Showing 63001 words to 66000 words out of 145961 words
aranta abubuwa da dama tak
e ayanawa, ne zai mata a hotel d'in? Tunowa tai da sanda ya rungumeta da sauri ta girgiza kai alamar a'a, Ashraf kam kallanta kawai yake saura kad'a ya bigi wata mota, da sauri yaja burki sannan ya kalleta yace " badai tunani kikeyi ni? Kamar ni Ashraf zan
yi miki wani abu ba? Banaji kinkai wannan matsayin ko da kuwa iskancin na keyi."
Nafi wanda kalamanta suka b'ata mata rai tace " nima ai bance wani abu zakamin ba, sannan ko wani abun ne ai banaji nakai wannan matsayin."
Kallan mamaki ya mata, sanna
n ya had'e fuska tamau yace " Da alama raini yafara tasiri a tsakanin mu."
Juya kai tai batace komai ba sai d'an kunkuni datai, a zuciye ya fizgi motar, lalai yarinyar nan shi take ma kunkuni? Sun isa Hotel din ya karasa gun parking, kallanta yai sannan
yasa hannu ya fizgota sam baisan da karfi ya jawota ba wanda hakan yasa ta fad'a kirjinsa, a hankali ta d'ago cikin tsoro, ya kalleta yace " me kika ce d'azu?"
D'an karamin bakinta ta turo gaba tace " ni me nace?"
Yai wani murmushi yace " bakima san m
e kika ceba ko rainin hankali? Da alama ma zagina kikai."
Idanu ta zaro cikin mamaki ta d'aga jikinta daga nashi tace " ni? Yaushe? Taya za'ai in zageka koda kuwa naman jikina kake yanka?"
Ya kura mata ido sannan yace " inkinaso in yadda baki zagen ba
to ki fad'amin a ina kikaji zancen za'a tareni a hanyar zuwa office."
Kallan sa tai cikin tsoro, ya matso da fuskarsa kusa da nata yace " what? Bazaki iya fad'a ba?"
Idanu ta kifta sannan ta had'iyi yawu, ya sa idanunsa cikin nata sannan yace "
bazaki iya ba?"
Idanunta tai saurin maidawa kasa saboda wani abu dataji ya taho mata, komawa yai yazauna tare da d'aukan wayarsa yace " kijirani ina zuwa."
Yana kainan yai hanyar fita, batasan sanda tasa hannu ta riko rigarsa ba, yazo fita yaji an ri
keshi, ya juyo ya kalleta sannan ya kalli rigarsa inda ta rike.
Nafi cikin tsoro tace " tsoro nakeyi Yaya."
Idanunsa ya kankance yana kallanta, ta cigaba " Tsoro nake kar na zama silar jawo gaba ko fad'a a tsakanin ku."
Ashraf yai karamai ajiyar
zuciya sannan yace " Nafisa me kika sani? Me kika sani game dani da 'yan uwana? Mutane sun d'auka ganin fara'a a fuskar mutane shi yake nuna suna cikin farinciki sai dai abin sam ba haka yake ba, kowa da kike gani shi kadai yasan wace rayuwa yakeyi a ciki
n zuciyarsa."
Nafi tai shiru kanta na kasa bata kuma sakeshi ba, Ashraf ya sa hannu akan hab'arta ya d'agota yace " Asim ne?"
Kai ta d'aga mai tare da maida kanta kasa, Ashraf yace " sakini inje in dawo lokaci na tafiya."
A hankali ta saki
rigarsa, ya fita.
Kallo ta bishi dashi jikinta duk ya gama sanyi.
Shikam Ashraf sam baiyi mamaki ba dan dama jikinsa ya bashi hakan, ya sani mutane dayawa ba sanshi suke ba a gidan amma kowa na kokarin b'oyewa banda Asim.
Yana shiga ya bada takardun
dayazo badawa sannan ya fito.
Nafi kam abin duniya ya dameta, Ashraf ya bud'e ya shiga, ganin yanda take kallansa yasa ya d'aga mata gira yace " ya akai kuma?"
Nafi ta girgiza kai alamar ba komai sannan ya tada mota sukai gidan lawyer d'in babans
a, nan ya ajiye wannan motar ya d'au tasa ta da sannan sukai gida.
B'angarensa suka nufa, yana gaba tana binsa a baya, sunje wuce wa ta b'angaren su Asim sai gashi.
Ashraf ya saki wani murmushin rainin hankali sannan ya cigaba da tafiya, ba wanda y
ama juna magana har Asim ya gifta Ashraf kad'an.
Yaji Ashraf yace " ASIM"
Ba Asim ba hatta Nafi wanda Asim d'in ke saitin ta ta tsorata da yanda Ashraf ya kirashi, Asim kam tsoro ne karara a fuskarsa, Ashraf ya tako a hankali yazo kusa dashi sannan ya
sa hannu ya dafashi yace " ka tab'aji inda kura ta nemi kama zaki?"
Asim yamai kallan mamaki sai dai bai amsa ba, Ashraf yai murmushi sannan yace " Ita kanta kurar da take tsoron zaki kaga kuwa ta ina ta isa ta kama sarkin dabobbi?"
Ya kara matsowa
kusa dashi sosai yasa bakinsa a saitin kunnensa yace " In har kurar tana neman halaka sarkinta to lalai sai tayi amfani da kwakwakwarta." Ya fad'a tare da nuna tasa kwakwalwar.
Sannan ya cigaba " in har batai amfani da nan ba to lalai ita zata fad'a ciki
n trap d'in datai na kama sarkinta."
Yana kai nan yasa hannu ya bubugamai kafad'a sannan yai gaba.
Nafi kam a tsorace tabi bayan Ashraf.
Shikam Asim anan suka barshi sai dayai kusan minti biyar a tsaye kamar abu kara motsi kafin ya juyo da niyyar
kallan Ashraf sai dai sam baya gun.
Sun isa b'angaren sa, Ashraf ya kalli Nafi yace " D'akina nakeso ki gyaramin."
Ta kalli falon wanda duk yayi kaca kaca ko sanda yake shi kadai baya taba yanda falonsa yai haka bare yanzu.
Ta kalleshi tace " ni
fa d'akinka kawai zan gyara."
Yace "Falon fa?"
Tace " Wannan kuma matarka sai tayi ai aikinta ne ba nawa ba."
Matsowa ya farayi ita kuma tana matsawa baya, tsoro takeyi sai dai itakam bazata taba yadda ta gyara musu falo ba wato ta gyara suzo su
zauna suyi soyayyarsu a ciki?
Jin tazo jikin bango yasa ta tsaya tare da kallansa a tsorace, Ashraf ya kalleta sannan yace " Maimaita kalamanki."
Kasa tai da kanta ba tare data maida ba, ya saki wani murmushi yace " in aka tambayi iyayenki matsayina a
gunki me zasuce? Ahh i am really curious."
Zaro ido tai cikin mamaki tace " ban gane ba."
Yace " Menene matsayina a gunki?"
Gabanta ne ya fad'i da sauri tace " Yayana mana."
Yace " Good."
Menene matsayinmu a gun iyayena da 'yan uwana?
Tace " W
anda ya taimakeni."
Yace " Bravo!, to menene kuma matsayina a gun 'yan kauyenku da mahaifinki?"
Baki ta shiga motsawa tana san magana sai dai bazata iya fad'a ba.
Ya juya ya fara tafiya sannan yace " in kina san 'yancinki kimin biyayya sai in baki t
akardarki cikin sa lama ki auri wanda ranki yakeso."
Cikin takaici tace " in naki fa?"
Yace " Well! Wannan kuma ya rage naki kinsan dai ba'a aure kan aure ko? Haka nan zakiyi ta zama har ila masha Allah."
Yana kainan yai hanyar dinning.
Tabishi da
kallan takaici, ba ma zaka zauna dani ba sai dai haka zan ta zama har ila masha Allahu, lalai ma Ya Ashraf.....
Cikin takaici ta shiga gyaran gida ranta inyayi dubu to fa ya b'aci, takaici duk ya turnuketa, ko inama wannan matar tasa taje? tai maganar
ranta a b'ace.
Hotunsu ta kalla dake manne a falo sunyi masifar kyau kamar me, taja tsaki sannan tace " Aikin kawai ko kyau ma."
Lol nikam ai dariya ce ta kamani na kara kallan hoton wanda yaune rana ta farko danaji an kushe wannan hoton.....Su Nafi
ko me yasa akaga munin hoton da ni kaina na bash A1?????
*THE INNOCENT TEAM*[7/4, 11:51 PM] YAYA HAYAT: *ZUCIYA*
Kowa da irin tasa
©Ayusher Mohd.....
38
Tsayawa yai cak cikin tsananin mamakin Nafi yarinyar da a iya saninsa sanda
ya d'aukota ko dukanta zakai bazatai magana ba illa ma inka gama ta b'uya a wani gun tai kukanta yau kuma itace........
Katsemai tunani Anisa tai da zanzaro ashar, tace " Lalai yau za'ayi kan babban b*********, ni kika rikema hannu?"
Nafi ta sake mata
hannunta batare da ta tanka mata ba sai neman giftata datai zata wuce.
Cikin zafin rai Anisa tasa hannu iya karfinta ta hankad'a Nafi, saura kiris ta kifa taji an tareta tare da rungumeta, nan suka karasa kasa su biyu, basai ta tambaya ba tasan waye ko
ince zuciyarta ta isar da sakon waye zuwaga gab'obinta.
Aneesa mamaki ya kamata ta saki baki dalala tana kallan wannan al'amarin shikam Ashraf suna karasa faduwa, ya mike tare da sake Nafi sannan ya kalli Aneesa cikin fad'a yace " kinada hankali kuwa
? Yanda kika hankad'ota inta fad'a kan wani abu fa??"
Aneesa kam cikin mamakin kalamansa tace " Ya Ashraf kana nufin tare mata kai ko me?"
Ya kalli Nafi cikin b'acin rai yace " wa zan tare wa? Ina miki fad'a akan zakiyi b'arna wata rana in har baki
kula da abinda kikeyi ba kina min wani zancen banza."
Aneesa tace " Naji na d'au laifina amma inaso inji me yasa ka tareta kai ka fad'i ita kuma ta fad'i a jikinka?"
Kansa ya shafa da hannu cikin takaici ya kalli Nafi yace " malama kama hanya ki f
ita, sannan in sakeji kin raina na gaba dake wlh inbakiyi wasa ba sai jikinki ya gaya miki."
Nafi kalamansa sunsa gwiwarta tai sanyi ranta kuma ya sosu sai dai ya ta iya? Mikewa tai jiki a sanyeye tai waje.
Tana fita Ashraf ya kalli Aneesa cikin tak
aici yace " ke bakiji kunya ba??yarinya karama ita take nusar dake nan d'akin aurenki ne ba wai na wani ba? Akan me zatama gyara miki gun da yazamar miki dolenki?"
Aneesa wacce idanunta suka ciciko tace " Yaya nikam inaji a jikina kamar ba auren soya
yya mukai ba, kamar ni kad'ai ce nake sanka kai kuma sanda kakemin kawai na 'yan uwan taka ne."
Idanu ya runtse sannan ya kalleta yace " a soyayyar danasan ina miki da, banaji yanzu ina miki ko rabinta sannan bana tsamannin zaki tambayeni dalili ganin
ke kikafi kowa sannin abinda ya jawo hakan."
Yana kai nan ya zari makullin mota yai waje.
Aneesa ta fashe da wani irin kuka na bakin ciki itama ta fito tai b'angaren Ummanta tana kuka wiwi kamar wacce akama duka.
*************
A b'angar
en Asim kuwa yana ganin su Ashraf sun tafi yai b'angaren mahaifinsa cikin tsananin tsoro da firgicin kalaman Ashraf.
Yana isa ya kwankwasa tare da murd'a kofar ba tare da ya jira an bashi izini ba.
Kawu wanda ke zaune gaban wani karamin akwati (kit
) yana duba wasu takardu yanajin motsin mutum yai saurin rufe takardun tare da maidashi cikin kit d'in, yana kokarin tura kit d'in karkashin gado Asim ya fad'o d'akin tare da kallan mahaifin nasa.
Shikam Kawu da sauri ya karasa turawa sannan ya had'e rai
tare da cewa " Kai Asim bakada hankali ne zaka fad'omin d'aki ba sallama?"
Asim ya karaso kusa da mahaifinsa tare da tsugunawa a gabansa yace " Abba ya zanyi?"
Cikin mamaki yake kallansa yace " Da me fa?"
Asim ya share zufa nan ya sanar dashi duk
abinda ya faru sai dai ba fad'amai da sanin Umma a harkar ba.
Kawu ya kalleshi cikin b'acin rai sannan yasa kafa iya karfinsa ya ture Asim, ya cigaba da magana cikin fad'a, Asim me yasa ne sam bakada hakuri? Banine nace kabar komai a hannuna ba?"
Asim ya rusunnar dakai yace " Abba kayi hakuri wlh ni sam banasan ganin yaron ne."
Tsaki kawu yaja sannan yace " zancen banza ma kakeyi, yanzu idan wad'anda ka tura sun kama Ashraf kenan 'yan sanda suka zo fa?"
Kana tunanin bazasu sanar dasu kaika ai
kosu ba? Daganan sai me? Kamaka zasuyi a banza."
Asim yai kasa dakai cikin dana sanin gaggawar daya aikata, kawu yacigaba " ni nace kabar komai a guna, akan me zamu halakar dashi bayan bamu gama sannin iya dukiyar dake karkashin sa ba?"
Asim ya jin
jina ma mahaifinsa kai sannan ya bashi hakuri, nan kawu ya sallameshi tare da zama akan gadonsa yai shiru yana tunani, can cikin wata irin murya yace.
" Yaya ya zakayi??? D'an da kakeji duk duniya baya shi gashi a tafin hanuna, ya auri 'yata sannan ma
tar fa kake santa kamar ranka ta dawo karkashina." Wata irin dariya ya saki wanda ni kaina saida tsoro ya kamani, da sauri nabar d'akin ina mamakin dama haka mutumin nan yake??? Lalai wata zuciyar akwai hassada da mugunta a cikinta.
Asim na fita yai
murmushin farin ciki tare da kara kallan kofar d'akin yace " Kai!!!! Amma Abba karshen mugu ne."
Ya sa dariya sannan yace " ko menene a akwatin nan???"
Kad'a kai yai ya nufi b'an garen Umma, ya shiga kenan ya zauna yana jiran ta fito daga b'andaki sai
ga Aneesa ta shigo da kuka.
Cikin kulawa ya mike ya rungumota yana tambayarta menene? Aneesa kam kuka take sosai, nan Umma ta fito ta samesu a haka.
Itama zama tai suka cigaba da tambayar Aneesa abinda ya sata kuka, Aneesa cikin kuka tace " Umma Ba A
shraf bane ya fifita yarinyar nan a kaina."
Cikin rashin fahimta Umma tace " Ban gane ba?"
Asim yace " Malama dalla daina mana kuka ki fad'a mana menene ke faruwa."
Hawayenta ta share ta shiga sanar da su duk abinda ya faru tun daga farko har kars
he."
Umma ta mike cikin fad'a tace " Lalai za'ayi tashin hankali a gidan nan."
Asim ya mike tare da cewa " akwai meeting dole ne yau ayi taron gaggawa na gida dan kuwa Ashraf yayi kadan ya wulakanta mana ke."
A zuciye yai waje......
***********
******
Nafi kam tana fita daga b'angaren Ashraf ta nufi nasu b'angaren taje shiga taji ance " Yaya Feena."
Juyowa tai tare da kirkiro fara'a tace " My Amrah kece da kanki?"
Amrah tai murmushi tace " yaushe kuka dawo?"
Nafi tad'an jujuya kai s
annan tace " ni kadai na dawo."
Amrah tad'an yi hucci kad'an kamar babba, Nafi tai dariya tace " Yaya Amrah ya akai ne?"
Tace " Mumy ce tace " in mun dawo daga makaranta muzo gun yaya Little ta mana wanka sannan ta d'auko mana kaya."
Nafi ta d'an ca
nza fuska kad'an tace "Amrah naji haushi fa! Wato ni bazan iya muku abinda Little zata muku ba ko me?"
Amrah ta matso kusa da ita tace " Yahkuri Yaya Feenah wlh ba haka nake nufi ba."
Nafi ta kama hannunta sannan tace " naji muje mu taho da Afrah."
Nan suka fara tafiya hannayensu rike da juna.
***************
A can kauye kuwa Datti yana cikin tsananin farin ciki da walwala, a 'yan shekarun nan dabobbinsa sun kara bunkasa sosai yazamo kaf kauyen garin ba wanda ya kaishi yawan dabobbi, shi
kadai yake rayuwarsa cikin farin ciki ba wanda zai kashema kud'i bare har arzikinsa ya ragu.
Sam bai damu da halin da Nafi take ciki ba bare kuma matarsa da d'ansa da suka gudu.
Duk sanda aka tambayeshi gidan Nafi sai yace sai dai a tambayi Dan L
itti dan kuwa shi bazai iya gane wa ba, hakan yasa duk 'yan garin sun d'auka da gaske yaje gidan 'yar tasa.
Sanda Dan Litti yai wata 5 a garin kachako yad'an tara kud'insa ya shiga garin kano neman Ashaf sai dai duk yanda ya nemesu ya kasa samunsu kasan
cewar garin da girma sannan baisan wani kwatance ba sai Ashaf mijin Nafi, wannan yasa duk inda ya tambaya sai dai amai dariya gani suke kamar shirme yake ko kansa ne ya tab'u.
Bayan kud'in hannunsa sun karene ya koma garin kachako ya cigaba da achabar
sa har ya d'an samu wasu kud'i, ya sanar da uban gidansa akan zaije kauyensu ya dawo.
Mamaki ne ya kamashi ganin kowa ya ganshi sai ya tambayeshi wai 'yar gidab Datti a wani irin gida akai kaita? Wasu ma cewa suke zasuzo ya kaisu.
Datti yanajin l
abarin D'an litti ya dawo ya taho takanas ya tareshi suka keb'e, Datti ya kalleshi yace " ya kaje gidan?"
Dan Litti ya girgiza kai alamar a'a, Datti yace " ka taimaken duk wanda ya tambayeka gidan Nafi kace musu munje ka taimaka min."
Mamaki ya kama d
'an Litti yace " What u say?"
Datti yai tsaki yace " malam ni banasan wannan yaren arnan naka kamin hausa."
D'an Litti yai saurin rufe baki dan yace ya daina turancin shima.
Nan Datti ya lalaba Dan Litti akan yai karya wai sunje gidan Nafi.
Shikam
d'an litti ko sati baiyi ba ya koma garin kachako ya cigaba da kasuwancinsa, ganin yayi abokai acan ga uban gidansa na sansa sannan can yafi kawo masa kud'i.
Wannan Kenan....
To be continue ......
*THE INNOCENT TEAM*
( _Dan Allah k
uyi hakurin jina dakukai shiru wlh Wayatace tad'an same matsala sai do akai resetting d'in d'inta Tukunna.....Thanks 4 ur Love._ )
[7/5, 6:20 AM] YAYA HAYAT: *ZUCIYA*
_Kowa da irin tasa_
*Na Ayusher Muhd*
39
Nafi ta shiryasu tsaf sun
zauna a falo sunata hirar su, labarin makaranta kawai suke bata itakam kai kawai take d'agawa amma sam hankalinta ba'a gunsu yake ba, abubuwan da suka faru a d'akine suke dawo mata.
Ta zarfafa cikin tunani sam bataji shigowar Little ba, sai jitai an
dafa ta, ta d'an xabura kad'an sannan tace " Amrah me kika ce?"
Little ta zagayo ta gabanta tare da harararta tace " Feenah wato baki mayi tunani na ba ko?"
Nafi ta kalleta