

ashi magana tana kokarin kwantar masa da hankali, har wata kanwar mahaifiyar Rahma ta shigo taje ta duba, yasan dokar asibiti ba a kwana da sunan jinya amman a haka ya karya dokar ya zauna a kujerar ya saka matarsa a gaba yana ta kallonta hannunsa cikin na

ta, ji yake kamar ya cire ta mata ciwon a take ta tashi, jikinsa nata raya masa mutuwa za tai ta bar shi, and all what he was thinking idan ta mutu ba zai iya rayuwa ba, taya ma zai rayu babu Rahma? Haka ya saka ta a gaba yana ta kallo, misalin 12 ya aikaw

a Nasir da sakon abunda yake faruwa, da Nasir ya kira shi kuma sai ya kasa dauka, sai kallon wayar yake gaba daya ya rike ce ya rasa inda zai saka kansa, gaba ya saka ta yana ta kallo har garin Allah ya waye, bachi be leka idonsa ba ko da wasa. A wani masa

llaci dake nesa da asibitin yai sallah asuba gaba daya addu'arsa Rahma yai ma, daya fito daga masallacin sai ya zauna cikin motar ya kifa kansa jikin sitarin motar yana ta sauke ajiyar zuciya idonsa na masa mugun nauyi. kiran Nasir ne ya shigo wayarsa amma

n ya kasa picking har tai ringing ta katse aka sake kira, gaba daya kasala yake ji yana jin shi ma kamar ba shi da lafiyar. Sako ya turawa Nasir na addireshin inda yake, sannan na kwantar da kujerar ya lumshe idonsa, cikin mintunan da ba su fi ashirin ba N

asir ya iso gurin, babban masallaci ne amman hakan bw hana shi gane motar Aliyu ba, domin irin ta bata da yawa a garin Abuja. Yana bude motar Aliyu ya bude idonsa da suka kada sukai ja yana kallonsa.

“Ya jikin nata?”

Aliyu yai shiru be ce komai ba s

a yawo yake da idonsa kamar marar gaskiya. Nasir ya dafa shi.

“Aliyu ka kwantar da hankalinka...”

“Wane irin na kwantar da hankalina? Kodar ta fa aka ce ta kone, ko baka gane ba?”

“Na gane, amman me likitocin suka ce?”

Aliyu be ce masa komai b

a, ya jinginar da kansa jikin sitarin yana sauke ajiyar zuciya. Can kuma ya dago ya kalli Nasir.

“Saboda kodar nan ta zalinci ce ko? Shiyasa ta kone? Ko kuma saboda Ataa ta ce ba zata taba amfanar Rahma ba? Ta mana Allah ya isa fa”

“Gaskiya ne Aliyu

zalinci kawai ba ban da addu'ar da tai muku ta isa ta saka wani abu ya faru, domin ita wacan da aka cirewa ba mu san halin da take ciki ba....”

“What if na bata hakuri?”

Nasir yai saurin tarar numfashinsa.

“Karka tinkareta kai tsaye yanzu tun tun

i ya kamata kai wannan kuma ba kai ba”

“No baka san yadda nake ji ba ne a yanzu Nasir, bana son na rasa Rahma”

“Ai ba cewa akai zaka rasa ta ba, amma

...”

“No hakuri zan bata Nasir”

Ya fada yana jan murfin motarsa ya rufe. Cikin saurin Nasir y

a nufi tashi motar ya shiga ya bi bayan Aliyu.

ATAA POV.

Na tashi da safe da zazzabi da kuma rashin kuzari, dukan abunda ya faru jiya sai ya zame min kamar mafarki ciki kuwa har da maganar da Muhseen yai min. Bayan na gabatar da sallah asuba

na dauki jakata na nufi garden na shanya duka kayana da suka jike sannan na shiga part din Mama Fulani na fara gyara falon, na nufi dakin Ammy na gyara mata nata falon, ina cikin saka air freshener na ji tana fadin

“Jiya ba ki dawo karbar abincin dare b

a, ko da mun fita asibiti amman ni da wuri na dawo saboda Alhaji”

Abubuwa ne suka zo min a rai, zancen Alhaji na san tana da mijin da suke taraiya ita da Mama Fulani domin wani lokacin ina ganin yadda suke kokarin shirya abincin ko wani abunda ya ke nun

a mijinsu suke yi ma amman ban taba jin zancensa a bakinsu ba, haka ma a gurin yayansa, ban taba cin karo da shi ba, fitar da shigowarshi duka ban taba gani ba, da wace motar yake fita ko yake shigo cikin gidan ban taba sani ba. Sai kuma zancen zuwa asibit

i waye ba lafiya? Kamar ta san abunda na ke sakawa a raina sai na ji ta ce.

“Matar Aliyu ciwon ya tashi Wallahi”

Da sauri na kalleta.

“Miya ke damunta?”

“Wai ciwon koda ne daman tun tana karama haka take har ta girma, to sai daga bayan kododi

n duka biyu suka lalace, daker aka samu wata aka siya aka saka mata a waje, yanzu kuma wai kodar ta kone, Wallahi ni yarinyar har tausayi take ba ni wannan jarabawar rayuwa”

Wani yanayin na ji, shi ba dadi ba shi kuma na bakinciki ba, a take na girmama

Allah a zuciyata lallai sakamakon zalinci ba mai kyau ba ne, koda ta kone abunda ban taba ji ba, sai dai na ji ance ta lalace amman wani iko na Allah yau na ji ance ta kone, lallai Allah ba azzalumin kowa ba ne.

“Lafiya?”

Ta tambaya ashe kallonta na

ke ta yi tun dazu ni ban ma sani ba. Har na bude baki nai magana sai muka ga an turo kofar falon an shigo, Kamal ne fuskarsa dauke da murmushi yana sanye da uniform din sojoji sun matukar karbarsa abun ka da dogon mutum sai yai kyau da kakin kamar yadda na

ganshi a wacan karon. Ledar jiya ce a hannunsa kai tsaye ya nufo inda nake yana gaisawa da Ammy da alama ya saba shigowa gidan, domin ita ma naji tana masa korafin ya daina zuwa kwana biyu kamar yadda Mama Fulani ma na ji tana masa.

“Wallahi aiki ne y

ai min yawa, yanzu ma kaduna zan je da safen nan sakon kawai zan bawa ba Mamar nan taki”

Kallonsa kawai Ammy take har ya karaso kusa da ni ya mika min ledar.

“Ga kayanki nan”

Tsayawa nai kallon ledar kamar mai shawarar karba, sai ya aje min ita k

asa yana kallon agogon hannunsa.

“Zaki bata min lokaci ko? Na shiga can a aka ce kina nan”

Juyawa yai ya nufi kofa yana yi ma Ammy sallama da kallo na bishi har ya fice sannan Ammy ta kalleni tana dariya ta ce

“Ina kika san Kamal?”

“Ranar na f

it gate shine ya kira na ce masa nan nake, sai kuma da muka fita da Anty Rukaiya shine ya ce na raka shi mu yi siyayya”

“Ok shine ya kawo miki na ki tsara? Tooo lallai yarinyar nan ashe ko ko zai janyo miki rigimar Maryam, saurayinta ne fa”

Na wara i

do.

“Da gaske?”

“Eh yana dan zuwa gurinta can ba a rasa ba, yau kuma ya dawo gurinki? Oh Maza akwai iya son mata”

Ta fada tana dariya ni kuma na nufi inda na dauko turaren na aje sannan na dawo na duka na dauki ledar na fito daga part din na nufo

gareji ban tsaya duba komai ba aje kawai nai na dawo part din Mama Fulani dan karasa gyaran kamar yadda na saba, ko da na shiga ita da yayanta suna dinning suna karyawa, fuskar Anty Maryam ta kumbura sosai har gurin idonta daya ya rufe bata iya gani da ky

au da shi, wata kila marinta Aliyu yai ta yi ko kuma wani abun ya buga mata a fuska oho, ni dai kallo daya nai mata na dauke kaina na shiga dakunansu na gyara ko'ina na wanke bandakunan sannan saka turare Awwaba na fito na sauko kasa.

“Zo ga abincinki

ki dauka”

Ya Muhseen ya fada yana aje min plate din a gefen taburin. Sai da na karasa kusa da shi sannan ya kalleni

“Ya jikinki? Na manta jiya ban saka miki kada ba amman ai baya jini ko?”

“Eh ba ya yi”

Na amsa shi jikina nata rawa domin na lu

ra da yadda Mama Fulani take watsawa Muhseen harara shi kuma be ma gani ba, gaba daya hankalinsa yana gurina, da sauri na karbi abinci naje na zube a plate dina na kawo masa sannan na dawo garejin na zauna ina cin abincin ina duba kayan da ke ledar, kayan

da ya siya min ne jaya turare da auduwar mata da man goge baki sai kuma chocolate da biscuit mai madara. Ina jin lokacin da motoci har biyu suka tsaya a harabar gidan, ni dai ban leko ba domin ban damu na san ko suwaye suka zo ba, a cikin jaka ta na saka m

an goge bakin da sauran kayan biscuit din kuma na aje shi a saman katifa ta da zimmar idan na dawo na ci, sai na dauki plate din da cup na nufi garden dan wankewa, ina cikin wakewa na ji kamshin turaren Aliyu da sauri na waigo sai na ganshi tsaye yana ta k

allona cikin yanayin da ke nuna yana cikin tsananin damuwa. Ni ma tsayen nai ina ta jiran na ji idan wani abun zai ce min amman be ce komai ba, ganin hakan yasa na juya na cigaba da wanke plate din sai na ji motsinsa a bayana daf da ni. Mikewa nai tsaye in

a kallonsa, sai ya bude ba ki kamar zai yi magana sai kuma ya kasa cewa komai. Daukar plate din nai zan wuce sai ya kira sunana.

“Ataa... ”

Sai na tsaya a tunanina wani abun zai ce na masa, sai kuma yai shiru be ce komai ba ya kawarda fuskarsa yana

hade yawu, da alama wasu kalmomin yake hadawa ko kuma yana saka abunda zai ce min ne.

“Matata Rahma bata da lafiya.... ”

Sai kuma yai shiru ya dawo da dubansa a kaina.

“Ataa na san ba a kyauta miki ba am.... ”

“Sai yanzu ka sani? Saboda kodar

matarka ta kone ko? So kake a sake cire ta mahaifiya a saka mata?”

Ya girgiza min kai alamar aa.

“So na ke na baki hakuri”

“Kana tunanin Hakuri zai canja zalincin da aka min ne? Kana tunanin hakuri zai saka Rahma ta tashi a take ne? Ko kuma kana

tsoro kar matarka ta tafi ta barka ne ka dandana zafin rashi kamar yadda na dandana na rashin dan'uwana saboda kai? Ko tsoron jinya kake kamar yadda nai ta mahaifiyata? Har ka fara tsorata da abunda ya samu matarka tun yanzu? Likitoci sun fada maka zata ra

yu ko ba zata rayu ba? Ai kana da kudi sai mu gani idan kudinka za su tare mata mutuwa, ko kuma za su sama mata lafiya a take, ko da yake za ku iya neman wani talakan marar gata irina ku cire masa kodar ku saka mata ita ta rayu”

Duk abunda na ke fada ma

sa be ce min komai ba, wani abun mamaki sai ma cika da idonsa sukai da kwalla. Wani mutum ne ya shigo garden din wanda ba zai wuce sa'ar Aliyu ba ya karaso kusa da inda muke tsaye yana ta kallo.

“Ke ce Ataa?”

Na kalleshi

“Wani ya baka labarina ne

?”

Sai ya kalli Aliyu ya sake kallona.

“Sunana Nasir ni abokin Aliyu ne kuma Aliyu ya fada min komai akanki, Ataa mun san an zalince amman....”

“Amman me? Amman ba ku gane ba sai yanzu? Ya kasa jure abunda ya same shi ko? Ni na jure jinyar mahaify

arta da kallon halin da take ciki har na tsawon wata daya da wani abu a asibiti, kullum ina ta zullumi zata mutu ko ta rayu? Ban sani ba, yanzu haka mahaifiyata tana can gida na baro ta na zo nan aiki saboda na sama mata kudin magani, wata kila ko da zan k

oma ta mutu, ko kuma rashin lafiyar ta kara tsanani, tun da na baro garin ban sake jin muryarta sai dai idan na kwanta nai mafarkinta? Saboda abunda mutanen nan suka min, har yau bata san cewa an cire mata koda ba, da wane ido zan kalleta na fada mata? Su

wa zan ce suka cire mata? Har yau mahaifiyata bata san gaskiyar ciwonta ba bata san komai a kai ba, kun jefa rayuwata cikin damuwa da bakinciki, amman duk ba ku gane ba sai yanzu da Allah ya jarraba Rahma na dan lokaci, sai ka kasa jurewa? Miye amfanin zuw

a da kukai a nan? Na yafe muku? Ko kuma na fada muku Rahma ba Zata mutu ba? Kun cutar da ni Wallahi babu wani dadi bakin da za ku min na yarda da ku, za ku iya cilata ni yin komai saboda ina talaka amman ban da yafiya, ba zan taba yafewa ba.... ”

Na kar

asa cikin kukan dana fara tun dazu sannan na nufi hanyar fita dGa garden din har bana iya gani da kyau saboda hawayen da suke min zuba.

ZAKI

By Khadeeja Candy

26...

Duk kokarin Kamal na rike ta kar ta kai kasa be saka ya iya taro ta ba har sai

da ta kai kasan, be san abunda ya faru ba amman tabbas ya ji karan mari a lokacin da ya kawo bakin kofar falon da zimmar shigowa kawo ma Ataa tsarabarta. Gaba daya falon yai tsif Husnat da Siyama suna ta mamakin zafin rai irin na Fulani, Maryam da Rukaiya

kam abun dadi yai musu daman ko su ne za su iya yi mata haka, sai dai suna tsiron kar Aliyu yai musu ba dadi amman idan Mama Fulani ce babu abunda zai yi. Momy ta girgiza kai tana kallon Ataa cike da tausayawa domin ta san ba lallai sai ta yi ma Mama Fulan

i wani babban abu zata yi mata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login