Showing 3001 words to 6000 words out of 20825 words
gun kasuwa
Inasan dukiyata takaita gashi nasamu cikin sauqi
Lantana tace wlhi itace Larai nima yakubu yace inyadawo zaiban ita
Tace Allah ya kawo shi
Haya gagan dakeyi shiya fito dasu hassana da mairo matan qannan baban Nafisa
Kae Larai kina ca6awa yarinyarnan tana kawo miki azziqi dama nice inji hassana
Mairo tace bani ingani
Larai tace aiwannan dubun hannun Masu qashin harziqi take zuwa. Bakeba
Nan mairo taja gefe dan tasan Larai tas Ba mutuncine da itaba
Duk da Nafisa tabata muhimmin ku'di saida ta rankwasheta
Abin baqinciki sae yanzu zatayi sallar asuba
Nan Nafisa tashige gun babanta tana jiran Larai ta dama koko tafita talle Dan Allah Allah take tafita dan taqara ganin MARWAN da Amar
πππ
'YAR QAUYE KO 'YAR BIRNIπππ
Har Nafisa tasiyar da kokonta bataga Su MARWAN Ba
Ahanyarta tadawowa ne tayi tunanin shiga gun Hajjiya wato agidan megari
Da sallama tashiga
Hajjiya dake alwala ta'amsa mata cikin fara'a tace
Kaga nafisatu yau ansiyar da koko lpy ko
Tace eh nazoma ganin larabawan nanne
Hajjiya tace suwa kenan
Tace Su ambar
Yanzu Hajjiya tagane suwa take nufi
Yayi murmushi tace
Suna 'dakin Adamu
Da sauri tature tiran tallan tafallah da gudu 'dinkin Adamu
Hajjiya tabita da kallo tana addu'ar Allah yasa Amar yasota danko tunanin MARWAN batayiba
MARWAN da Adamu suna hirarsu ta'yan uwa
Amar na'dakin amma Sam yaqi kulasu wae adole fushi yake da MARWAN
Har fushin yashafi Adamu
Saiji kawae sukaji ana kwankwasa kofa
Adamu yace waye tace nice Nafisa
Tunanin Adamu ko Hajjiya CE taturota shiya shi cewa to kishigo
Tamur'da kofar taqi buduwa. Dole sanda yatashii yabu'de mata
Bajin ko 'dar taratsashi tahuce tazauna kan kafet Adamu yabita da kallo
Tace sannunku
Amar yace yauwa sannu Nafisat
Tace wae meyasa kuke canjamin suna ne.
Cikin 'dan waro ido ka'dan Amar yace
Waya canja miki suna
Tace kaga Hajjiya nacemin Nafisatu kae kace min Nafisat
Wannan tanuna MARWAN Wanda tunda tashigo yake kallan yana kissima abubuwa da dama acikin ranshi
Yana kirana da FEENAH
Amar yace to wanne ne aciki yafi miki da'di tace FEENAH
Yace gud kinza6i Wanda yadace tace
Yauwa nasan FEENAH yafi da'di yace hakane.
Yauwa baba Larai tadakeki kuwa
Tata6e baki tace rankwashina kawae tayi
Dan naci darajar kudin dakaban yace Allah.
Tace wlhi
Yace yanzu me kikazo yi tace nafito tallene shine da nasiyar nace sae nazo naganku
Yace ayya sannu FEENAH mungode sosae tayi dariya tace kaima kadena cewa Nafisat ne yace eh tunda naga kinfisan FEENAH tace to ai kae Nafisat yafi da'di abakinka yace ko tace eh yace to kinfisan ya MARWAN yakiraki da FEENAH tace eh dan abakinshi yafi da'di
Da sauri Amar da Adamu suka kalli MARWAN
Amar yace am sorry Yaya kakar6ita plx
Adamu yace wae ya'ayi kukasan Nafisa
Tace jiya suka sanni
MARWAN yaja tsaki
Quri Nafisa tayi mishi da ido tana cewa
Me yasa meka kake tsaki yadalla mata harara yace bansani Ba
Cikin rashin damuwa tace aidama kae da ganinka zakayi fa'da
Zaiyi magana Amar yayi saurin cewa tashi muje inrakaki takama baki tace yauzan zama abin kallo aqauyan nan
Yace meyasa
Tace saboda zanyi tafiya da balarabe
Dariya yayi yace to tashi muje tatashi sukafita.
MARWAN yaqayin tsaki Adamu yace yayane yayah yace
Kaduba shashanci irin na yarannan wae saidae Lalle na auri yarinyarnan
Cikin mamaki yace
Haryaushe kuka santa dahar zaima maganar auranta yace ohofah
Hajjiya ganin Amar da Nafisa sunfito sae abin yabata Shaw'awa tace yadae
Yace zan rakata gidane tace to saikadawo suka fita
Suna tafiya Nafisa tace gaskiya kanada Kirki yace ko
Tace eh
Yace kidena lefin da za'adinga dukanki kinji tace to dae dae nan suka iso
Yace toni natafi tace sae Naji banasan rabuwa dakai yace ko tace
Allah yace kinga dole murabu dan gobe ma zamu tafi
Ta waro ido tace zakuta gobe shikenan bazan qara ganinku ba yace eh
Tace dan Allah karkata kae
Yace dole natafi nafisat dan inada karatu.
Sae dae inzaki bimu
Tayi dariya tace
Yaushe zanbiku nabar babana
Kumama baba Larai bazata bariba
Yace to in babanki yace kibimu zaki bimu tace eh zanbiku amma sae dae inza kusani a makarantar boko
Kuma innaga babana ya warke
Yace OK nina tafi
Ta'daga mae hannu
Yatafi Yana murmushi
Koda Amar yatafi zuwa yayi ya'ibi ku'di tare da 'daukar mota
Ba'inda yasauka sae gidansu Nafisa
Yace ma babanta yazo yakae shi asibiti ne
Dan aduba lafiyar Sa
Baba yayarda Amar yatafi dashi
Lokacin Nafisa tafita tallan shinkafa da wake
Baba Larai kulewa 'daki tayi Dan acewarta Amar ba mutun bane
Sunji asibiti anduba baba antabbatar da ciwan da yake daminshi
Sunce hawan jinine amma bae shiga jikinsa sosae danhaka zasu bashi magani yasha natsawan wata 'daya
Nan Amar yakar6a mae maganin suka tawo
Akan tanyarsu tadawowan yasiyama baba katifa da kafet tare da situru.
Baba sae samishi albarka yake
Haka suka dawo gida
Yasa yara suka kwashe tarkacan 'dakin suka saka kafet da katifar. Sannan yamae da baba 'dakin
Yanata samae albarka
Yatafi
Nafisa CE Mae tafiya kan hanya tanata wawakenta tana tsalle tasan yau baba larae zata bata abinci taci San ranka dan tasae da shiinkafa da wake
Ke Nafisa ke Nafisa
Taji qawarta Fatsima na kiranta
Tatsaya tana dariya
Fatsima tace naganki sae murna kike ko kinsiyar da abinci ne tace eh nasan yau zanci abinci na qoshi
Tace hakane fah
Kinsan meye tace aa
Wae ya'u ne yake suna za'amana aure dashi
Tace Lalle kice zandinga zuwa gidanki muna shan hira tace
To aini bana sanshi kwata kwata
Tace to wakike so tace bakowa
Tace tab kinajin da'dinki ne shiyasa
Dae dae nan sukazo wuccewa ta wani lungu
Aifa sae sukaga
Lanta da yakubu saurayinta suna iskanci.
Kasan cewar Sam mutane basu damu da sama lungun idoba shiyasa har za'ayi abu alungun agama mutane basu ankare Ba
Yakubu yadanne lantana yata iskanci da ita.
Nafisa tace lantana me yakubu yake miki
Nan suka tsaya da jan kaya
Lantana tace bansani
Kuma wlhi kika fa'da sainaci ubanki kema Fatsima kifa'da kisani.
Fatsima tace saina fa'da 'din aini ba Nafisa bace nasan abunda kukeyi itace bata saniba
Tace to kifa'da inci uwarki
Tace kici uwarki Larai dae
Taja hannun Nafisa sukabar gun
Nafisat tace iskaci sukeyiko
Tace eh man
Nafisa tayi mamakin ganin 'dakin babanta fes tatan baye shi yagaya mata komae
Nan tahau murna
Su hassana da mairo ma suna santin 'dakin amma baba larai cewa tayi bazata shiga 'dakinba Dan 'danshan jinine Amar
Nafisa tace jikokin me garine fah Babah
Babanta yace shareta Nafisa
Larai tace eh tasherenin sae me kwa'dayayye kawae yace nine kwaa'dayayye tace kai'dinfa yace Lalle rashin mutunci nake yakai inda yakai
Tace har ya hucce
Yace wlhi Larai kikiyayi ranar dazan tashi
Tace ai'in Allah yayarda bazaka tashiba haka zaka qare rayuwarka
Bae kulata ba
Dan kallan mahau kaciya yake mata
Nafisa tace kayi hakuri baba yace Ba komae kidae kidinga min Addu'ar Allah yabani lpy tace to Allah......
Bata qarasaba taji am maka duka da takalmi abayanta.
Qara tasake tare da miqewa agigice
Baba Larai CE
Tace harda cewa yayi hakuri yarinya dake kin'iya makirki
Tace kiyi hakuri
Tace zoki 'dau cincin kifita
Nan ta'dauka tafita tana kuka
πππ
Washe gari Su MARWAN sun gama shirinsu natafiya
Amar yace kakale baqo zaiyi halinsa tace wlhi bansan rabuwa daku
Yace to ya za'ayi dolene ai
Kinga ana leman yah MARWAN gun aiki.
Nikuma karatu
Tace to kugae damin da kowa.
Naha'dama Momyn taku kayanta suna mota
Amar yace kae matarnan yanzu zaki cikamana ciki da warin daddawa
Tace eh jiyama kacita ai yace inani inacin daddawa
Nan suka rabo cikin jin da'di
Akan hanyar sune Amar yayi parking kofar gidansu Nafisa
MARWAN yace lpy.
Yace kayi hakuri mushiga gidan kugaisa da baban nata tunda yanemi alfarmar hakan
Baice komae ba yafito daga mortar
Amar ya kunkusa kofar gida.
Nafisa na wanke wanke baba Larai tace ke jeki duba kiga waye
Tace to.
Ganin datayi Su MARWAN ne shiyasa koma da gidu cikin gidan
MARWAN yakalli Amar shima yakalle shi
Yace tunda takoma sae mushiga mutafi ko
Amar yace ila taje gayama....
Bae qarasaba sae gata
Tace ina kwananku
Amar ne ya am'sa
Yace kinfito kuma kinkoma da gudu tace
Naje gayama babane kunzo
Yace kushigo.
Nan suka shiga
Taje taci gaba da wanke wankenta
Baba Larai bata guduba wannan karan ba amma ta la6e kofar 'dakin tana sanjin me za'a fa'da
Baba ya musu sannu da zuwa
Suka gaida shi.
Yace nagode sosae da temakwanku garuni da 'diyata
MARWAN yace bakomae
Amar yace dama zamu koma gidane yanzu yace ayya kano ko yace eh
Yace yanzu ku yaran Abdallane suka eh
Yace ikwan Allah
Allah ya albarkaci rayuwarku
Ameen MARWAN yace
Baba yace yanzu yaushe zaku da'da dawowa Amar yace ai sae kunganmu kawae
Yace Allah yasa muqara ganin juna sukace Ameen
Baba ya tsaida kallanshi akan Amar yace dama inasan rokwan alfarma agunka. Yace to inaji.
Yace inbazan takura kaba inasan ka Auri Nafisa dan tunda naganka naji kashiga raina kae da 'dan uwanka.
Nasan Kaine zaka riqe Nafisa amana
πππ
'YAR QAUYE KO 'YAR BIRNIπππ
Tarine Yakama Amar bai shiryaba yayi saurin kallan MARWAN yaga yana murmushi alamar irin yashiga annu
Murmushi shimah yayi yace ai baba ya MARWAN yarigani shine yakesan Nafisa yanzuma munzo wajankane da magana
Tab....
MARWAN yace azuciyarsa amma Sam bae yarda ya'dago kansaba
Da murna baba yace ato aishi kenan wlhi nabaka Nafisa halak malak
Idan naji sauqi zanje gun megari da kaina
Amar yace basae kasha wahalaba zasuzo da Kansu
Yace to Allah ya kawosu
Yace Ameen
Nan Amar yace to zamutafi
Yace to Allah ya kiyaye hanya
Ya ajiyemae ku'di yana cewa kakula da shan maganin insha Allah zaka miqe
Yace to nagode sosae Allah yayi albarka
Yace amin
MARWAN yayi mamakin yanda dazasu fita yabi Nafisa dakallo
Itama tayi mamaki
Amar yayaficuta da hannu
Nan tsame hannunta
Tabiyosu
Kuda tafito wajan tuni MARWAN yashige Mota.
Amar yace zamutafi tace shikenan bazan qara ganinkuba
Yace aikinzama tamu tace meyasa kace haka
Yace haka kawae
Tace to yanzu yaushe zaku dawo
yace ila
In baba yagama yagama shan Magani
Tace to Allah yakiyaye
Taleqa cikin mutar tace ya MARWAN Allah yakiyaye
Da Saudi Amar yajata
Dan yasan ka'dan da aikin MARWAN ya falleta da mari Dan yacika yayi fam qiris yake jira ya fashe
yace munyi latti Nafisa
Tace to ai banyi sallamah da ya MARWAN Ba yace kunyi saikin gamu yafa'da yanamae shigewa motar yafigeta
Tabi motar da kallo Allah yasani bataso tafiyansu Ba.
Gashi taso MARWAN yayi mata magana dan tanajin da'din muryar shi sosae
Sam amota MARWAN bae kula Amar Ba
Todama Amar 'din yasan bazae kulashi Ba amma yana tsoran shurunsa
Sun isa gida lpy lau
Suka samu Momy da dady suna hira afalo zainab na game a laptop
Da gudu tazo tataresu tana cewa oyoyo ya MARWAN oyoyo ya Amar
Cikin fara'a sukace oyoyo my sis
Momy tace sannunku kunsha hanya
Amar yace wlhi
Dady yace to sannun Ku nasan kan kuqara zuwa garin sae kun'dau shekaru
Amar yakalli MARWAN qasa qasa yace
Ai dady zamu koma nanda wata 'daya
Cikin mamaki momy da dady suka kalli Amar dan sunsan koka'dan basasan zuwa qauyan
Momy tace to Allah dae yasa lpy
Yace lpy Momy alkairine
Yayane yayi mata a can
Momy takalli MARWAN tace wae haka
Gamamakin Amar sae yaji yace eh
Daka tsalle zainab tayi tana murya tace
Allah nagodema ma
Kae I luv u ya MARWAN naji 'dadi
Dady yace masha Allah 'yar gidan waye
Amar yace wae 'yar Malam shehu
Dady yace Malam shehu Malam kae ban ganeshi Ba
Yace yanadafa 'ya Nafisa amma mamanta tarasu tun tana qarama
Dogon tunani dady yayi can yagano Malam shehun yace nagane shi
To Allah yasa matar alkairice agaresa Amar yace amin
Momy da tasaki baki tace
Ikwan Allah yanzu MARWAN aure zaka qara ina soyayyar da kakema matarka
Amar yace kae Momy kibarshi man
Dady yace banda abinki ai so tsuntsune
Amar yayi dariya yace hakane dadyna
MARWAN ya'dau keey 'din motarshi yace Nina tafi
Dady yace to yaushe kakesan ayi bikin
Ya kalli Amar
Da sauri Amar yace nanda wata biyu yace
Yanaso ko
MARWAN baiyi magana Ba yafice
Momy tace nisae naga kamar matar bata shigeshi Ba
Dady yace inbata shige shiba yazaiyi yace yana Santa
Kawae halin miskilancin 'dannakine yatashi
Tace ina mamakin halin nan nashi ko nawa yayi oho
Dady yace Allah yakyauta
Amar najinsu yatashi yayi shashinsa yana cewa Momy kayanki namota Wanda Hajiya tabayar abaki
Sis kawomin abinci atare sukace to
to
Zainab na kitchen tana ha'dama Amar abinci
Allah Allah take tagama taje dan gulma nacinta
Ta'ajiye Mae abincin akan table
Yace yauwa sis
Tace ya Amar ya'akayi ya MARWAN yafa'da San wata yace
Duk shirinane
Nan yabata lbr tadinga dariya
MARWAN tuqi kawea yake amma tunanishi yazaiyi da auran Nafisa Allah yasani soyayyar matarsa ne kawae azuciyarsa
Amma tunda Amar ya matsa zai aureta kawae
intagirma tagane bayasanta tarabu dashii
Dan ra'ayin shi nazaman mata 'dayane
Yayi parking motarsa cikin gidansa yafito
Dagudu maryam tazo tarungume shi tana murna shima cikin 'doki yafara kissing dinta
Tajashi falo
Tace yanzu sae kafara wanka kaci abinci sae kaban lbr
Yazareta daga jikinshi yaqare mata kallo
Maryam bawata kyakkyawa bace amma kallo 'daya zaka mata gano Abu biyu atare da'ita
Nafarko tanada wayewa sosae
Nabiyu kallo daya zaka mata katabbatar da bata da kunya
Amma ga MARWAN duk duniya bamekyan marwan dakuma kunya
Bayan MARWAN ya gama kallanta Riga da wando ne tasa tayi kyauta sosae
Yamayar da kallansa kan falan
kaca kaca yake
yace wae my luv yaushe zaki fara tsaftace gidannan tayi shuru yaci gaba
Saiki tsaftace jikinki amma gidanki baxai sami wannan gatan ba πππ
Tace haba hony daga dawowarka zaka faramin fa'da
Yace ok bazanyi miki magana akan gyaraba
Wlhi halin nan naki yana bani haushi
Tayi farii da ido tace yadena baka haushi honey
Su Habiba ne sukazo shiya gidan yayi datti
Kuma wlhi nagyara jiya yace
Tun jiya
Tace eh
Yace banga dalilinki nahanani kawo miki 'yar aikiba
Tace inaaaaaaa
banasan 'yar aiki sobuda 'yar aikin aunty Zakkiya ita ce tazama kishiyarta
Yayi murmushi
yana tuna kishi irin na maryam
Akwaita da kishi
Yace kina tsoran wata takwace miki nine
Tace kwarae
Ai duk macan da tayi gangancin sanka tota yaudari kanta
Ba'dan ka'dan ba
Yace danni nakine
Tace ato
Shiga yayi betroom. Yanda yayi zatan ganinsa hakako yagansa wato aburkice
saikace Ba mace agidan
Girgiza kae kawae yayi yafa'da toilet nanma takaici kamar ya kasheshi. Dakansa ya tsaftace toilet 'din yayi abin da zaeyi
tana kan gado tanajin
Shi
Yafito yace amma toilet 'dinnan yafi 4 days baiga wanki Ba
Tace tunda katafi
Dake ba shigarsa nakeyiba
Amma ai bae kae 4 days ba
Yana zaune a dining takwawo Mae abinci indomie ce da egg
Yana kallanta yakauda kae tace lpy
Yace ita tajawo hakan
Gsky bazanci Ba
A duniya baki da abinci sae indomie
Gashi itamma baki iyaba. Abu duk qarni
Cikin jin haushi tace
Nagajifa
Wae meyasa kowane lukaci kakesan kusheni
Komae nayi ban iyaba
Amma ai kasan bana girki agidanmu bare aiki
Amma kae ina qoqarin yima komae amma baka gani.....
Taja tsaki tabar gun
Tashi yayi ya'dau keey din mota ya fita
Dan yasan yanzu yana zuwa lallashinta sae tasashi yaci indomie shikuma Allah yasani ba zaeciba
Hotel yanufa yaci abincin da yakeso dama yasaba zuwa Dan 'yan hotel 'dinma sunsan shi
Sanda yagama yadawo gidan
Sam yanda yabar komae haka yazo ya ganshi yayi tsaki
Allah yasani MARWAN akwae shi dasan tsafta shiyasa duk ran weknd yake zama yagyara gidan
Har zae shiga 'dakinta saidae yafasa. Yashiga nasa.
Ya gyara kowane saqo da lungu na 'dakinsa
Ya tsaftace yadawo falo ya gyara shi
Tare dasa tuarare
Nan gidan yafito tsaf
Nan gidan ya 'dau kamshi
Kitchen yashiga shima yagyara shi sosae
MARWAN dama yasaba da wanke wanke maryam nan komae yafito tsaf
Ya qara yin wanka
Sannan yanufi 'dakin ginbiyar tasa
Tana zaune kan gado tana catin rannan 6ace
Kallo daya yayi mata
Yaga bazae iya jure fushinta ba
Nan yajawota jikinsa yana lallashinta
Dake itama ahannu take nan warware
Maryam tana harkar maganin mata sosae
Tabbas dashine takejan hankalin MARWAN yana jin da'dinta sosae amma baya gamsuwa da'ita
πππ
'YAR QAUYE KO 'YAR BIRNIπππ
Sam MARWAN ya manta da zancan wata Nafisa
Yana falan Momy sana hira tsakalin 'da da Uwa
Sae ga dady yafito