Showing 30001 words to 33000 words out of 70108 words

Chapter 11 - IZZAR SARUTA COMPLATE

kashe Dameer da Deeyanan ma gaba daya Amma kam d

ole ta dau mataki tun kafin abun yafi k'arfin ta Dan yanzu Dameer ya huce tunanin ta tunda har ya iya budan Baki ya gaya Mata magana "wayyyo Ni Haleematun-Sa'adiya ya zanyi da yaron Nan??".

Yana fita D'akin da aka sauke Yan Saudi ya shiga Dan tun ji

ya da rana rabon shi da saka kakar shi a Ido Yana shiga kuwa ya tatda ta kan sallaya tana lazumi zaunawa yayi a gefan ta San ya daura Kan shi a k'afan ta ya fara Mata magana cikin muryan shagwa'ba da harshan larabci.

"Jaddah na kin tashi lafiya ya b

akun ta dan nasan yanzu kena nan kina yi tunda zaman Nigeria sai mu da aka haife mu a cikin ta" shafa kan shi tayi sannan cikin harshan larabci ta soma mai magana.

"Lafiya lau Alhmdllh ya kwanan kishiya ta da fatan tana lafiya? " Turu Baki yayi sann

an yace, "haba yanzu jadda baza ki fara tambaya ta ba sai wata can da ban ai Ni ya kamata ki fara tambaya ya na kwana tunda ke ma ai ban tambaya kowa ba ke na fara tambaya".

Murmushi tayi sannan tace, "kishi kike kenan tashi min a wuya su kake ka k

'arasa ni ka girma baka san ka girma ba yanzu haka zaka dungayi a gaban matar ta ka? ".

Tashi yayi tsayi sannan yace "Ni na tafi sai zuwa anjima kuma, Amma yau zaku koma ko?".

"Eh insha Allah yau zamu tafi Amma da Ammin ka tace, mu Bari mu taf

i gaba daya da ku Dan matar ka baza ta zauna a nan ba tunda a can kake gwara ta tafi can Kai ni ban iya surutu Kira ta zata gaya maka duk yanda muka tsara" cewar Jadda.

"To" kawai yace sannan ya fita a D'akin yana tunanin zance jadda shi kam ba wani

tafiyan da zaiyi da ita tayi zauniyar ta anan duk sanda ya zo shikenan Amma ba in dai zai Kai ta haka dai yake ta maganar zucin shi har ya k'arasa part din su, ko da ya shiga parlour kaman ba mutum a D'akin dan Deeyana tana bedroom a zaune ko fitowa parlo

ur batai ba ta k'ara yin wanka dai.

Hucewa bedroom d'in shi yayi toilet ya huce Dan ya watsa ruwa ya shirya sbd har fada zasu gaishe da mai-martaba, kusan minti arba'in yayi a toilet sannan ya fito shiryawa yayi cikin wasu kayan sarauta milk color bas

u da wasu kwalliya da yawa yayi kyau sosai sai ya fito sak a ainihin balaraban shi turare ya dauko yana fesawa noking d'in kofar parlour yaji ana yi sai da ya gama abun da yake sannan ya fito parlour.

Bude kofar yayi wasu bayi ne guda hudu rike da k

ayan abinci gaishe shi sukai sannan suka ce gimbiya Marwa ce ta aiko su su kawo musu breakfast, nuna musu hanya yayi da hannun shi suka shiga suka aje sannan suka fita, kallon kayan abinci yayi sannan ya tab'e baki yayi hanyae bedroom d'in Deeyana sai da y

a fara noking shurun da yaji ne yasa shi ya shiga.

Bata cikin Bedroom d'in tsayawa yayi yana kallon kofar toilet kaman yaji alaman karan ruwa, zaunaea yayi a kujeran bedroom d'in ya fito da wayqn shi yqna dan nawa kusan minti biyar sai gashi ta fito k

aran bude kofar ne yasa ya san ta fito daga kai da zaiyi dukai ido hudu ita da shi.

Gaban kuwa sai da ya fadi kallon juna suke wanda kowa yana tambaya kan san wannan wace irin kama ne muke haka?? duk kan su basu da amsar da zasu ba juna kusan minti

goma suna kallon-kallo can dai Deeyana tayi kasa da idon ta kirjin ta na wani irin bugawa shi din ma haka ne.

Tambaya yake ma kansa wacece wannan kaman mu ta baci to ko dai aljanna ce k'ara kallon Deeyana tayi wanda yanzu ta far bakin kofar ta koma

bakin Bed ta zauna ita ma tunani fal ranta, ya rasa mai zaice mata ma sai kawai yace, "kece Deeyana??" Shuru tayi kaman bata ji abunda yace ba dan hankalin ta ya gama tashi bata tab'a ganin mai kama da Abban ta irin Dameer ba shi kawai zai nuna mai fari ne

da kuma gashin shi da yake kaman na larabawa amma komai na abban ta irin na Dameer ne.

Shurun da yaga tayi ne yace, "maybe ke d'in kurma ce Amma in kece Deeyana ki shirya ga break d'in ki cen a Parlour" kallon shi Deeyana ta k'ara yi a karu na biyu

sannan tayi sauri ta saukar da idon ta kasa gaban ta na cigaba da faduwa.

Murmushi gefan baki yayi ganin yanda duk kaman ta tsorata sai kawai ya fita a dak'in da tambayoyi fal ranshi kuma bashi da mai amsa mai sai dai mafita daya ya kira Ammin shi,

bedroom d'in shi ya shiga sannan ya fito da wayan shi ya fara kiran Ammi ringing biyu ta dauka, "Ammi na ya kike ina missing d'in ki".

Murmushi tayi jin muryan dan nata sannan tace, "lafiya lau dan Ammi ya yata tana lafiya" yace, "lafiya lau Ammi n

a" "to madallah" cewar Ammi.

"Hmmmm Ammi kin san wani abu" gyara zama Ammi tayi sannan tace, "A'a lafiya dai ko??" "Ummmmm Ammi yariyar nan muna kama da ita sosai Ammi" "wacce yariya kenan Dameer??".

"Ammi yariyar nan mana da aka had'a ni da it

a" jin zancen Ammi tayi wani iri sannan tace, "ni fa Dameer har yanzu ban gane mai kake nufi ba ya zaka ce kana ma da yariya bayan kuma kace Ba'a masarautar yariyar take ba".

"Ammi baza ki tab'a gane mai nake nufi ba amma Ammi insha Allah zamu zo saud

i a satin nan dan kwata-kwata ban gane wannan abun da Momma ta had'a ba a zancen da take min tace, ita ma bata san yariyar ba wai makarantar

su taje anan ta fara ganin yariyar to Ammi kaman da muke da ita fa sannan jiya baban yariyar ya fad'a min wata kalm

a da har yanzu inq tunanin ta a zuciya ta".

Tashi tayi tsaye sannan tace, "Dameer gaskiya kam ina buk'atar ganin ta sabida akwai wani abu da mu bamu sani ba Allah ya kawo ku lafiya" "Ameen" yace nan dai suka cigaba da tattauna maganar.

Yan

uwa Amma kuwa haka suka koma gida suna yabon karamcin masarautar mure barin ma gimbiya Haleematun-Sa'adiya sunfi mata addu'a kowa yace tana da kirki sabida ta musu hidima Amma taji dadi sosai dan daman addu'ar ta kenan Allah ya ba yarta kwanciyar hankali d

a hutu to gashi ta samu sai dai fatan Allah ya basu zaman lafiya.

Misalin karfe sha-biyu gimbiya Aisha da sarauniya maimunatu suka shigo part d'in Deeyana dan shirya ta za'a kaita fad'a kuma za'a zagaya da ita masarautar gaba daya a bedroom d'in ta

suka samai ta, tana zaune sai tunane-tunane take sallaman su da taji ne yasa ta tashi da sauri ta gyara hijab d'in da yake jikin ta tana musu sannu da zuwa.

Da sauri sarauniya maimunatu ta rungume ta tana fadin, "my sister kin kwana lafiya ya bakunt

a?" Murmushi Deeyana tayi sannan ta dan dungusa ta gaishe su tace, "lafiya alhamdullh" gimbiya Aisha tace, "kinci abinci ko?".

Daga kan ta tayi alaman "eh" wanda zata shirya tane ta matso ta fara mata kwalliya su kuma suka fita zuwa parlour, sosai m

ai kwalliyan ta tsarata sannan ta miko mata kayan da gimbiya Aisha ta bata tace, shi zata ba Deeyana ta sa, masha Allah tana gama saka kayan mai kwalliya ta fara feshe ta da turaruka masu kamshi da daukar hanci.

Alkebba ta miko mata sannan ta fara s

anya mata, kai bazan iya tsayawa lissafo muku kyau da Deeyana tayi ba, murmushi matar tayi sannan tace, "gaskiya kinyi kyau gimbiya" ita ma Deeyana murmushi tayi sannan tace, "nagode" sarauniya maimunatu ce ta shigo taga ko an gama mata tana yin arba dq De

eyana ta tsaya cak ta kasa ko k'wak'waran motsi ganin Deeyana take kaman k'anwar ta a hankali ta fara takowa in da Deeyana take sannan tace,

"My sister kinyi kyau masha Allah" kasa da kai kawai Deeyana tayi taba murmushi a hankali sarauniya maimunatu

ta kama ma Deeyana hannu suka fito parlour, gimbiya Aisha ma zaro ido tayi tana mamakin kaman da tagani a fuskar Deeyana sakin ta tayi sannan ta shiga bedroom d'in Dameer dan ya fito su tafi, har lokacin jikin sarauniya maimunatu a sanyaye yake ta rasa mai

zata ce ma, Dameer tayi ma ma mgn sannan ta fito.

K'ara shiryawa yayi sannan ya fito samun su yayi a Parlour kowa shuru kowa da tunanin da yake a ransa, suna ganin shi suka miki sarauniya maimunatu ta mai shi gun Deeyana sannan tace, "doki ne zaku

hau ka rike ta".

Kai kawai ya d'aga mata sannan ya sanya hannun shi cikin na Deeyana dan bega fuskar ta ba ta saki hulan alkebban, a hankali suka fara takawa har suka fito harabar part d'in nasu fadawa ne suka iso gare su da sauri janye da dokuna.

Jikin Deeyana ya fara rawa dan bata tab'a hawa doki ba wani fari aka matso da shi gaban su sannan aka ce wannan na gimbiya ne ana nufin na Deeyana kenan, gyara mata akai sannan aka ce ta hau ai bata san lokacin da ta kara tamtsi hannun shi a nata b

a kallon ta yayi sannan yace, "lafiya?".

"Muryan ta na rawa tace, fadowa zanyi in na hau" dariya yayi har hakuran bakin shi na beyana yace, "daman kina magana ai nasha kurma ce" shuru Deeyana tayi kuma taki sakin hannun nashi sarauniya maimunatu da

take karasowa tace, "mai kuke jira my Bro's?".

Beyi magana ba sai ganin kawai da sukai ya dauka Deeyana ya daurata a dokin cike da tsoro Deeyana ta rike mai hannu tana girgiza kan ta, gyara wajan hawan yayi sannan ya hau dokin kin, gaba daya fadawa

sukai kasa da kai gimbiya Aisha kuwa tsayawa tayi tana kallon ikon Allah murmushi sarauniya maimunatu tayi sannan ta d'aga mai hannu.

Haka suka fara tafiya a kan dokin Deeyana ta rike shi gam, shi abin ma dariya yake bashi jin yanda jikin ta ke ra

wa, fada suka nufa fadwa wasu na gaban su wasu na baya sai busa da ke tashi, suna isa fada shi ya fara saukowa sannan itama ma ya taimaka mata ta sauko hannun shi cikin nata suka shiga fada guri na musanman aka nuna musu suka zauna mai-martaba sarki Fahad

Abdullah yana zaune a kujeran shi.

Gaisuwa Deeyana da Dameer suka kai ga sarki sannan suka koma suka zauna addu'a sarki Fahad Abdullah yace, ayi sannan ya fara musu nasiha ya kuma sa ma Deeyana albarka, sun dan dade a fada sannan suka fito yanzu ma ha

ka akai doki daya suka hau part d'in gimbiya mabaruka suka nufa.

Gimbiya mabaruka tun da taji zuwan su ta fito dan ta tare su, suna saukowa a doki tazo ta rungume Deeyana da fara'ar ta shiga suka ta zaunar da su a Parlour ta nasiha ta fara musu mai

ratsa jiki sannan ta sanya musu albarka sai da suka tashi zasu tafi sannan ta bude hular alkebban da ta dan rufe mata fuska tace, "bari in ga jikar taw... "

Bata karasa ba ganin Deeyana da tayi gimbiya mabaruka tayi shuru ta sai kallon Deeyana take

kuma kallon ta Dameer yayi ganin kallon yak'i karai wa sai kawai ya kama hannun Deeyana suka fita a dak'in,a zuciyar shi yana cewa lallai akwai wani boyayan sirri tunda gashi ita ma gimbiya mabaruka taga Deeyana ta kasa magana.

Haka suka kara hawa dok

in akai ta zagaya dasu masarautar suna gaida da mutane, part d'in gimbiya Haleematun-Sa'adiya yanzu suka nufa, duk da bata jin karfin jikin ta hakan be hana ta zuwa tarbar su ba tunda haka ake in dai za'a zo gaishe ka to sai ka fito kayi tarba ita da jakad

iya suna tsaya har su Dameer suka karaso doki guda taga Deeyana da Dameer haushi ya kara kamata jakadiya ta tafo ta tace,

"Uwar gijiyata kalle abun mamaki yanzu yarima ko kunya baya ji" cizan bakin ta tayi sannan tace, "jakadiya wannan yaron in ban

yi da gaske ba bakin cikin shi zai kashe ni barshi kawai nasan maganin shi".

Sankowa Dameer yayi a dokin sannan ya kama Deeyana ta sauko rungume ta yayi a jikin shi ya fara cewa, "sannu kiyi hakuri dan wannan tafiyan ya zama dole ne amma da baza kiy

i ta ba sabida nasan ba dadin ta kike ji ba".

Kallon mamaki Deeyana tayi mai tana xancen zuci, gimbiya Haleematun-Sa'adiya ta zuke fuska sannan matso kusa da su tace, "to mara kunya dan yanzu sunan ka kenan a gurina sai ka sake ta ko" "la Momma baza

ta iya tafiya da kanta bane shiyasa" yayi maganar kaman zaiyi kuka.

Hmmmmm kawai gimbiya Haleematun-Sa'adiya tace, da karfi sannan ta janye Deeyana suka shiga kilisarta, murmushi yayi sannan yabi bayan su magana gimbiya Haleematun-Sa'adiya ta fara

ma Deeyana sannan tace, "ki dauke ni kaman mahaifiya duk wani abu da Dameer ya miki ki gaya min kinji"

Kai Deeyana ta daga a hankali jakadiya ce ta shigo da kayan motsa baki sannan ta aje tsakiyan su tace, "to sarauniya gashi a dan tab'a" "ummmm"

kawai Deeyana tace murmushi gimbiya Haleematun-Sa'adiya tayi sannan tace, "my daughter cire hular ki sha iska"

Murmushi Deeyana tayi sannan ta cire shi dai Dameer na zaune na danna waya abun shi, gimbiya Haleematun-Sa'adiya na kallon Deeyana gaban ta

ya fad'i fuskar yarima ALIYU ne kawai ya fadu mata k'ara kallon Deeyana tayi a karu na biyu nan da nan zufa ya rufe ta jakadiya da taga gaba daya uwar gijiyata ta burkice sai take mata mgn da ido akan menene.

Kallon in da take kallo jakadiya tayi da

sauri ta zaro ido dan kaman Deeyana da yan masarautar ya baci, kusan minti goma suna zaune haka can dai Dameer ya tashi yace, "Momma na zamu huce" bakin ta na rawa tace, "to Dameer" kallon ta yayi sannan ya kama Deeyana suka fita.

Jakadiya ce ta mat

so kusa da gimbiya Haleematun-Sa'adiya tace, "uwar gijiyata mai zamu gani kin ga abun da na gani kuwa lallai ba shakka wannan yariyar jinin masarautar mure ne sabida su jinin su baya boya".

Zufa gimbiya Haleematun-Sa'adiya ta share sannan tace, "na

shiga uku ni Haleematun-Sa'adiya mai yasa duk abun da zanyi baya tafiya min dai-dai wannan yariyar jinin waye kenan a cikin masarautar nan na had'a ruwan dafa kaina".

"Aliyu" shine abun da kawai wata murya tace.....

*

๐Ÿค”๐Ÿค”

to fa wacece wannan

kuma*

*Aunty baby ce

โœ

*

[1/6, 10:37 PM] Mum Irfaan

๐Ÿคฑ๐Ÿป

:

๐Ÿฆš๐Ÿฆš๐Ÿฆš๐Ÿฆš๐Ÿฆš๐Ÿฆš๐Ÿฆš

๐Ÿฆš๐Ÿฆš๐Ÿฆš๐Ÿฆš๐Ÿฆš

๐Ÿฆš๐Ÿฆš๐Ÿฆš

๐Ÿฆš๐Ÿฆš

๐Ÿฆš

๐Ÿคด๐Ÿป

*IZZAR SARAUTA*

๐Ÿคด

๐ŸŒ

*_ALHERI WRITER'S*

*ASSOCIATION_*

โœ

*~[ Alheri danko ne, duk inda kayi shi zai dawo gare ka, bur

in mu mu ribantu da alherin da ke cikin wannan harka]~*

*ALHERI SAI DAN AlHERI*

๐Ÿ‘Œ

*Story*

*&*

*written*

*By*

*Aunty baby*

โœ

*DEDICATED TO..*

*TO MY SON AREEF*

๐ŸŒท

*Sadaukarwa ga UMAIMA ALIYU*

*BISMILLAHIR RAHMAIR RAHIM*

๐Ÿ“

*page* 4

โƒฃ

3

โƒฃ

โฉ

4

โƒฃ

4

โƒฃ

*___________*

๐Ÿ“–

"Aliyu!! wannan yariya da kike gani jinin Aliyu ce dan kallo daya nayi mata na tabbatar da haka Haleematun-Sa'adiya ya kamata ace yanzu kin girma kin daina duk

wani makirci sabida wallahi gaba nake jiya miki kuma ni bazan tab'a tona miki asiri ba duk sanda Allah ya tona miki shikenan dan rayuwar na abun tsoro ce" gimbiya mabaruka kenan matar sarki Abdallah.

Wani mugun kallo gimbiya Haleematun-Sa'adiya t

a zuba ma gimbiya mabaruka sannan tace, "daman fa ke ba sona kike ba duk cikin masarautar nan shiyasa yanzu zaki zo kina min wasu banzan maganganu to wallahi ina miki kashedi na karshe karki kara shiga hurumin da ba nake ba a cikin masarautar nan karki ga

wai ke matar uban mai-martaba ne hhhhhh ba raga miki zan ba".

Murmushi gimbiya mabaruka tayi sannan tace, Haleematun-Sa'adiya kenan yanzu ko wannan abun da yake shirin faruwa be ishe ki ishara ba yaron da kikai sanadiyar fitar shi a masarautan n

an shi kuma yanzu a rashin sanin ki da muguntar ki kika kara shigo da shi..".

"Dakata! Dakata!! Wallahi in dai ina raye Aliyu bazai tab'a kara shigowa masarautar nan ba" Gimbiya Haleematun-Sa'adiya ta fad'a tana shiga bedroom d'in ta fuuuuuu, Hmmmm

kawai gimbiya mabaruka tace sannan ta fita a dak'in, jakadiya na tsaye sororo ta kasa tafiya! tana shiga bedroom d'in ta ta fara zagaye dak'in tana zantuka.

"Ni gimbiya Haleematun-Sa'adiya zan saka abu a gaba ban cin ma buri na ba wallahi karya ne

" shigowa jakadiya tayi da sauri sannan ta tsugunna gaban ta tace, "kiyi hakuri ya uwar gijiyata Allah ya huci zuciyar ki in dai ina raye baza ki tab'a shiga damuwa ba".

"Huuuuuummm jakadiya wani bala'i ne yake shirin tinkaro ni yanzu y'ar Aliyu t

ana cikin masarautar nan komai na ya gama lalacewa ya zanyi

yanzu?" ta fada tana zauniya a bakin Bed d'in ta dafa kanta tayi dan ji take kaman zai fashe, jakadiya ta gyara zaman ta sannan tace,

"Ummmmm uwar gijiyata sai kace ba ke ba wannan Dan m

atsalar har zata kwance miki kai abu mai sauki" matsowa tayi kusa da gimbiya Haleematun-Sa'adiya ta fara gaya mata magana a hankali sannan ta kare da cewa, "haba uwar gijiyata ai ki daina damuwa wannan shine hanya mafi sauki da zamubi".

Daga kai g

imbiya Haleematun-Sa'adiya tayi sannan tace, "shikenan kuwa jakadiya shiyasa nake sonki wallahi sabida k'wak'walwar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login