Showing 144001 words to 145961 words out of 145961 words

Chapter 49 - ZUCIYA COMPLETE

ba?"

Tace " gun mijina?"

Yace " da kina so kicemin a gun Little zaki kwana?"

Tace " naga

da acan nake kwana?"

Yace "da kenan yanzu ai kayanki zaki tattaro ki dawo bangaren mijinki."

Murmushi tai tace " ni dai kunya nake ji gaskiya."

Yace " kunya ko? To ni bari nazo na daukeki."

Yana kaiwa nan ya kashe wayar.

Dariya tai ta

ce " in zaka iya kenan ba."

Ta koma suka cigaba da hira, batai minti 10 da zama ba suka ji sallamar Ashraf.

Little tai kasa da kanta, shigowa yai ya zauna kusa da Little tare da dagota yace " kanwata ko neman Habib kike ne?"

Dagowa tai da saur

i tace "ni kuma?"

Murmushi yai yace " to ni kike nema?"

Kasa tai da kanta tana murmushi, Ashraf ya harari Nafi yace " malama tashi ko?"

Nafi ta zaro ido ta kalli Mumy da Inna cikin tsananin mamaki, wai keke damun Ashraf? Abinda tafada kenan

a ranta.

Mumy tai murmushi tace " Ashraf bafa inda zataje."

Kallan Mumy yai cikin mamaki.

Mumy tace " Nafisa tana bukatar wani shagalin biki dan a kara shaida auranku, mutane dayawa basu san matarka bace, ita kanta kunya ya hanata sanar da k

awayenta."



Cikin tsantsan mamaki ya kalli Mumy yace " to ai...."

Mumy ta hade rai tace " mun yanke hukunci da mahaifiyarta nan da sati d'aya za'ai ko yar walima ce sannan ta tare."

Haushi ya kama Ashraf yace "har sati?" ya fada yana

kallan Nafi.

B'oyewa tai bayan Little tamai gwalo, haushi ya kamashi ya mike yace " hmm amma da ina tunanin gobe zamuje kauye tare da Inna dan ta nemi yafiyar Datti."

Mumy tace " hakan yayi kyau, inyaso sai Little ta rakaku."

Yace " amma mu bi

yu ma....."

Mumy ta katseshi zan ma Habib magana shima kila zaiso yaje kauyen kaga sai kuje da armashin ku sai ku dauki babbar mota, gashi Afra nan ma xasuyi rakiya."

Haushi ya kama Ashraf yai waje cikin takaici, bangarensa ya nufa ya kalli yan

da ya tsara musu bangarensu yace " har wani sati? Sannan goben ma baza'a barmu mu biyu ba???"

**********

Washegari haka suka shirya suka dauki mota babba, Little, Inna,Nafi, Afra da Amra, Dan Litti Habib da Ashraf suka nufi kauyen su Na

fi.

A hanya Ashraf yai musu siyayya sosai duk da Habib ne ya sashi dan shi gani yake bazai iya kaima Datti komai ba, haka suka isa kauyen

A kauyen su Dan Litti suka fara sauka aka saukeshi mutane sai kallansu sukeyi, sannan suka wuce rigar Datti

.

Sun samu ba kowa a gidan gidan ma a rufe yake nan fa hankalinsu ya tashi sai ga wani yazo wucewa nan ya sanar dasu ai yana gidansu.

Nan suka shiga mota suka gangara, Datti na kwance a karkashin bishiya shi kadai abin duniya duk ya isheshi yan

a ganin mota ma ta tsaya amma ko alamar mikewa baiyi ba, mutane suka zagaye motar, nan fa su Nafi suka fito ba wanda ya ganesu gwarama Inna yayan Datti na ganinta ya ganeta.

Sai da aka musu iso suka zauna a ciki sannan yayan datti ya aika a kirashi.

Ba'a dade ba sai gashi nan, nan yaga inna sai dai maimakon masifa gani sukai ya saki kuka yana ce mata " innar Nafi mun shiga uku na saida ma masu yankan kai Nafi."

Kuka yake sosai wanda saida yasa Nafi ma kuka, Ashrad ya kalleshi yace " baka gane

ni ba baffa?"

Kallansa yai yanasan gano fuskar sai dai ya kasa, Ashraf yai murmushi yace " mijin Nafi ne."

Nan fa aka dau salati, nan Ashraf ya zayyane musu komai, Inna ta nemi yafiya shima datti ya nemi yafiyar ta data Nafi.

Sun dade kafin

daga bisani suce zasu tafi,Datti yace ai auransa nanan da matarsa, jin matsalar data sameshi yasa Ashraf ya ciro kudi masu yawa ya bashi yace ya sai wasu dabobbin, sannan suyi shawara in sunfisan zaman nan to in kuma sunfisan birni sai ya turo a daukosu.

Nan ya musu sha tara ta arziki suka fito, kowa sai sha'awar Nafi yake, nan Hanne ma dataji labari tazo taganta alokacib itakuma 'ya'yantama 2.

Su kadai suka taho dan dan litti yace sai yayi kwana biyu, zai dai dawo lokacin bikinsu da Nafi.

***********

Duk yanda Ashraf yaso su kebe da Nafi abin yaci tura har ranar zagayowar sati, Nafi tayi rabon Iv gida ya cika sai dai Anisa da Umma sukam suna zaune a bangarensu ko fitowa ba sayi.

Nafi da kanta ta sai kusu kayan da zasu sa a c

ikin kudin dake katin da ASHRAF ya bata.

Ta aikama Anisa da umma.

Hall aka kama, ga innarta ta zo itada mahaifinta da hanne, dama ta shirya musu dinkuna.

Su ferry da Little amara kirjin biki kenan sai hidima sukeyi, duk inda Little ta wuce

Habib binta kawai yake da ido, sosai guri ya cika Abdulkadir wanda ke kula da dan siyasan nan shima yazo dan yanzu ya zama babban mutum Ashraf ya bude mai shago babba anan titin Zoo road inda yake saida kayan masarufai yanzo ko motar da yake hawa ka kalla

sai ka kuma kallo, tunda ya iso shikuma ya kyalla ido yaga ferry hankalinsa ya tashi, sosai ta birgeshi.

Anyi shagalin biki sosai mutane kowa ya tayasu murna, sai dai Nafi tunda ta zauna Ashraf ya hanata tashi, ko kiranta Dj yai sai yace a mata uz

uri haushi duk ya isheta datai magana sai yace wai bazai yarda a wahalar mai da baby ba.

Haka aka gama taro aka watse, Little da Ferry sune suka kai Amarya Nafi bangarenta inda Little tai ta mamakin sanda aka canza komai na bangaren.

Duk yanda

Habib yaso suyi magana da Little abin ya faskara, haka suka kai Nafi bayan sun ajiyeta Little ta juya zata tafi Habib yai saurin binta suna fita yace " Little haka zamu dawamma ko magana babu?"

Kallansa tai tace " yaya da wani idon kakeso na kalleka b

ayan mahaifina shine sillar lalacewar rayuwar Dady?"

Habib ya kalleta yace " amma wannan ba ya wuce ba?"

Kai ta girgiza mai tai gaba zata wuce, hannu yasa ya rikota da sauri ta tsaya cak gabanta na faduwa yace " Little bantaba tunanin ina sanku h

aka ba sai bayan faruwar wannan abun."

Juyowa tai ta kalleshi tace " nifa?" tafada hawaye na gangaro mata, tace " nifa da nake sanka tun ina yarinya?"

Wani irin kallo suka shiga yi ma juna.......

Ferry kam da Abdul bansan ya akai ba can na

gansu tare suna hira mamaki ya kamani nace hmmm lalai......

Shikam Ango ana watsewa ya yaye mayafin dake rufe a fuskar Nafi yace " su Amarya am gama gudun?"

Tai kasa dakai wai kunya, dariya yai yace " au abin Amaren gaske zakimin?"

Ta turo

baki tace " ba amaryar bace?"

Yai dariya yace lalai su Amarya bari in kaiki ciki in gwada ingani ko Amarya ce da gaske."

Zatai magana taji ya sureta..........

Washegari da safe taga bangarenta sosai taji dadi sai dai tace ya dawo da Anisa,

ya aminta da shawarar sai dai yace sai dai a gyara mata wani bangaren dake cikin gidan dan kuwa inhar ta zauna dasu gaskiya itace a wahale dan kuwa bazai iya adalci ba zai kuma sanar da ita hakan.

Da zai fita zuwa gun Anisa ne ya zaro takarda ya mi

ka mata yace " uwar gida ga wasiyyar ki."

Yai gaba

Kan kujera ta kwanta a hankali ta bude takardae.

_Zuwa ga sirikata_

_Bansan me zance miki ba, ban kuma san dalilina na yin wasikarnan ba sai dai nasan abu d'aya shine ke rinjayata, dan

Allah ina rokonki da kularmin da wannan yaron nawa, amanace na baki kisoshi saboda Allah bawai dan dukiyarsa ba, ki nunamai kulawar dazaisa yamanta shi marayane, wannan ita kadaice rokon da zan iya miki a rayuwa._

_Ga nawa gudun mawar na auranku, ba

yawa sai dai wannan nine nake daburin baki ba wanda yasan da zamansu sai ni sai ke sai Lawyer na Salim, nagode kwarai._

Murmushi tai sannan tace " Abba zan kula da yaya sosai, zan sadaukar da komai nawa a kansa."

Nanta zaro takardar dake bayan wasiy

yar, takardace ta nuna mallakin wani gida da kuma shago, mamaki ya kamata, da alama kuma gida ne babba sosai hakama shagon.

**************

Bayan shekara d'aya, sauri take sosai tana hada breakfast Ashraf da babynta mace wato Zainab suna zau

ne akan dinning ya daurata a cinyarsa yana bubuga mata kan dinning da cokali wai tai sauri su yunwa sukeji.

Nafi ta taho da sauri rike da plate ta ajiye a gabansa ta sa hannu ta ja kunnensa da karfi yadanyi kara kadan yace " muguntar ta motsa kenan?"

Harararsa tai ta rike kugu tace "Yaya daga nan ina zaka?"

Yace " zama zanyi in huta kadan kafin na fita aiki."

Ta hade fuska tace " dama shigaban Company an bashi damar kin zuwa da wuri?"

Yace " an fara akaina?" ya fada yana murmushi ta

ce " ni kuma fa daga nan ina zani?"

Yace " makaranta zaki."

Ya fada tare da sumbatare Zee, Nafi tai kwafa tace " kai da zaka zauna a gida, mu da zamu fita shine kake min kidan yunwa?"

Ya tabe baku yace " to ya zamuyi Zee ma yunwa takeji."

Ta kalli agoggo ganin lokaci yayi yasa tai daki da gudu ta dauko mayafinta da jakarta ta zo kusa dashi tamai kiss a kunci sannan tama Zee tace "yaya inkun gama wasab naku ka kaita gun Ya nisa."

Ya mata salute yace " yes ma."

Dariya tai sannan t

ai waje.

Motarta ta fada sannan ta kata key tai gaba.

Little ansa ranar auransu da Habib.

Dan Litti kuma Ashraf ya turashi kasar Spain dan yin karatu.



*ALHAMDULILA*

_Nan ne na kawo karshen littafina na zuciya kowa da irin

tasa, darusan dake ciki Allah ya bamu ikon fani dasu, kura kuran da ke ciki Allah ka yafe mana, Ameen suma Ameen._

Godiya ta musamman ga

*Yan Haske Writers Association*

Ina godiya kwarai da duk wani mai kaunar littafin nan, na gode kwarai da k

aunar da kuka nunamai, naji dadi kwarai.

Gaisuwa ga duk 'yan gro din da nake ciki dan yawansu bazai sa na zayyanosu ba sai dai ina mika gaisuwa ta Allah ya barmu tare Ameen....

Masoyana na gode kwarai da kulawarku, da kaunar ku, Allah ya karem

in ku a duk inda kuke.

*ILYSM*

*URX AYUSHER MUHD*

����������������������

[truncated by WhatsApp]

*Juma'at karem*

*#ASHRAFEENAH TEAM*

*one love

💞

*

🤸🏻

‍♀

WHATSAPP NO:

+2349030159301,08165548431

[

truncated by WhatsApp]

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login