Showing 27001 words to 30000 words out of 122467 words

Chapter 10 - Buzu Book 2 Complete

Unknown   

26 Aug 2026

43

shi, ya yi nisa da nawa zamanin? Me ya sa kakannina suka zaSi zama 'yan bori? Suka gada mini wahala da masifa take ta bibiyar rayuwata. Na zama mujiya a cikin mutane, duk inda na tsuguna sai wata masifa ta afku, da za a jefa mini zargi, kasantuwata ni ba mutum ba ni ba wani jinsi daban ba? Me yasa zan girbe ba?ar shukar da ban san a lokacin da aka dasa ta ba? Ina son mijina duk da daga ni har shi, ba mu san waye shi ba.
Duk da Nijar ba Waki Waya bane ba, ba kuma ?aramar al?arya ba ce ba, ?asa guda ce, na gwammace zagaye ta neman ahalinsa na dam?a shi a gare su, da na ci gaba da zama da shi, mummunar ?addarata tana shafarsa, ko kuma na zama 'yar bori na ci gaba da gadar da wahala da masifa ga zuriyarmu, gara ko ma mene ne ya ?are a kaina." Ta ?arasa maganar cikin ?araji, tana kuka mai bayyanar da tsantsar ba?in cikin da yake binne a cikin zuciyarta.

*****

A hankali yake driving cikin nutsuwa, yana sauraren Jamila, da ke bin wa?ar da ke tashi a cikin motar ?asa-?asa, sai kuma ta yi shiru.

"Ya ki ka yi shiru kuma?" Ta ce "Au wai ka na ji na?"
Abba ya ce "Eh mana, har kin fi masu wa?ar ma iyawa" Dariya ta yi ta ce "Ka ji ziga, muryar ta su da aka tace, aka goge tawa kuma a haka, ka ke cewa na fi su iyawa"

"Au ba ki yarda ba? To shikenan ni dai na san kin fi iyawa" ya yi maganar yana parking Win motar a harabar gurin shan ice-cream Win. Abba bai taSa soyayya ba, duk wannan abubuwan da yake yi wa Jamila, bai taSa furta mata cewar yana sonta ba. Sai dai ita sarai ta gane sonta yake yi, so kuma ba na wasa ba. Sai dai tana mamakin yadda duk wannan abin da yake yi mata, ba ya iya nuna wa a gaban Hajiya Sa'a, hakan ya sanya ta fara tunanin ko dai yana da wata manufa a kanta ne.
Sai dai ta lura halaye da Wabi'unsa, sun sha banban da na Hajiya Sa'a, shi Abba akwai tsantseni, da gudun saSa wa Allah. Dan duk da son da yake yi mata, sai da ya yi mata faWa a kan shigar banza da ta kan yi wasu lokutan.

Ice cream su ka sha, yana ba ta labarin yadda ya yi karatu, da irin ?alubalen da ya fuskanta na rayuwa. Su ka gama ya Wauke ta ya mayar da ita gida.

Bayan ta shiga gida, Mama ta ce "Yauwwa ke nake jira dama, gas ya ?are na kira wayar ki kuma ba ki Waga ba"

"Ina hanya ne, ga ATM Wina, a bawa Nasiru ya je ya Wuro. Har za ta shiga Waki sai ta fasa ta ce "Ni kuwa jama'a ina Nana ne? Wayarta ba ta shiga, shekaranjiya waccan ma na biya gidan da mijinta yake gadi, na ga kamar babu kowa a gidan"

Mama ta taSe baki ta ce "Au ke ba ki san abin da yake faruwa ba dama?"

Ta tsaya tana kallon Mama ta ce "Mene ne yake faruwar?"

"Ai tuni aka kore su daga wannan gida. Ke ba zama ki ke yi ba ne shi yasa, suka koma unguwar su Ummi, to kin santa duk inda ta zauna bala'i ne yake bibiyar gurin, hatsaniya ta haWa ta da matan gidan da suke, suka ce mayya ce aka tashe su. Ai nan Babanku ya je aka yi ta fafatawa, da ta kwaso jiki ta taho nan, wai za ta dawo mijinta babu lafiya, na ce bani da gurin jinya a gidan nan. Allah ya raba ni da masifa, ba za ta dawo mini ba, to ?arshe dai wai yanzu tana ?auye, can gurin Uwani a can take jinyar mijin nata"

Jamila ta yi sak, ta ce "Mama Nana tana ?auye fa ki ka ce?"

"Eh mana, to idan ba ?auyen ba ina za ta je? Tana can"

"To waye yake ba ta Abinci?"

Mama ta ce "Oho ina na sani?"

"Amma ya aka yi tsawon wannan lokacin ban sani ba? Yanzu ba kamar da ba ne, ban ji daWin abin da ki ka yi ba Mama, bai kamata a kore ta ba a ce ta koma ?auye da zama ba. Da ina nan ko na sani, da na kama musu wani gidan, gaskiya sai ta baro ?auye"

"To ke ina ruwanki? Mene ne naki a ciki uwar Iya? Kina kallon irin ba?ar azabar da na sha, a kan zamana da ita a gidan nan. Na meye za ki kuma jajubo mana ita. Gara ki bani kuWin da za ki kama mata hayar na bawa WanLadi, Wan autanmu ya tafi kasuwa da zaman banzae da yake yi, na yi masa aure tun da Allah ya sanya kuttun arziki ya fashe mana, ba ki kai kuWi inda babu amfani ba"

Jamila ta dubi Mama ta ce "Wannan Wan uwanki ne, sai ki nemi kuWinki ki yi masa, nima 'yar uwata nake tunani. Haba Mama, ko wani Nana ta kashe miki ?iyayyar ta isa haka ai. Ai yakamata a tausaya mata, miji babu lafiya ga zaman ?auye, ita Uwanin za ta Wauki nauyin Abincinsu ne? Tun da muka tashi a wahala muke a gidan nan, amma ita nata ya fi na kowa ma" Jamila ta ?arasa maganar cikin damuwa, ta shige Waki, ta bar Mama da buWaWWen baki.

*****
Kallonsa Nana take yi, suna zaune sun yi juguum daga ita har shi. Bayan ta gama yi masa kitson zanen hannu guda takwas, ta yanke masa faratansa na hannu da na ?afa.
Kamar wadda aka mintsina ta tashi tsaye, ta kalle shi ta ce "Sayyid, bari na je na dawo" ya bi bayanta da kallo har ta fice.

Sai dai a ?alla ta kai awanni biyu kafin ta dawo, ko da ta dawo ta tarar da shi ya haWe fuska, ta yi shiru ba ta kula shi ba, ta koma tsakar gida.
Ta laluba kayanta, ta Waukko wata takarda mai Wauke da ayoyin ru?iyya da na karya sihiri, sannan ta hura wuta a cikin murhu.
Ta dawo tsakar gida ta zauna, ta fara da Bismillah da karanta Suratul fatiha, sai Suratul fala?i da nasi. Ta karanta ayoyi biyar Win farko na Suratul Ba?ara, ta fara karanta Suratul mulk, a hankali sai ta fara gani dishi-dishi, ta fara daina ganewa. Ta busa ayoyin a cikin ruwan, Sai ta ajiye takardar. Ta Wauki wata leda da ta zo da ita, ta fito da man habbatussauda da jan Almiski.
Saboda wauta sai ta buWe miskin, ta kai hancinta, da sauri ta dungurar da shi a gurin, ta ja da baya, dan tuni ta ji jikinta ya fara tsuma.
Sai da ta Wan samu nutsuwa, sannan ta zazzaga tazargaWe a cikin bokitin, ta kawo ganyen magarya guda bakwai, ta saka a leda ta Wan bubbuga musu muciya, ta haWa a cikin ruwan. Ta yi shiru tana tunani a ranta ta ce "Allah ya sa ba mai magani na zama ba, ?aisar bai mayar da ni 'yar bori mai bayar da magani ba, larurar Sayyid ta saka na fara koyi da magungunan sarkin baka."
"Amma ai ayoyin Alkur'ani ki ka karanta, shi ma kuma Sarkin Bakar yana amfani da Alkur'ani" wata zuciyar ta tunatar da ita. Haka dai ta ci gaba da wasi-wasi.
Can yamma, bayan ta tabbatar da ganyen magarya da tazargaden sun tsumu, ta Wumama ruwa ta tsiyayi ruwan tofin ta tace ta haWa da ruwan Wumin, ta kawo man habbatussauda ta tsiyaya a ciki, ta kawo jan miskin nan da ta saka kwalbar a ruwan Wumi, ya narke ta tsiyaya a ciki, ta Webo garwashi a kasko ta shiga Wakin. Yana ganin Nana ya tashi zaune yana kallon ta, ya ga ta samu ?yalle ta Waure hancinta da bakinta.
Ta nufo shi ya ga ta hau tuSe masa kaya, ya din ga bin ta da ido, ta bar shi daga shi sai gajeren wando. Hannunsa da yake ma?ale take kallo cikin damuwa, ta shafa hannun.
Sai kuma ta yi Bismillah ta fara shafa masa wannan ruwan. Tun daga cikin kansa.
Girgiza kai ya fara yi, yana ture ta da lafiyayyen hannunsa, yana toshe hancinsa. Ya din ga girgiza kai jikinsa yana karkarwa bakinsa yana rawa, ya din ga wani irin gunji yana mi?a. Amma sai da Nana ta ji?e shi da ruwan nan tsaf.
Ta kunna kiran salla a wayarta. Ta kawo tazargade, da habbatussauda da ganyen magarya ta zuba su a kan garwashin nan, haya?in ya turnu?e Wakin, ta ajiye shi a nesa da shi kaWan. Ta fice daga Wakin ta kulle shi a ciki. Ta tafi ta din ga wanke hannunta. Wani irin jiri ya din ga Waukar ta, ga matsanancin ciwon kai, Sari Waya da ya sanya take jin, tamkar kan zai yi bindiga ya rabe.
Ta samu guri ta zauna a tsakar gida, ta dafe saitin zuciyarta da yake ta bugawa da sauri.

Bayan wasu mintuna, ta tashi ta je ta le?a ta window, ta hango shi a kwance a ?asa. A tsorace ta buWe shi, ta nufe shi da sauri tana kiran sunansa.
Gaba Waya ?wayar idonsa ba?ar ta Wauke sai farar, ta dur?usa a kansa kawai ya mi?o hannu zai sha?e ta, amma ta ri?e hannunsa. Hannun ya din ga rawa, ya sauke shi a hankali.

"Sayyid" tana ambatar sunansa, ?wayar idonsa ta dawo ya kalle ta.

"Sannu Shugaba" hararta ya yi ya juya mata baya. Dariya ta fara yi ?asa-?asa.

Ta ce "Haba Shugaba, ya ka juya mini baya, juyo ka kalle ni" ya ?i juyowa. Ta tashi ta buWe labule saboda yadda warin ita ma ya fara damunta.
Ta Waukko tsumma, ta hau goge masa jikinsa, saboda ya daina warin miskin nan ita ma ba ta so.
Ya tashi zaune, tana goge masa. Ta ce "Ko a yi wanka?" Ya Waga idonsa yana hararta, jikinsa ya koma jawur kamar wanda ya ?one.
Ta din ga Soye dariyarta, ta yi masa wanka, ya din ga sinsuna jikinsa yana yamutsa fuska.
Ya shafa fuskarsa ta ce "Ka yi ha?uri, magani ne, ina son ran Ubangiji Allah ya kawo mana afuwa" Ya ture ta daga jikinsa. Amma ta manne masa ta hau cinyarsa ta zauna tana dariya.

Ta juyo da fuskarsa suna kallon juna, ta lumshe ido ta buWe ta ce "Sannu shugaba" Ya jinjina mata kai. "In zubo Abinci ne?" Ya girgiza kai.

"Sai an yi salla?" Ya gyaWa mata kai.

Ya yi sallar magariba da isha'i, ta zubo masa Abinci.

Washegari ma da sassafe, ta kuma rutsa shi tana shafa masa ruwan nan. Yau ma ture ta ya din ga yi yana girgiza mata kai. Ta kunna masa haya?i, ta gudu ta rufe shi a Wakin. Haka ta sake tarar da shi, ya koma ja ya haWa uban gumi. Ta yi masa wanka. Ta ba shi Abinci ya karya.
Allah ya dafa wa Nana, ba su taSa rasa abin da za su ci ba. Kuma haka take ta jujjuya kuWin.

Sai da ta gama yi masa duk abin da zai bu?ata, sannan ta tashi za ta yi wanka, tana tsaye daga ita sai bra da zani a ?ugunta, sai cika bakinta take da aya mai gishiri, ga cikinta ya Waga sosai.
Ta waiwayo suka haWa ido. "Ya ake kallona haka?"

Ya yi mata alama da hannunsa mai lafiya ta zo.
Ta ?araso gabansa ta dur?usa ta ce "Gani" ya nuna mata cinyarsa.
Ta ce "Ina da nauyi fa, jiya ma dan na tsokane ka na zauna, ka ga baka da lafiya" ya saka hannu ya janyo ta, ta hau cinyar tasa tana dariya.
Yatsansa ya saka ya Wan latsa cikinta, ya kalle ta yana murmushi. Ita ma murmushin ta yi ta ce "Kullum sai ya ce ko ta ce tana gaishe ka" Da hannunsa yake tambayarta yaushe za ta haihu?

"Nima ban sani ba, amma dai bai fi wata? huWu ba, saura wata biyar in Allah ya sa mu na raye. Idan ka samu lafiya sosai, za mu je mu ?ara dubawa idan su Habu sun dawo, idan ba su dawo ba sai mu tafi Nijar. Duk da na san da sun dawo zuwa yanzu za su neme mu" Ya yi shiru yana ci gaba da kallon cikinta, da lokaci lokaci yake dan harbawa.
"Zan je na yi wanka"

Da hannunsa ya yi mata alamar, su je ya yi mata.

"Kana fama da kanka za ka yi mini wankan? Wato a ramawa kura aniyarta ko? To na yafe idan Allah ya baka lafiya sai ka yi mini Rayuwata" Cikin murmushi ya sunkuyo da kanta ya sumbaci goshinta ta da laSSanta. Hira yake so ya yi da ita, amma ya kasa sai dai ya kalle ta yana murmushi ko kuma ya din ga yi mata nuni da hannunsa.

Ya Wauki wayarta, ya kunna wa?ar da take yi masa, yana yi mata nuni da ta yi masa. Ta ce "A'a karatu za mu ji ba wa?a ba, a wannan yanayin da muke ciki, ai ba mu ga ta wa?a ba Sayyid" Ya tsuke fuska yana hararta. Ta ce "To shikenan, bari a kashe wa?ar, sai na raira maka da bakina ko?" Kawai ya tsare ta da ido yana wani lumshe ido.

Tana dariya ta ce "Wai Sayyid ni fa ban gane maka ba kwana biyun nan, rigima ka ke ji, amma Alhamdillah alamun sau?i ne da nasara.

Aka shiga kwana na huWu, tana shafa masa tofi tana kunna masa haya?i ta gudu ta bar shi a Waki. Yau sai dai ta gama shafa masa, za ta gudu ya ri?e ta gam. Duk yadda ta so guduwa ta kasa. Ya kalle ta yana murmushin mugunta. Aikuwa jikinta ya fara tsuma ta saka masa kuka, jin yadda gaba Waya duniyar take juya mata, tana shirin fita hayyacinta.
Har dare ya yi suka kwanta, ba ta kula shi ba, dan gaba Waya jikinta ya mutu murus, babu abin da yake yi mata daWi.
Can cikin bacci ta ji ya yi magana"Ma viee"

"Sayyid"

"Na'am"

"Magana ka yi?"

"Eh, yanzu na ji ta zo"

Ta tashi zaune cikin murna tana taSa shi ta ce "Alhamdillah Sayyid, Allah ya ?ara lafiya"

"TaSa ni na ji, ko zan ji wani abu"

Ta ce "Ga shi ina taSa ka"

Ya ce "Ba wannan ba" ya yi maganar yana rungumota da duk hannayen sa biyu.

"Sayyid hannunka ya warke?" Ta tambaye shi a kiWime cikin farin ciki.

"Eh" ya amsa a ta?aice yana ?o?arin yin wani abin daban.

"Bari na lalubo waya na haska ka na gani"

"Kar ki haska ni"

"Me yasa ganinka fa zan yi, hannun zan gani"

"Kar ki haska ni" ya sake maimaitawa.

A Wan tsorace ta ce "Anya kai ne?" Ya yi dariya ya ce "A'a ?aisar ne. Idan ma ba ni ba ne, ai kina ganewa"

Ta yi dariya ta ce "Wai Sayyid ya haka ne? Ka tsaya mu yi murnar ka samu sau?i"
Ruf ya rufe bakin Nana, bayan ya tabattar da lafiyarsa ta dawo. Duk da ya yi farin ciki da mi?ewar da hannunsa ya yi, wanda farkawa ya yi daga bacci kawai ya ji hannun ya saki, duk da ya yi masa wani iri babu daWi.

Bayan wani lokaci, ya saka hannunsa ya Waukko fitila a gefen Nana, ya kunna ya haske ta. Rufe fuskar ta ta yi, ta juya bayan ta da sauri.
Ya kwanta a jikinta yana yi mata raWa a kunnenta. "To tashi ki haska ni ki ganni, kin ga hannun" Nana ta ?are rufe fuskarta a fulo, ta ?i Wagowa.
"Kin ga" ya yi maganar yana taSa ta da hannun. Shi wannan abubuwan da take yi ma, ba ?aramar dariya take ba shi ba.

Da ?yar ta tashi, tana kallon hannun nasa da take ganin, tamkar almara ya mi?e.
Ta ja hannun ta ga ya mi?e, ta ce "Kuma ba ya ciwo?"
Ya girgiza kai yana taSa hannun ya ce "Ba ya yi"

"Allah ya ?ara maka lafiya mai Worewa"

"Amin. Na gode. Na gode" ta rufe bakinsa ta ce "Ya isa haka. Allah za mu godewa"

"Alhamdillah. Amma ya zama dole na yi godiya, kuma na jinjina miki, saboda" bai ?arasa maganar ba ta cije shi a kafaWarsa, kamar yadda ya kan yi mata, idan yana jin raha.
Kamar ba su ne cikin zullumi da damuwa ba, suka koma shagalinsu. Dare ya tsala amma tamkar rana a gare su, ?arshe ma zaman hira suka zauna. Da anjima sai ta tattaSa hannun nasa, dan ta tabattar lafiya kalau yake bai kuma ma?alewa ba.
Haka suka kwana cikin nishaWi, da kewar juna.
Da safe ta gama abin da take yi, ta shigo da maganin da take shafa masa, ya kalle ta ya ce "Wallahi ki ka zo kaina da wannan abun, sai na yi miki wanka da shi, ke ma na kulle ki a Wakin, ki ji abin da nake ji" Ganin yadda ya haWe rai ya sanya ta rabu da shi.
Wunin yau ma lafiya suka yi shi, babu damuwa, duk da jikinsa babu ?arfi sosai.
Ya ci Abincinsa ya yi sallolinsa babu wata matsala. Sai dai yau ma Nana ba ta samu rintsawa yadda yakamata ba, sai da ta san ya warke. Wani nannauyan bacci ya yi awon gaba da ita.
Wani mutum ta gani a tsaye a jikin bishiya, ya lulluSe jikinsa da mayafi. Ta yi tsuru tana son ta ga waye haka.
Yana Waga mayafin ta ga fuskarsa, ta ja da baya, ta tsorata. Tsohon nan ta gani, jikinsa yana ta fitar da wani irin ba?in abu, fuskarsa ta yi ba?i ?irin, ga haya?i na fitowa daga cikin bakinsa da hancinsa gaba Waya siffarsa ta yi muni babu kyawun gani.

Sai da Nana ta ja da baya, cikin tsoro da razani.

"Kin tafka kuskure yarinya, kuma za ki san kin taSa Giyaz bin Jaddul Jinn. Babu wanda ya taSa karya alkadarina, abu ya yi tasiri sosai haka a jikina. Dan a duk lokacin da aka yi yin?urin illata ni, barin guri nake yi. Sai dai kash kina Wauke da abin da aka yi mini tarko da shi a wancan karon." Ya jefo mata wani littafi jikinta ya ce "Ga shi nan, littafin da ki ke ta bibiya sai kin ji ?wa?waf, ki ?arasa karantawa kafin na je na yi jinya na dawo. Amma ki sani dawowata ba za ta haifar miki da Wa mai ido ba. Domin illar da ki ka yi mini sai na ninka wa mijinki, wahalar da ki ka sha ba ki ga komai ba." Kawai ya Sacewa ganin Nana.
Nana ta kalli littafin hannunta, na gurin ?aisar ne, da take ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login