Showing 12001 words to 15000 words out of 20825 words
Yajah tsaki duk agajiye yake bayajin zae iya wani gyara yanzu
Shiyasa yafito daniyar zuwa gidan Momy
Karab idanshi yakai kan part 'din Nafisa
Nan zuciyarshi tabashi yashiga.
Yako shiga.....
Wani kamshi yaduki hancinsa yaqarema 'dakin kallo ko'ina tsaf tas
Yaduba toilet
Nanma tsaf yaganshi
Nanko yatu6e yashiga wanka
Tofah tundaga ranar yamayar 'dakin Nafisa 'dakin harkarshi idan yagama abinda zaeyi sae ya gyara
Sam maryam bata damuba. tunaninta ai Nafisa batanan
To yauma dan yana saurine shiyasa bae tsaya gyara waba
Da Nafisa taga haka
Nan tahau gyara tana tunanin ko maryamce takawo bakinta falan
Sanda tatabbar tagama tsaftace ko ina sannan tanufi kitchen tadafah jalof tazauna taci taqoshi
Sannan tayi wanka
Tasa qananan kaya Threequarter ne ajikinta sae qaramar rigarta mae hannun bureziya ko cibiya bata rufe mataba tafeshe jikinta da turare
Tanufi part 'din maryam
Sallamah tayi akofar amma taji shuru
Dake takudirce aranta sae MARWAN yaga kwaliyarta
Nan tatura kofar MARWAN ne zaune kan kujera ranshi a6ace. Ga falan kaca kaca duk kwalayan datti
Gabanta yafa'di. da sauri tajuya dan fita
Yace Mae ya kawoki
Cikin in ina tajuyo tace am um dama nazo gun Aunty maryam ne dan in gae sheta
Shuru yayi kawae yana kallanta tunda daga sama har qasa
Yace batanan
To tace
Har takae kofah yace
Kinyi kyau FEENAH
Sauke ajiyar zuciya tayi tace nagode. Tafita
Tana mae godiya ga Allah tare da'da samun qarfin gwiwa
Bayan fitar Nafisa da minti 3 MARWAN yaja tsaki kallo 'daya zakamae
Katabbatar dacewa qiris yake jira yafashe
Dan yau yanaso yayi maganin maryam akan fitar da takeyi batare da saninsaba kuma tabar mae gida da datti
Canko sae gata
'Kamshin turaran 'dakin Nafisa ne yasata ganewa tadawo taja tsaki
Amma maeeee
gabantane yafa'di da taga motar MARWAN
Cikin sanyin jiki tashiga falan bako sallamah
Tace my honey yaushe kadawo
Yaqare mata kallo tas riga da wandone ajikinta kayandae datafi sawa yace
Daga gidan uban'wa kike tace
Gun Habiba fah naje
Cikin fusata yace
Allah yasa gidanku kikaje tace
Haba MARWAN yakake San zagina yace
Ai zagin kikeso
Sanin halinshi yasata cewa
Nidae bawan nanba kayi hakuri nayi lefi
Bazan qaraba yace
Wlhi kika qara fita batare da saninaba sae namiki abinda harki mutu baza kimantaba.
Tace afuwa wlhi bazan qaraba
Bae kulaba natsawan minti biyar
Can yace banasan ganin dattinnan
Tamarairaice tace yanzufah nadawo honey ya kamata kabarni inhuta yace ko tace kwarai yace
To bara inje 'dakin FEENAH idan kingyara kyakirani
Cikin tashin hankali taje tarungume shi tace aa wlhi zauna yanzu zangyara
Yace wlhi maryam daga yau kika qara barin 'dakinki da datti wlhi fita zanyi inje 'dakin FEENAH dan tafiki tsafta nesa ba kusaba
Cikin fargaba tace Allah bazan qara ba my honey yace to sakeni
Nan tasakeshi yakoma kan kujera yana kallanta tana gyaran
Sanda tagama tsaf
Tazo tazauna gefanshi ya'dan rungumeta tafara kissing 'dinshi nan al'amura suka canja maryam tasan kan MARWAN shiyasa yakejin da'dinta sosae amma kash baya gamsuwa da ita
Bayan Nafisa tadawo 'dakinta tayi alwala tare dayin sallah tabi lafiyar gado
Nanko bacci ya'dauketa
Washe gari da misalin qarfe 8am
Tashe wankanta rigace dae da siket amma yayimata kyau dan siket sisfieces yazauna ajikinta sosae
Ga kalar atanfar mekyau
Breakfast ne agabanta sauri sauri takecin shi.
Dan tanasan zuwa gun MARWAN tatam bayeshi tanasan zuwa gun Momy
Data gama sae ta'dauki turare tafeshe jikinta dashi
Abin mamaki tana niyar fita sae gashi yashigo
Da sauri tadurkusa har qara tace gudMrning yayah
Yanda tafa'da ya'dau hankalinshi yace Mrning how was ur 9nt tace pyn
Yace gud
Tace I wanna go nd bisit Momy
Shuru yamata yanufi TV stand wani agogon shi ya'dauka yace
Go nd pic up ur veil lets go
Da sauri tatashi ta'dauko gyalan nata tafita
Acikin mota tasamae shi yace
Bakije kin gaida Auntynki Ba.
Tajuya tanufi part 'din maryam
Afalo tasameta
Kallo 'daya zaka mata katabbatar da bayi wankaba
Cikin girmamawa Nafisa tace ina kwana
Zuba mata ido kawae maryam tayi dan tuni tunaninta yatafi dan ganin yanda Nafisa taha'du
Cikin wata munafukar murya tace lpy
Nafisa tajuya har takae kofa tajuyo tace aunty zanje gun Momy ne yanzu sae nadawo
Tace badae MARWAN ne zae kaikiba
Tace shine yanama mota
Tashin hankali afurgice tata itako Nafisa tafita
Ashe biyota tayi
Tasa hannu kenan zata bude kofar maryam tamake hannun tare da bangajeta tana cewa
Wlhi bazaki shiga motarnan Ba
MARWAN Wanda yake danna waya ya'dago da kansa ya gansu akansa
Da sauri yafito yace lpy
Tace gallamae harara tace bansaniba. Saboda tsabar munafunci irin naku namaza shine kakesan fita da ita wlhi baka isa'ba yace meyasa kikesan yin abu kamar yarinya gun Momy fah zata lefine dan nakaeta
Tace babbama kowa Dan wlhi inaji ina gani bazaku fita tare Ba
Ranshifah yafara 6aci
Yace to wlhi tare zamu fita
Tace ko
Yamae da kallanshi kan Nafisa yace shiga mota mutafi
Takai hannu zata bu'de murfin kofar........
Ga mamakin Nafisa sae taga har tashiga mortar maryam batayi yinqurin hanataba kuma bata tankaba
Shima yashiga motar yana niyar tayar da'ita sae kawae tasa kuka tare da tafiya falanta da gudu
Cak MARWAN yatsaya yajah tsaki abae yane yace mata matsalane.
Topah 😳
Nan yafita yabita
Ranko Nafisa ya6aci Danji tayi kamar tatashi takomah 'dakinta tafasa tafiyan
Sae dae ta danne.
Shiko yana shiga falan yaganta kan kujera tana kuka
Ya rungumeta yace.
Haba my luv plx kidinga kama girmanki wlhi inkina haka yarinyarnan Zara rainaki.
Tace nifa banasan galinka da ita yace
Yace mekike tsoro tace randa zaka fara Santa kuma kafara kusantarta yace.
Kae habah wannan aisae ke ka'dai
Tace amin alqawari yace nayi.
Tace yauwa
Yace plx kidena damuwa komar zae tafi yanda kikeso tunda zuciyata takice.
Nan yalalla6eta
Sannan yakoma mota.
Kallo 'daya yayima Nafisa ya tabbatar itama tashaqa kuma take jira itama.
Sam sae yaji zuciyarshi. Namishi zafi inhar bae lallashi Ba itama.
Haka suketa tafiya yana satar kallanta
Amma ita kokusa bata kalleshiba
Sam tashare shi
Ga mamakinsa sae yaji yadamu da yanda Nafisa tanuna 6acin ranta
Ahaka suka'isa gidan
Yanako yin faking tafita.
Yabita da kallo
Da sallamah tashiga falan
Zainab najin muryarta tafito da gudu tarungumeta tana cewa sannu da zuwa dama nayi tunanin ganinki yanzu
Nafisa tayi dariya tace Allah sarki nayi kewarki 'yar Uwa
Tace nima haka wlhi
Tace ina Momy tace
Tana ciki gun dady
Tace to muje 'dakinki kafin tafito tace muje
MARWAN nakallansu sae suka bashi sha'awa
Amma yayi mamakin yanda sukesan Nafisa amma suke qin maryam
Nan yashiga gunsu Momy ya gaidasu suka amsa Cikin kulawa
Momy tace dafatan kazomin da Nafisa
Yace wae mae yasa Momy kukafisan FEENAH akan maryam
Tace dukkansu muna sansu
Yace no Momy soyayyar da kuke nunawa FEENAH tafi ta maryam
Tace karka dameni dan Allah
Yace Allah yahuci zuciyarki tare da ita mukazo
Dady baiyi magana Ba
MARWAN yatashi yace ni natafi
Tace zaka biyo tananne ka'dauketa ko direba yakaita
Yace no zan biyo
Suka bishi da addu'a yafita
Nafisa da zainab ne kan gado sunata hira Cikin nisha'di Zainab tace
Kinga yanda kike kyau kuwa kamar ba 'yar qauyan nan mae tallan goroba
Nafisa ta'daka mata duka tace
Nidae matar yayankice yanzu komae zakice kice
Ta kwashe da dariya tace wlhi har maganarki da yanayinki ma yacanja
Cikin shagwa6a tace
ya isheki fah wlhi zan gayaki da Momy
Tace bafah da ya MARWAN kikeba da zakimin shagwa6a
Zatayi magana
Momy tashigo
Dasauri tasauka tadurkusa tace.
Sannu Momy ina kwana tace lpy Nafisa kindawo lpy
Tace lpy lau Momy
Tace gud haka akeso dafatan kina qoqari
Tace inayi
Zainab tace kobatayi zatace tanayi Momy
Nafisa ta harareta tace Allah Momy inayi tace
Barta nasan kinayi
Tace yau momy nizanyi girkin gidannan
Momy tace to ba damuwa Nafisa indae girkine gashinan yana jiranki amma nadare tace to
Momy tafita
Zainab tace kice yau zanci girkin amaryar matar babban yayah
Tace aikonayi bazan baki Ba
Tace kin'isa
Tace zakigani
Tace idan har banciba to sae nasan yanda nayi ya MARWAN ma baiciba
Tace tab mijin nawa zaki hana abincina wlhi baki isaba
Zainab tace Hakka kike dama dazakice mijinki bako kunyata
Tace akan mijina nafi haka
Zainab takama baki.
Tace aranta Allah nagode ma da yarinyarnan take kilewa dan da dukkan alamu zataba maryam wahala
Nafisa tace kinyi shuru tace no mamakinkine ya kamani
Dariya kawae tayi
Girki sosae Nafisa tayi dan towan shinkafa tayi miyan ogun taji bushash shan kifi da naman kaza ga man shanu
Tayi kunun aya
Sannan tadafa kuskus da miyar kwae
Tajera kumae akan dannin
Zainab tace gsky matar babban yayah 'kamshi ya dameni asanmin
Tace to za'a sanmiki amma saikinje kinyimin wanke wanke
Tawaro ido tace tab lallema kin rainani ga Jamila
Tace aiyau nahani Jamila aiki
Tace plx Auntyna temakeni wlhi zan iya miki kuka
Tayi dariya tace to kiyimana
Momy dake jinzu tana karanta jarida tayi murmushi tace
Nafisa karkibata saitayi wanke wanken dama takwana biyu batayiba
Tace yauwa Momy
Zainab batace komae Ba tanufi kitchen 'din danyi
Amma tana zuwa tatarar Ba wanke wanke Ashe tayi da murmushi tafito tanacewa.
To nagama
Nafisa tace to angae sheki zokici
Nan taci tana santi
Momy da dady ma sunyi santi dan dady sae samata albarka yakeyi
Takoji da'di sosae
Nan tada'da godema Jamila aranta dan itace jagaban koya mata komae
Sae gab magriba Amar yashigo
Aiko yacika da murnar ganin Nafisat yace kaga Auntynmu
Tace kaiko
Yace menayi
Tace Allah Amar kadena kirana da Auntynmu
Yayi dariya yace wannan kuma saidae kiyi hakuri dan bazan denaba
Amma yaushe kika iya sunana tace
Dama nacema sae nazama 'yar birni
Yace hakanefah
Amar yayi mamakin yanda akace Nafisa CE tayi girkin gidan
Dan gsky yaci abinci Mae da'di yace kae Auntynmu kodae gidanku kwanona zae dawo
Dariya tayi kawae
Momy takira Nafisa taha'da mata magungunan mata Masu kyau
Dana Sha da madara da na tsarki dana dafawa duk
Tace kitabbatar kuna komawa gida kifara Sha zasu qara miki lpy da 'yanci agun mijinki
Kunya takama Nafisa
Tace kidena jin kunyata ni mahaifiyace agareki
Sae bayan isha'i MARWAN yashigo gidan
Kallo 'daya Nafisa tamae tagane yana tare da gajiya Allah yasa da kwalliyarta
Yace tatashi sutafi
Momy tace da dae kaci abinci zaifiko Dan naga kamae da yunwa atare dakae
Baiyi musu ba zainab tasamae tuwo
Yafaraci idan Nafiisa akanshi tana Addu'ar Allah yasa yayaba
Yakoci sosae yakora da kunun Aya
Yace Momy wayayi tuwannan
tace yaci ace kagane girkin matarka
Yace FEENAH tace ita mana
ya maeda kallanshi kanta da mamakin dama ta'iya girki haka
Da sauri Nafisa ta sunkuyar da kanta
Baice komae ba yatashi yace to zamu tafi
Momy tace Allah ya kaiku lpy suka amsa da Ameen sukafi
Haqiqa sunba kowa sha'awa
Suna Cikin tafiya MARWAN yace kinyi kyau FEENAH
Cikin sanyin murya tace kafiniyin kyau yayah
Wani zirrr yaji tundaga kansa har babban yatsansa na qafah
Yarinyarnan fah tana hargitsashi da muryarta yace aransa
Yadaure yace ko
Tace Allah da gaske naso nafara yabaka amma karigani
Shuru yayi
Can wayarshi tayi qara ya'dauka
Aminu yagani abokinsa
Yace ina hanyar zuwa gida ne
Aminu Yace no bawani abu bane dama inasan intunatar dakaine dan Allah kazo da maryam gobe wajan reception wlhi Zakkiya tanasan taje
MARWAN yace to zatazo Ango kanata wani zumu'din aurannan
yace kae anaku ai abinda kayi yafi haka yakashe
Ya'dan kalli Nafisa
Yace mekikeso nasiya miki tace Ba komae
Yayi faking dae dae inda wajan kayan fruit yasiya yaja motar
Koda MARWAN yayi faking Nafisa tafito
Maryam tagani afarfajiyar gun
Rantako a6ace tawatsa mata harara
Nafisa da tsoro
Tuni tsoro yashigeta tayi saurin cewa sannu da gida aunty maryam
Tace sannu da gidan uwarki
MARWAN yafito yace wae mae yake damunkine
Tawatsa Mae harara
Tace ban saniba
Yace OK yarufe motar yayi part 'dinta
Dama tuni Nafisa tayi shashinta da gudu
Suka barta ita 'daya
Cikin takaici tabi bayan MARWAN
Koda tashiga yana toilet tazauna gefan gado
Bayan ya fito tace
Ai wannan wulaqancine kufita tunsafe sae yanzu zakudawo kuma aikae 5 kake dawowa
Yace am sorry aikine yamin yawa sae bayan isha'i naje gidan
Bu'dar bakinta sae cewa tayi qarya kakeyi
Cikin mamaki yace ninake miki qarya
Tamurgu'da mae baki tace eh
Sae jin saukar mari tayi
Marinko yashigeta
Yace fitar min anan
Tasan halinsa sarae ka'dan da aikinsa ya dakata tuni tafice
Nafisa ko bayanta qara mae
wanka tayi tabi lpyar gado tare da addu'a
Washe gari
Tatashi tashare lungu da sa'ko
Tafeshe da turare
Sannan tayi kitchen
Doya da kwae tayi tare da saidin
Gefe guda kuma tayi Lipton wanda yaji kaninfari da citta
Sannan tajera kan dannin tashiga wanka
Su maryam ma suntashi.
Amma sam taqi kula MARWAN
Shima dake miskilancin nasa yamotsa ko kulata baiyi Ba
Sanda yaga shirinsa tsaf yanufi dannig bakomae yaja tsaki Sam MARWAN baya wasa da cikinsa gashi yanajin yunwa
Yamae da kallansa kanta yace ina breakfast 'dina
Tace banyi ba
Yace dalili
Tace kajegun Nafisa tabaka
Yace OK dama ai tafiki iyawa yafita
Sae kuma yadawo
Yace wlhi kika kuskura kika biyoni gunta ranki idan yayi dubu saiya 6aci yafice
Tabishi da kallan mamaki. Dan ita tace yaje gun Nafisat ne dan tana tunanin bazae iya cin abincinta ba batasan aikin gama yagama Ba
Ahankali yashiga falan idanshi yasauka kan danning
Yazauna yana bu'de doyan
Mae makwan yaji qarni kamar yanda yasaba jin na maryam
Sae yaji qamshi
Nan yafara ci yana mamakin yanda Nafisa ta'iya sarrafa komai
Nafisa ko tana gaban miro tana kwalliya
Faudace dae da'dan man baki sae tafeshe jikinta da turare tafito
Karab suka ha'da ido
Ta durkusa tace
Ina kwana yayah yace lpy lau FEENAH kintashi lpy tace eh yace gud zonan
Taje kujerar kusa dashi tazauna
Yace nacinye miki breakfast ko
Tace aa damafah kainayi ma
Yawatsa mata wani kallo tuni jikinta yamutu yace
Aiko nagade dafatan za'adinga min kullun tace insha Allah
Sanda ya tabbatar yacika tunbinsa sannan yace to FEENAH cikina zae fashe tace yayi hakuri dan Allah karya fashe
Yatashi yana cewa ni natafi
Tace Allah ya kareka yayah yabaka abinda kakeso ya kareka daga sharrin maqiya
Cak yatsaya Dan yaji da'din addu'ar sosae
Yace tnx my luvly FEENAH yafice
Harya shiga motarsa yatuna zae gayama maryam tashirya zuwa reception 'din Aminu anjima yafito
Kuka sosae yasameta tanayi
Nan tausayinta Yakama shi yace
Menene koma tace
Wato MARWAN yanzu har lukaci yazo da zaka fara wolaqantani akan wannan yarinyar
Yace cigaba inajinki
Tace kucaka qazama da ita har ka'iya zuwa kaci abincinta
Yaja tsaki yace banji
Me kikesan fa'daba
Tace sonake kadena shiga sharinta bare har kaci abincinta hira taha'da Ku
Yace tab
Tace miye
Yace kin ibo da zafi
Wlhi bazan iya dena cin abincin FEENAH Sam
Kibarma maganar indena shiga shashinta dan abune wanda bazae yuhuba
Amma namiki alqawarin bazan ta6a yarda santa yashiga zuciyataba bare har in kusan ceta
Tace nashiga uku yanzu bazaka iya dena kukataba
Yace kwarae inadae damuwarki karna sota kuma karna kusan ceta indae wannan ne anhucce shafin
Tace MARWAN
Yace Dan Allah kikwantar da hankalinki bana san yarinyar nan kwata kwata to akan Mae zaki dami kanki plx anjima kishiya muje reception din Aminu
Cikin kuka tace ba'inda zatani
Ok yafice
Nan yaci karo da Nafisa ya hucceta
Tashiga falan da sallama tare da cewa Aunty maryam ina kwana
Cikin fusata tace fitarmin afalo dan ubanki
Ba musu tafice
Tsaf Nafisa taji abinda MARWAN yace
Amma ranta ya6aci da yace baya Santa kwata kwata
Nan tasa aranta sae yasota indae kirsa na aiki
Tana mamakin yanda maryam take nuna kishinta afili
Dan wlhi zata iya rantsewa tafita kishi nesa bakusa Ba
Dan tatsani maryam ba'dan ka'danba
Batasan tararyar MARWAN dakowace mace inhar aure ya halarta garesu
Misalin qarfe 4 MARWAN yanufu gida dan shiryawa reception din Aminu
Koda yazo gidan yatarar maryam batanan ranshi ya6aci amma yasa aransa zai koya mata hankali
Nan yayi wanka yashirya yanufi falan Nafisat
Nan yaganta tana bitar karatu
Yace FEENAH
Tace na'am
Yace tashi kishirya kirakani wanigu
Tace toh
Rasa kayan dazata tayi shiya tazauna gefan gado kawae tana kallan kayan canda yaji shiru yashigo yace yadae tace wanne zansa
Wata atanfa yaza6a mata 'dinkin riga da siket yayi kyau
Tatsaya mutsul mutsul yace kisaman tace to kafita
Yayi murmushinsa
Yafita
nantasa tafeshe jikinta da turare
Koda tafito qura mata ido yayi dan tayi kyau komae najiinta yana baiyana yanda yakeso
Yacije baki
Yace yace muje ko
Nan suka kama hanya
Wajene wanda yatara wayayyun mutane kallo 'daya zaka musu katabbatar sun jiqu da ilimi musamman boko
Aminu yayi mamakin ganin MARWAN da Nafisa yace wannance amaryarmu ko
MARWAN Yace yah
Yace tayi to ina ganinka