Showing 3001 words to 6000 words out of 42684 words

Chapter 2 - YAR FILLO COMPLETE

29 Aug 2026

53

/>
Tayi murmushi tace " Kanwar Dadyn Safna mana saikace baka san taba kawar Zannurace fa kud da kud.

Yaja tsaki yace "batayimin ba plz aunty abar zancen nan iya nan dan

Walh bata ckn kalar jerin matan da nakeso na aura

Abdulhakim yagalla masa harara yace "aiko dai walh baka isa ka watsaya dadyn Safna kasa a idoba kama sani kamar anyi angama.

Yayo kan Abdulhakim da fada "to aishikenan ubana inka isa dani kadaura

auren ingani.

Aunty maryam ta daga masa hannu ranta abace tace "kai mara mutumci nixaka bawa kunya ni xaka wulakanta …

"Aunty ba wulakantaki nayiba gaskiya na fada

Tace "wane gaskiya kodai rashin mutumci meye da Ni,amah na rashin kyau da xa.a

k'ita gata da ilimi gata da kyau gasu da arxiki to me kake nufi da nuna kin aurenta ? Ko ka nunan ban isa ba kokuma ka wulakanta min miji kasa kuma inji kunya ko? To walh baka isaba wannan maganar saita zama babba dan saina kaita har gun Dady

Abdal

lah ya mike afusace yafuce yabarsu afalon

Ranta yabaci Abdulhakim yahau bata hkr "kada ki damu Aunty tunda har dady na kasar kawai kije kisanar masa kinsan kuma dole za.aiwa tufkar hanci.

Yai mata sallama yafuto yatarar da Abdallah ackn mota yanata

kumbure kumbura

Baikulashiba yashiga yajasu suka futa

Abdallah yace masa "kaga mallam kafuta daga ckn maganar kada kasa baki ack dan walh banga me yimin doleba

Abdulhakim yace "Aure dai dole kayishi duk gudunka ……

"To inga meyiminshi

ban shiryaba kokai dole akai maka naga kabani shekara uku atleast yanzu kanada 35 kaine ma yakamata asawa ido afarawa yiwa Aure baniba.

Abdulhakim yaharareshi yace "oho dai tabaya ta rago.....

*Auntyn Sayyada da Shahidah ce*[9/26, 6:08 PM] It

z B Y ebrerheem:

👌🏼

🐄

*"YAR FILLO*

🐄

_Dijen kauye_



🏕🏕🏕🏕🏕🏕



🏕🏕🏕🏕



🏕🏕



🏕

*True life Story*



*Nabilancy Luv*

💘

(Autyn S&S)

PG 10-15

Abda

llah yai kwafa kawai bai sake kula Abdulhakim ba har suka isa gida

Ransa Abace yashiga ckn gidan momy bata falon sai kannansa matan Zannurace jininsu yahadu sosai Tana ganinsa tahau fadin "oyoyo my bros "

Ya dallah mata harara ransa b'ace fuska b

a fara.a yawuceta yahaye sama dakinsu

Tatsaya kawai saroro jikinta asanyaye tana mamaki don bai taba mata hakanba

Itako mubina ko kula shi batayiba don bata shige masa ita yar dakin yaya Abdulhakim ce kud da kud dan hakama ganin datayi yaiwa zan

nu hakan saitahau dry tana fadin Allah yakara

😜

Amma ahankali don bataso zannun taji sbd suma sunayin yar tsama sako da sakuwane basa awa guda basuyi rigima dama yayun nasune yan rabon fadan

Takoma tazauna a kujera asanyaye

Ammafa taji ba dadi

tahau kuma tambayar kanta shin me akaiwa yaya haka? Toko nayi masa laifi jiya bansaniba?

Ganin yaya Abdulhakim yashigo saita mike cikeda kissa tana fadin "yawwa yayana dama kainake jira kashigo inji shin me akaiwa yaya awaje naganshi awani yanayi.

Fuskarsa shima ba fara.an ya amsa mata "meyasa baki tambayeshiba? To ban saniba

Yawuceta zai haye sama yaji mubina na masa sannu da zuwa ya amsa mata da sakin fuska harda tambayrta momy fa.

Zannura taqule taji haushi wai meyasa yaya Abdulhakim ke

basar ta ne ko yana nufin har yanzun bai gane sonsa takeba? Toko lallai tana gab da tafurta masa takawo karshen shariyar dayake mata.

Yana kwance adakin nasu yaji shigowar Abdulhakim bai daga kai yakalleshiba harya gama abinda zaiyi yafice abunsa

Juyi kawai yakeyi akan lallausar katifar dake kan katon gadon

Zancen Aunty maryam ke masa yawo akwanya shiko me zaiyi da yarinyar nan Ni,imah mara kunya Aigara yahakura baiyi aureba dadai yaxauna da ita amatsayin matar Aure

Yadauko wayarsa yai da

iling din lambar masoyiyarsa lowest

Bugu biyu ana uku ta daga dayake jakar kano ce ta iya hausa nan suka hau hira ckn hausarta kadan kadan amma sukan juye turancin

Awa biyu sukai suna shan hirar soyayya tana gaya masa takusa zuwa nigeria tanada

wani uncle nata a kaduna zata sauka gunsa ammafa sbdshi zataxo kuma tanaso suyi Aure intazo

Nan ya amince tareda yi mata alqawarin zai auretan

Sukai sallama yalula tunanin yanda zai tunkari dadynsa da zancen lowest domin gara kawai yabainata ga d

anginsa ko akyaleshi da maganar auran wata

*Hhhmm aganinka wannan mafita ceko ? Tabdijan da kasan Abinda zai faru dakai Abdallah da baka jan gwalo wannan maganar Auren kristan dinba*

😅🙆🏼

*********

Da daddare yasami dadynsa afalonsa

Ckn nut

suwa ya gaidashi aladafce

Dady da murmushi ya amsa yana fadin "mutanen kauyen rogo kun dawo lfy

"Lfy qalau dady.

Dady yace "Ya harkokin gonar da fatan komi na tafiya daidai?

Abdallah yace "komi lfy sai godiyar Allah ba matsala dady

"To

masha Allah haka akeso Allah yyi muku albarka dama nima wani satin nakeson zuwa kauyen tunda nadade banjeba.

Abdallah yagyara zama yafara kame kame don yarasa ta inda zai fara batun dayaxo dashi

Dady yagyara xama yace "ya akai ne Babana akwai magan

a ne?

Yahau sosa keya "eh dady me muhimmanci ma kuwa fatana dai Allah yasa kafahimci abinda nake qudirin yi na alkairi kakuma mara min baya akan maganar danaxo da ita.

Dady yahau fara.a "insha Allahu zanyi kokari fadi inajinka babanah.

Kai t

saye yacire shakku yahau batu "dady dama inaso in Auri wata yarinyane saidai ba musulma bace kumaa ba.a kasar nn takeba tare mukai karatu amma tabimin alqawarin musulunta inhar xan Aureta dan haka dady dan Allah badan niba kataimaka ka goyamin baya in sami

lada kaima kasamu ta hanyarta kaga annabi xaiyi...."dakata haka

Cewar dady ransa abace "kasan me kake cewa kuwa Abdallah? Agidana zaka kawo kristan in rfaye xanbarka ka auri Aljihun baya. To inma mafarki kake kafarka dan baxan aminceba kada ma kaf

ara tun wurima inaso kurabu kafin azo asami matsala maxa tashi kabar gurin nan kafin raina yabaci dakai.

Sum sum yatashi yafuta ransa ba dadi kamar yasaka ihu

Yabar dady da fada da kumfar baki dama dadyn nasu gwanine saidai ya iya zama da mutane ak

wai dadin zama ammafa inka taboshi ba dama

Koda momy tazo ta tararsa taji ba.asin fadan dayakeyi nan yazayyano mata komi

Da Allah yataimaka ra.ayinsu daya bata goyi bayan Abdallaah ba itanma bata amince ba

Tahau fadin "wannan iskancine ma da ra

inin hankali wayaga yayi wannan gwamutsen adangi aidan sunga anxuba musu idone ba.ayi musu dolen suyi aure bane tunda sun isa

Dady yayi kwafa "barni dasu zanyi maganinsu nan da watanni inbasu kawo macen Aure ta arxiki ba walh dakaina xan zaba musu k

uma saidai suganta ranar daurin aure in an daura ai gata suka samu shiyasa zasuyi abinda sukaga dama.

Washe garin da akai haka saiga Aunty maryam da batun Ni,ima taxowa dady da zancen

Nan yahau ya zauna yace tayi masa ita zai karba yabashi tunda

har abin yazo da hakan saidai kawai ranar daurin aure yaji andaura masa aure

Momy ta amince da haka. Itama auntyn ta amince

Yasa Abdulhakim gaba yace yafito da macen aure nan da wata 2 inba hakaba zai musu aure da duk wacce yasamo musu

Abd

ulhakim yaringa jin

Haushin Abdallah danshi yajaxa musu wannan hukunci shi yanzun ina yaga wata budurwa shida ba kula mata yake ba,? Tab yanxu ya xaiyi

Abdallah baisan budirin ayake ba

Haushin dady yaki amincewa da bukatarsa yasa yahada kaya yata

fi hutu gidan yayan momy wani lauya ne dayake zaune a Gombe

Uncle Ahmad attajirine yanaji da Abdallah tun yana yaro dama yana xuwar masa hutu gidan akwai sa,anninsa da jininsu xahadu amma terrorine basaji suma yan rawar kaine yusuf da umar

Yanda r

an dady yabaci da tafiyarsa haka ran Abdulhakim yabaci don yasan daya san xai tafi baxai barshiba bada motar gida yatafiba lallai abokinsa yayi fushi da gida tunda har ya iya hawa motar haya

Abin yatsayewa dady rai domin fafutuka yagama musu na bude

musu wani babban kamfani yakuma yakuma basu mukamai aciki Abdallah yasami babban matsayi kowanne nada office ack da kuma babban matsayi na bangaren abinda xai tsare

Aranar da dady yasa zaije kauyen rogo aranar yashiryi tafiyar shida Abdulhakim

Dady nason Abdulhakim sbd yanda yake masa biyayya ko d'an cikinsa baya masa

Inhar yaxartas masa abu to ya zauna baxai musaba balle daga murya ballantana takai dayai fushi dashi

Koda suka sauka agidan gona

Dady yana canyana hutawa

Abdulhaki

m yaxame jiki yatafi gidansu kawarsa

Ta tsala kwalliyarta ckn kayan saki tayi ubansun kyau tamkar dan ita aka sak'a kayan

Ta dauko tallan furar tafito zaure kenan taga ansako kai ciki

Tsorata tayi ta daka tsalle gefe hannunta rike da kwarya

r nonon

"Handi in boni ni dije wayyo Allah na... tana shirin juyawa takoma ckn gidan knn taji muryar abokin birni yana cewa "dawo kawata matsoraciya ninefa aboki

Asukwane tajuyo suka hada idanu tace " Ashe!?

"Ammafa kasa natsorata dayawa to ya

ushe agari haka?

Yakasa shigowa ckn zauren yace "yanzu yanzun kuwa tare muke da dadynmu yana gdn gona ma yanzu haka

Takama baki tace "laaa kace tare kukaxo a,a lallai bari nayi masa damu na musamman kakai masa.

Ta dire kwaryar da sauri tash

iga gida tadauko kwanan sha mekyau sabone ma tahau damu da sauri harda suga tasa

Furar taji nono mekyau mara tsami

Ta rufe yana tsaye yana kallonta da sha,awa yanda tayi kwalliyarta gwanin burgewa

Ta mika masa tace "rike ka kai masa kace inji

ni.

Yakarba yana dariya yace "saidai kizo muje kikai da kanki.

Takama baki tace "wuuuh rufamin asiri kada yaganni yar kauye yace min kaxama kamar dan,uwanka yaki sha.

Abdulhakim yace "ashe kina yarda da zancensa? To bari kiji khadija keba kaxama bac

e hassada kawai yake miki kinada kyau kinada tsafta kada ki damu muje kikai masa dady baida wulakanci bakuma zaiki shaba dan fura mutuniyar sace.

Tace "gaskiya baxanje dan,uwanka yaimin wulakanciba dan baxan raga masaba ko gaban waye.

Yayi dry yace "

sha kuruminki badashi mukazoba.

Jin haka yasa tace "to zankai masa amma kaxo muje infara kai furata bakin kasuwa kada wasu su tsaremin guri ko.

Yace "a,a zansiye furar yau inyaso sai akaiwa momy dan tanason furarki nataba kai mata tayita santi.

Bayanda ta iya haka tashiga gaba suka tafi gidan gonar

Shike rike da kwananshan damammiyar furar dadyn

Dady na kishingide sai ganin bafulatana kyakykyawa yayi tashigo kanta dauke da kwaryar nono sun nufoshi itada Abdulhakim

Har kasa ta durku

sa ta gaidashi

Ya amsa yana fara.a

Abdulhakim yadire masa fura yace "dady ga fura maikyau daga khadija gatanan surukar kace taxo gaidaka.

Wata kunyace tarufe dije donjin ance ita surukar dady ce

Ashe dama ba ita daya ke fama da ciwon son Ab

dulhakim ba shima yana sonta gashi har xai iya furta cewa ita suruka ce gaban mahaifinsa

Taji kamar tatsaga kasa tashige takasa daga idonma takalli dady don kunya

Dady ya kafa kai yad'and'ana take yahau santin fura

Yace mata "kai masha Allah amma

naji dadi surukata y

asunanki?

Kanta akasa tace " *Dijen kauye*

Kamar yadara saikuma yadake

to ai dama dijen kauyece

😅😅

"Sannu kinji nagode Allah yayi mk albarka.

Ta mike akunyace tace "Amin.

Dady yazaro kudi baisan yawansuba y

abaiwa Abdul yace "gashi abaiwa khadija tukuici

Abdul yai godiya yace "to muje atahowa da momy tata furar.

Nan suka tafi suka bar Dady yana shan fura me dadi ko abirni yadade baiji kamar taba

Tas yashanyeta kuwa

Nan Abdul yadawo yatararsa yaxau

na kusa dashi Dady yace "a ina kasamo wannan yarinya me nutsuwa da kirki haka.?

Abdul hakim yace "Ai dady tun xuwanmu kauyen nan Allah yahadamu take mana hidima ita da iyayanta duk adalilin tana son Abdallah Amma bakaga yanda Abdallan ke mata wulakanc

iba

Dady yaharxuka "Au dama Abdallah takeso? Ainazaci ko budurwar kace danaji kace surukata lallai Abdallah yacika mara kirki wato ga yarinya me hankali tana sonsa shine zaikawo mana arniya wacce ma bamusan asalintaba to tabbas zanyi maganinsa anan z

an tsaya tsayin daka inga tazama matarsa kabarni dashi ayau zuwa gobe kafin mutafi zanje ga magabatanta atsaida magana kada ka kuskura kagaya masa ta waya dan sai andaura auren tukunna yasani

Ran Abdulhakim yai fari dama target yahada kuma yakama sbd

yaci alwashin saiyayi maganin Abdallah na abinda yakeyiwa khadija kawa

Cikin kwantar da murya Abdulhakim yace "to Amma dady ba anyi zancen ni.ima ba?

"Kabarni da duka zancen nasu ba xanjanyeba tare zan daura auren dana yar fulanin nan dana ni,imar

duk su xama matansa inga ta tsiyar Auran kristan kuma duk inda yaje ai dole yadawo.

Abdulhakim yahau gyada kai

Can kuma yahau tausayin Abokinsa amininsa daya tuna yanda yatsani matan nan guda biyu gashi kuma zasu zama matan sa wai yaya kenan ………??

?

_Muje zuwa_

[9/26, 6:08 PM] Itz B Y ebrerheem:

😅😅😂🙆🏼

🐄

*"YAR FILLO...*

🐄

_Dijen K'auye_



🏕🏕🏕🏕🏕🏕



🏕🏕🏕🏕



🏕🏕



🏕

*True life Story*

*Nabilancy Luv*

💘

(Auntyn S&

S)

PG 15-20

Kwana yakama dady a kauyen Rogo domin baa shirin kwana yazoba

Dole saida yaga mahaifin Dije wato marikinta knn mijin addaji

Baffa yawale mutumin kirki Yatarbi Dady cikin karamci da murnar ganinsa domin duk cikin k

auyen ansan dady da irin taimakonsa ga wanda bayadashi gashi da son shiga ckn dattijan kauyen inyazo shiyasa kowa yasanshi

Baffa yawale yai masa shimfida azaure suka gaisa a mutumce tareda gabatar da juna

Dady yace "Nasan kasanni amma ni bansan

kaba saigashi Neman Aure yakawoni gidanka yara sun hadamu.

Baffa yace "to!to madallah naji dadin hakan.

Dady yagyara xama yace "wato dama d'an wajena ne yake son "yarka nikuma Shine nabiyo baya domin atsaida maganar Aure kuma banason aja kwanaki d

ayawa.

Baffa yace "waye kenan yake sonta ? Yasunansa ? Ko wancan na wajen danaga kunzo tare? Yana nufin Abdulhakim da sukazo tare yatsaya awaje

Ddy yace "Yana birni bamuzo dashi ba yayi tafiya dafatan za.a bamu auran khadijan domin so nake nan da s

ati mudawo adaura auran kuma bana bukatar asiya mata komi zanyi mata kayan daki da duk abinda yakamata .

Baffa yaji dadi sosai har ransa take kuma yai amanna da wannan daddad'an batu yacewa dadyn '"Naji dadin wannan magana takaruwa da farin ck dakaxom

in da ita nidai anawa bangaren na amince saidai kuma akwai wanda yake tamkar jigo gareta da zan gayawa kafin atsaida ranar daurin auren

duk da nasan shima baxai ki ba kanin mahaifin tane don ni daka ganni kanwar mahaifinta nake aure yarinyar marainiyace ri

konta nakeyi kawai.

Dady yagyada kansa yace "Allah sarki A ina kanin mahaifin nata yake domin inaso inje dakaina nasameshi muyi mgnr sbd agobe sassafe zankoma

Da baffa yaga Alh mustafhan amatse yake da zancen saikawai yatashi dakansa yarakashi ha

r gidan kawu Amadu

To shima kawun nata mutumin ne me saukin kai kuma yaji dadin wannan magana taneman Auren dije da murnarsa yakalli baffa yace "to inbanda abinka baffa yawale kaida diyarka meye naka nasaikaxo guna neman yardata Alhalin duk dayane kum

a "ya dai takace kyauta aka baka komi kayi daidaine tunda baxaka cutar da itaba

Baffa yace "wannan ai dole ne inga nabaka hakkinka kada kuma nayi abu nikadai

Kawu yace "to hakane amma saidai naji kuna batun ayi biki kwanannan aikyanta abamu lok

aci sbd musamu damar yin kayan daki tunda birni zata xauna balle muyi mata "yan tagajan tagajan

Nan baffa yai ms bayanin da dadyn yai masa kan cewar su zasuyi mata komi basai sun wahalar da kansuba

Ai dajin haka kawu ya aminta da batun tunda Alla

h yahutarsu

Kafin dady yatafi saida yadire sadaki dubu dari komi da komi gaisuwar iyaye nagani inaso toshi, sannan yadire dari yace abaiwa amarya tayi siyayyar kayan da zatayi fitar biki da sauran hidima

Sosai sukaita mamakin wadannan dubban kudade

n don basu taba ganin ankawo su haka a auren kauyenba

Kudin agun kawunta yk domin baffa yace shiyafi cancanta yarike bashiba dukda saida akai tirjiya kafin yakarba shima

Koda baffa yaxowa da Addaji batun tayi murna sosai tasawa abin Albarka

A

al,adar kauyen kuma ba.a taba zanta Auren budurwa Agabanta balle agaya mata inhar antsaida mk da miji saidai kawai kiji anayi

Hakama in ita takawo mijin to idone nata kawai

To wannan ce tafaru ga dije domin kuwa kwata kwata batasan bidirin da akeyib

a na Auren da za.ai mata

Itadai akullum tana tunanin Abokin birni tana jin zugin sonsa aranta tana tunanin ta yaya zata gaya masa tana sonsa tunda yaki ganewa

Shiko Abdulhakim ransa qal yai mugun qulli tsakanin dijen da Abdallah dama can yasha aiya

na cewar inama yaga Allah yakaddara auren Abdallan da dijen yaga shin yaxaiyi yaga yanda zaiyi da rayuwarsa tunda yazama mijin wacce yafi tsana aduniya.

Murmushi kawai yakeyi inya hanga yahango irin xaman tabbas yasan akwai daru da tirka tirka

Saiy

aringa jin kuma tausayin kawar tasa yasan tabbas zata shiga wani hali tunda itanma ba son Abdallah takeyiba tatsaneshi shine shaida to amma zaici damarar taimaka mata azaman da zatayi da Abdallah ganin bai cutar taba zai ringa kai kafa akoda yaushe domin d

ebe mata kewa can wata xcyr tace dashi shin kodai akwai son khadija aranka? Dasauri

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login