Showing 21001 words to 24000 words out of 42684 words
kifara daga farko ko kuwa bakyaso abari?
Khadija data kankame waya tana faman farin ciki tahau naxari anya kuwa zatayi karatu kuwa?taji fa ana cewa akwai wahala
Tanadason taga yau itanma t
anajin turanci saidai tasan zatasha wahala sosai kafin ta iya wasu abubuwan takalli wayar hannunta tasan ita kadai darasine akan rashin ilimi domin inbakada ilimi ma hatta waya gagararka take ka iyata koda calculata ce
Tanaso kuma ace itama tazama wayay
yiya kodan yan iskan mata yan rainin hankali irinsu Zannura
Dady ne yakatseta da cewa "khadija inkinga bakya ra,ayin karatu bazan takura mk kiyi adoleba dama ra,ayinki nake sonji tunda kokin aminta sai in mijinki ya amince sannan zansa ya nema miki.
Dije ta dago kanta asukawane takalli Abdallah dayake ta danne danne awayarsa kamar bayajin abinda dadyn ke cewa ma
Takalli dady tace masa "na amince dady inaso
Dady ya gyada kansa yace "yayi kyau to Kai Abdallah kaji khadija nason karatu ta amince i
nnema mata kaima ka aminta?
Kansa akasa yana amfani da waya yace da dady "wannan ba matsala bane na amince tayi karatunta.
Dady yace "to ai shikenan saika nema mata akusa da gidanka kuma mekyau nakeso ta fara daga primary yakamata tafara
Abdall
ah yakarkace kai yakalli dije yace "yanzu dady wannan gododen ce zatayi primary ackn yara ? Lallai amma zata zama maman yara kenan
Momy ta tareshi da fadin "to inbanda abinka Abdallah nawa khadijan take da baxata shiga ckn yara ba itada natabbatar ko s
ha bakwai batayiba sannan kuma ai tanada fuskar yara girman jikin me kawai kaidai kawai kayi mata fatan Alherin.
Dady yace "koma dai meye banaso asami matsala nabar maka komai ahannunka indai private ce zasu karbeta ko aji nawa ne tunda kudi za.a kashe
don haka banaso asami matsala katabbatar kuma kai zaka ringa kaita makaranta kanaji
Ran Abdallah abace ya amsa da to kawai badan yasoba
Abu dayane yafaranta masa rai dayaji har zuwa wani lokaci iyayan nasa basui masa magana akan ko dijen takawo karar
sa ba sai hankalinsa ya dan kwanta don ya zaci ko yanda tace masa zata fada din ko ta fada.
Duk yanda ta wakana afalo akan zancen saka dije makaranta Abdulhakim yaji tas dayazo saukowa amatatttakalar benen ransa bai masa dadi ba sbd bayaso ace khadija t
ana futa kullum sbd yasan inhar akace yau khadija ta waye ta bude idonta to za.a sami matsala yatabbatar baxata zauna da dan,uwan saba.
Daki yakoma yazauna akan gado yadafe kai yahau tunanin mafita
Abdalla yashigo dakin nasu yana fadin " dan,uwa wai
dama kana cikin gidan Amma banji motsinka ba?
Abdulhakim yadago kansa yakalli Abdallah yakakaro murmushi yace dashi "ina cikin gidan banfita ba banajin ddi ne.
Abdallah yabashi hannu suka gaisa yace masa "sannu friend ko akwai damuwa ne?
"Babu wa
ta damuwa kawai dai baccine da bai ishe niba jiya nakai dare sosai ina ciccike files dinnan da za.a fita dasu gobe
Abdallah yace masa " Ayya sannu dan,uwa Allah yasauwake.
Amin
Harya juya zai futa Abdulhakim yakirashi yawaigo yace "akwai wani a
bunne?
Abdulhakim yace "kwarai xoka zauna muyi magana me muhimmanci ma kuwa.
Yaxauna kusadashi
Abdulhakim yagyara zama yace dashi "uhhmm akan maganar Khadija ne dama.
Gaban Abdallah saida yafadi domin yasha ko zancen dasukai na shan giyar da
yai ne da ita ko dama Abdul din tagayawa aiko yana shakkar Abdulhakim yaji sbd baya masa ta dadi zai iya juya masa baya su bata
Abdulhakim yace "wato naji maganganunku dasu dady daxu akan batun saka khadija makaranta da za.ayi nikam banso hakan ba ban
so kuma naji ka aminta ba sbd khadija bata san kowa ba akano saimu inajiye maka halin matan birni da maxuga kaga lafiyar Allah take kada tazo ta shiga sch tahadu da muggan kawaye su canxa mata ra.ayi akanka taxo tafi karfinka dan haka ina me kiranka da bab
bar murya akan kadakatar tun wuri sbd....
Abdallah yadaga masa hannu "dakata Abdulhakim wato inna fahimta so kake kace min nan gaba zata iya fin karfina kenan?
Gyada kai kawai Abdulhakim yayi
'"Ta dade batafi karfi naba walh ni da hakan zata kasan
ce zanfi kowa son hakan sbd kai shaidane natsani yarinyar bana sonta adole nake zaune da ita to meye nawa dan tashiga sch aini fatanama Allah yakawo ranar rabuwa ckn sauki ko Allah yasa nasamu na Auri burin raina lowerst
Wani mugun tsaki Abdulhakim yaj
a masa yace "akullum kana bani mamaki domin kana kawo abinda bazai taba yiyuwa bane kuma baxaka gane anmaka gataba sai nan gaba.
"Aini walh ba gata akaiminba dan ancuceni antauyeni kuma nasan dasa hannunka tunda da ace kahana dady da hakan batayiwu ba s
bd yanajin maganarka yana kuma bin abinda ka kawo to amma dayake kashuka min mugunta aikaima boyemin kayi inba hakaba tunda anjona min Ni,ima tokai meya hana ka karbi yar kauyen? Kawai dai bansan nufinka nayin hakanba sbd dakai ta dace kuma kagujeta nikuma
baxata taba samun farin ciki aguna ba sai bakin ciki.
Abdulhakim yace "nikuma inhar ina raye baxan taba barin khadija ta kasance a ckn bakin cikiba... "to ko insaketa ka Aureta danta samu farin cikin? Yatambayeshi ahasale.
Abdulhakim yace "wannan
kai ta shafa gaka ga khadija ga dady nan kakuma san irin hukuncin daya yanke maka nasakin daya daga cikinsu dan haka _is not my concern_
Abdallah yabuga masa tsaki yafuce
Koda yasauka kasa falon bai tadda kowa ba su dady sun tashi haka suma su mubi
na da dije sunkule adakin mubinar
Kai tsaye gidan abokinsa Anwar yawuce domin kwakwalwarsa tadau caji dayawa ruwa yawatsa sannan yazo falo yabaje adoguwar kujera yanashan sigari hankali kwance yana waya da babynsa lowerst
Sai faman zuba masa shagwa
ba takeyi harda kukanta wai itakam _she miss him over_ gaskiya zata diro nigeria akarshen wata koya shiryi tararta bai shiryi xuwantaba dole zatazo dai
Babu yanda zaiyi da ita adole ya amsa mata badan yasoba
**********
Sukuwa su Zannura da Ni,ima
can wani kauye suka je me suna kaburma dake yankin dawanau kwatance sukabi suka kai kansu
Sunsha wahala kafin sugano gidan malamin me suna mallam matawalle wanda ake masa layi sai mutum yayi kusan awa guda kafin aganshi dan cikowar dake gun
Suny
i budu budu dasu nakurar jar kasa wanda danma a achaba suka karaso gidan
Suma layin suka hau don mutane sunkai 20
π±
suka tarar
Dakyar dai da hakuri da juriya suka samu suka shiga dakin da mallam yake
Mallam matawalle yaji bayanin da Ni,ima
takoro na yanda take zaune da mijinta amma baya sonta
Mallam yace "me kk so ayi masa?
"So nake mallam asaka masa azababben sona a zcyrsa wanda zaizamo ma duk abinda nace shi zaibi kuma inaso yarabu da kowacce mace yatsaya akaina kawai
Yahau gyad
a kai sannan yayi rubutu ajikin kasa yabukaci jin sunanta dana mijinta fada masa
Yayi surkullensa yagama sannan yahada mata magunguna nawanka dazatayi da kuma na turarawa da wani rubutu da zata ringa yayyafa masa afilon dayake kwantar da kansa akai inxa
iyi bacci sau uku
Dubu 20 tabashi tana godiya suka tafi ckn farin ciki
Koda suka fito dg kauyen saida suka siyi ruwa suka wanke kafafunsu dankar aganosu agida
*****
"Yanzu matar yaya dan Allah harkin gaji daga dan wannan aikin da kikayi
.?
Mubina ta tambayi dije tana me jan babbar silbar fulawar da suka buga gabanta
Dije tahau dariya tana fadin "ke walh bakida tausayi mubina yanzu duk irin wannan Dukan da naiwa fulawar baisa kinyabamin ba saima mita xakiyimin Allah zangudu gun
momy
Dije takarasa fada tana dariya
Mubina tace "haba matar yaya ke yanzu saiki tafi kibarni da uban aikin nan me yawa kinga fa ko cincin din bamu fara ba cake kawai mukaifa bamuyi su samosa ba balle azo kan meet pie
"Kai yau naga ta kaina
dai danazo taya aiki gashi za.a wahalar dani akan za.a burge sirika
Mubina tahau dry tace "to amma dai naga kema zaki amfana tunda ko banza zaki gwanance awannan bangaren ko.?
"Eh kumafa hakane. Dije tafada. Tana janyo silbar gabanta kinga bani wan
nan aikin kama wani kawai.
Haka sukaita hira har suka gama abubuwan da suka tsara zasuyiwa saurayin mubina faisal wanda zaitafarwa mamansa shi dayake tana son mubina tana mata aike sosai shiyasa itama yau zata burge
Koda Su Ni,ima suka dawo basub
i takan su Dijeba sai suka qule suma adaki suna qullequllensu
Cikin ledar take Away taf mubina tabaiwa dije snaks din ta tafi dashi don magriba nayi Abdallah yaxo Daukarsu don komawa gida
Abdallah Sbd Ya qular da dije sai yace da Ni,ima "ke shi
ga gaba dan kinfi kalar gaban mota
Aiko ta shige tana wani yauki da yatsina Wai nan annuna mata so
Allah Sarki dije ko ajikinta don hankalinta kwance tashiga baya ko afuska bata nuna jin haushin hakanba β¦β¦β¦β¦
_muje zuwa_
π
*YAR FILLO*
π
_D
ijen Kauye_
πππππππ
πππππ
πππ
ππ
π
*True life Story*
*Nabilancy Luv*
π
(Auntyn S&S)
*SADAUKARWA GAREKU*
*Takwarorina abin Alfaha
rina ina yinku!ina sonku!!inaji daku manyan mata!!* Luv you all....
*Nabila maman khalil*
*Nabila Rabiu zango*
*Nabila Dikko*
ππππππππ
_Kaga hazik'an marubuta kaga jaruman marubuta kaga Nagartattun marubuta anbuga anbarku kun iya kun huta
Nabil..-Bil..'s_
ππΌππΌππΌππΌππ
PG 75-80
Abdallah yashiga tambayar kansa "shin wai son yarinyar nan nake yi kome? Wai yaushe ma zan daina mata kallon mata tane? Yar kauyen har yau zanji kishinta wacce natsana.yarinyar da ba wayyiyaba
.,mittsss!! Yaja tsaki tareda tashi yafuto daga dakin yai zaton zai tadda Abdallah don yabagarar sugaisa sai yaga ashe yatafi ma.
Tana zaune akan 3 siter tanata buga game abinta ko daga kai takalleshi batayiba duk da taji motsinsa
Shima kallo daya
yai mata yafice ransa nai masa quna
Baisan daliliba ganin yarinyar natada masa wani abu arai bayama inyaganta ayanayi irin nayau.
Ranar Asabar yana kwance akan doguwar kujerar dake falon da lowerst takama a hotel din da remote a hannunsa yana c
kn chanza tasha babyn nasa ta fito daga toilet da tawul ajikinta iya guiwa tazo ta dane cinyarsa tana fadin "ohh!my real gaskiya yau saika kaini yawo na zaga gari inba hakaba baxaka je koina ba kuma sainaje na nemi gidan dady ayau.
Da sauri yazabura y
azauna daidai yana fadin "zan kaiki babyna shirya shirya maza inkaiki kada ki ballomin ruwa.
Ta tashi daga kan cinyar nasa tana dry tashige dakin gadon nata ckn yan mintina ta shiryo ckn riga da wando tafito tana tashin kamshi
Yakalleta ckn mayen
so da sha.awa yace mata " _your dress is fine my baby_
tahau yarfa hannuwa tana murmushi tace "tanks my real.
Yadauki key dinsa akan table yai waje tabishi abaya.
Gidan Anwar yafara kaita sukasha hira suka kuma kora abar
Sun watse acan don
sun tadda wasu makakkun mata gogaggun "yan bariki acan sunata shan shisha
Kafin su tafi matan sukai sabo da lowerst har musanyen lamba sukai "yammatan subiyu musulmaine
Anwar yaita kallon lowesrt kamar maye dan rayawa yai aransa saiya dandaneta shim
a don tayi masa
Duka '"yammatan fa dama nasane amma dan hadama bai hkr ba kai
πͺππΌ
A dabarance ya kwafi nambar lowerst dayaji tana baiwa yammatan nasa
Grand Squar yakaita tayo siyayya na kayan kwalan da abubuwan bukatu sannan suka fito
Akan
hanyarsu ta komawa hotel yaji wayarsa na ring
Yana dubawa yaga Dadyne yad'aga da sallama
Aiko amsa masa sallamar baiyiba yabal baleshi da fada "Abdallah bakajin maganar mahaifa kafuta daban ackn yarana,maxa maxa kazo gida yanzun nan yaron banxa y
aron wofi.
Ckn kidima ya amsa da "To dady ganinan zuwa yanzun.
Yana kashe wayar yakalli babynsa dake gefe guda yace mata "Dady ne baby fada yake tamin bansan daliliba yace min maxa yanzun inje yana son ganina.
Tayi fari da ido tace "to muje mana.
Yazaro ido yace "ke!kina haukane ?dawa zanje ke?tabdijan kice akasheni yau knn haba baby keda naketa boyeki sbd tsadar ki to meye amfanin aganka da wacce zaka Aura mukam akwai matsala hakan a addininmu
Ta lumshe idonta tareda budesu tar akansa tace "
to ba matsala ka kaini masaukina saikaje din.
Yai kasa da motarsa daga kan kwalta yarage tafiya yatsaya cak yakalleta yace "ina girmama maganar dady na bana so inga yana min fada sosai kuma tunda kkga hakan akwai matsala dan haka kiyimin afuwa kitari ma
shin dan sahu kije zanzo da dare muyi maganar
"To amma dai inkazo kwana zakayi ko? Tafada da shagawaba
Ya daga kansa yace "kwana biyu ma kuwa.
Yazaro kudi yabata
Takarbesu kuwa tafuce
Yaja motarsa sai gidansu gabansa na dukan uku uku
***
***
Wani bugawa da kirjinsa yayi kamar anbuga durom saida najiyo bugun don fargaba data d'arsar masa naganin falon ack da "yan gidan gefe guda azaune akan kujera dady da momy ne
Sai Aunty maryam acan kan one siter azaune
Mubina na gefe akasa z
aune ta zabga tagumi kanta akasa
Zannura kuwa tana gefe itama sai kuka takeyi kasa kasa tana share hawaye
Abdulhakim na zaune kansa shima akasa yana goge zufa
Jikin Abdallah yagama bashi babu lfy yau agidan
Asanyaye yasamu guri kusada Abdulhaki
m yazauna
Yagaida iyayan Nasa ckn ladabi
Dady yahau harararsa yana fadin "gaka dai kamar na Allah to amma ashe me sabon Allah ne tahanyar dayafi tsana shan giya... "wa,iyazubillah.
Wata zufa ce ta karyo masa agoshi yahau sharcewa
Dijece tafado
masa arai domin ita kadaice sukai zancen yana shan giya yakuma roketa Alfarmar karta fada
Ya manta da Ni,ima taganshi ahalin maye ko don ba.a hayyacinsa taganshiba kuma basuyi maganarba
"Yaushe kafara shan giya bansaniba "?
Dady ya watso masa yam
baya wacce yakasa amsata
Dady yadubi Abdulhakim yace "kai.fadamin yaushe dan,uwanka yafara shaye shaye bansaniba? Nasan lanada masaniya saidai in boyemin zakayi amma kasan komai akan Abdallah.
"Walh bansanshi da dabi.ar shaye shayeba saidai in yanz
u yakeyi bansaniba
Abdul yafada asanyaye
Abdallah dayai tsuru agefe dabara tafado masa ckn ladabi kansa akas yace "Walh dady bana shan komai na buguwa abinda yafaru ranar munje wani partyn abokina nida wasu abokanmu to sai mukai dare kuma sukaimin mu
gunta alemo suka saka min abinda zai bugarni walh anan nasha yabugarni dan Allah dady kayi hkr kayafemin bada sanina nasha ba .
Dady yace "ohhh!nayi zaton koka fara shan giyane da sai ince kasako min yarana don baxan yarda su zauna da dan giyaba tunda
akwai cutuwa don wataran zaka iya dawowa kai mata duka.to amma tunda hakane ya wuce.
Ohhh shet!Abdallah yaji inama yafadi gaskiya dayasan za.ace yasakesu tunda yana a maxaunin mashayi walh inama yafada da tuni yarabu da alakakai.
Dady yanuna z
annura yace "kaga kanwar kanan zannurat tun daxu take mana kuka akan nace mata ta fito da mijin Aure taki domin nan da wata guda zan daura mata aure intaki fidda miji domin mubina da Abdulhakim zanhadasu aure tunda naga tasu tazo daya.
Abdallah yaji d
adin hakan sai yahau yiwa zannura magana ckn sanyi don jininsu yafi haduwa "kiyi shiru sis kifidda mijin kinji
Aunty maryam tace mata "kinga malama kitsahirta mana da kukan ya isa hakan.
Momy tace "kunga kukyaleta tayi mai isarta dole tayi shiru a
i.
Zannura bakin ciki da takaicine yasata wannan kukan son Abdulhakim ne aranta yanzu shikenan kanwar tace zata zama matarsa knn? Ko dai tafada ne kawai ko adawo mata dashi kanta.
Itanma mubina ranta ba dadi take jinsa domin tanada wanda takeso kuma
taga dai yaya Abdul ba sonta yakeba kawai dai Amintace ta yaya da kanwa tsakaninsu tokenan anxaci soyayya sukeyi yanzu yazatayi da nata saurayin dan fillo?
Abdulhakim dinma zufar dayakeyi bata dadi bace domin anmasa shigar sauri tunda a matsayin kanwa
ta ck guda yadauki mubina kuma sam bayajin zai iya son ta. To nawa ma take itada baifi watanni da gama sec.datayi yanzu yaya kenan bakuma zai taba iya bujirewa ba domin dady ubane cikakke yana masa ladabi da biyayya bai isa ayau yai masa musuba
Dady
yai tambayar duniya ga Abdul ko yanada ta cewa akan batul koda wacce ykso amma fafur tai shiru kamar yadda itanma mubina tayi
Ahaka taron yawatse babu mafita rai babu dadi domin Abdallah ne kawai ransa qal yasami mafita shikam yafidda kansa a gun dady
Yana zuwa gida sashin dije yawuce yataddata afalo tana kallo
Kai tsaye yakashe kallon dama yashiryi mata wulaqanci dan yana xaton ita tahadashi da iyayansa yau
Da daga murya tace "mallam meye hakan ?
Yace "na tsofaffine ?ko dasu kkzo? "Yar k
auye kawai
Ta bugi kirji da tsiwwa tace "fadi ka kara bana jin haushi dijen kauye nake kuma badasu nazoba amma kamar mallaki na suke tunda bakai kasakamin adakinba da kunnena naji agidanku ance kaf komai na gidan nan har gidan dadyne yabaka dan haka mey
e naka na gadara mallam.?
Yace
"Ohh!ranar da kikaje gulma da kai karar nasha giya knn? To karyarki muna fuka ke baki isa kihadani da iyayenaba don ayau na wanke kaina fadamusun da kkyi inashan giya baiyi tasiri aransuba kuma giya yanzu nafara sha.
Wannan kai tashafa kaida Allahnka.
"To inkinsan nida Allah nane meyasa baki barni dashiba kika gayawa su dadi kodon kin saba gulma.?
Tace "kai nafada da ban fadaba walh kai baka isa kayimin sharriba aiwalh danasan hakama dana fada din aikin banza
....saukar mari taji akuncinta har sau biyu
Ta dafe gun tana kuka ta zabura tayi kicin tatafi dauko madoki danta rama
Aikafin tadawo yafuce da sauri sashen Ni,ima
Ni,ima yau burinta yacika hakanta yacimma ruwa domin kuwa tatsala kwalliya ta gani