Showing 15001 words to 18000 words out of 69481 words
kulleta takice kawai a bude har gidansa naje yace bashida lkcna Kira kuwa nayi masa yafi dari yaqi dagawa don Allah ki kirashi qila ke a dace ya saurareki" shiru ta
yi ayyana ta inda zata fara kiransa katseta Muhseen yayi da cewa hakan zaki daure ki kirashi Rafi'ah Shirin barin qasar yakeyi idan muka sake yabar qasarnan baa daidaita komai ba tofa auren Bestienki ya hau gorar wahala tsakiyar teku domin ni nasan waye Ja
'afar fiye da tunaninki wlh akan biyan buqatarsa baya duba alaqa kota kwabo Kuma bashida kirki indai akan ra'ayinnsa ne zai iya batawa kowa rai"
Jinjina Kai tayi cikin qoqarin aro juriya tace “sh...shikenan zan kirashi" kashe wayar tayi ta lalubo
numbersa gabanta na duka ta latsa har tayi Ring ta katse bai dagaba ta
sake Kira shima bai dagaba saida ta kirashi sau goma bai dagaba ta rubuta Masa gajeran saqo tace _“please Mr Ja'afar Wakil ka daga don girman Allah"_ cikin seconds saqonsa ya shigo kama
r haka.
_"Gobe 7:30 zan wucce Indonesia banida lkcn daga wayarki idan kinason mgn dani dake kece zan iya baki 30 minutes cikin lkcna kizo gidana ki sameni yanzu ba dazuba ba anjima ba"_ zaro ido tayi waje tanajin wani tafasasshen gumi na karyo Mata bata g
amajin zagayar kalamansa ba Ni'imah ta kirata ta daga ta fashe da kuka tace “Bestie yaqi daga wayata wai saidai naje gida na sameshi nikuma bazan iya zuwaba" wani kuka Ni'imah ta rushe dashi tace “kada kiyimin haka Rafi'ah ki taimaki igiyar aurena wlh Ja'a
far ba dan iska bane bazaiyi Miki komai ba kije kijimin meye laifina ki bashi hqr da yawuna idan yabar qasarnan zan dade banganshi ba kije Rafi'ah please kije"...........
_Vote_
_Comments_
_Share_
_Please_
*_Oum Hairan_*
[1/3, 9:1
7 PM] Mrs AA Fansah: *_My Bestie's Husband_*
*_Ummuh Hairan_*
*_Wattpad-realfauzahtasiu_*
*_11-12_*
_____________________________
_____________________________
Girgiza Kai Rafi'ah tayi tace “Aa Ni'imah mijinki
azzalumine bashida adalci baison me sonsa ba meyesa laifin wani zai shafi wani...." Katseta tayi tace “naji Rafi'ah nidai ki taimakeni kije don darajar qauna da aminta kinji" ajiyar zuciya tayi jikinta ya qara sanyi tace “shikenan zanyi qoqari bari zance d
a Ammi zanzo gurinki asibiti duk yanda mukayi zakiji" ajiye wayar tayi ta fara kaiwa da komowa a dakin zuciyarta cunkushe da tsoro yanzu ita ya zaayi ta taka taje gidan Ja'afar Wakil da wanne irin yanayi zai karbeta?
Tambayar da takeyiwa kanta ta kasa sam
un amsa kenan daqyar ta iya sawa kanta juriya ta dauki doguwar rigarta ta zura tayi rolling mayafin ta dauki takalmi da wayarta da key din motar Ammi ta fice daga dakin ta nufi dakin ammi tana bisa sallaya ta zauna bayan ta idar da sallar ta dubi yar tata
tace “ina zaki?" Sunkuyar dakai tayi qarya ba dabi'arta bace shiyasa takejin nauyin yinta to yanzun dai dole ta kamata tace “zanje wajen Bestie ta kirani tanason ganina urgent don Allah kada kice aa Ammi" murmushi ammi tayi tace “toni na Isa na hanaki kid
ai kula da kanki don Allah Kuma ki Kama bakinki tsakanin Mata da miji sai Allah akansa sai taji haushinki"
Jinjina Kai tayi cikin jin dadin sa'ar da Allah ya bata ta fito ta dauki motar ta fice Kai tsaye unguwar da martaba estate take ta nufa Sai
da taje daidai get din tayi parking ta dauki wayarta ta kirashi bai dagaba saboda yaga tsayawar matar koma yaji a jikinsa itane hakan yasashi turo mata da number gidan tayi horn security din ya bude Mata ta shiga tabi titi na biyu tayi parking daidai block
29 ta sake kiransa ya bai dagaba sai megadi da taga ya bude Mata ta shiga tayi Parking ta sake kiransa sai taga wani mutum ya fito sanye da rigar kitchen da alamun kuku ne yazo ya qwanqwasa Mata glass din ta zuge ya gaisheta tare da cewa “yallabai yace a
shigar dake" Saida gabanta ya fadi tayi kamar tace aa saidai tasawa kanta juriya ta fito ta kulle motar tabi bayansa suka shiga ya mayar da qofar ya kulle taja ta tsaya a parlourn qasan tana qarewa gdan kallo manyan hotunansu ita da Ni'imah da sukayi kafin
bikin sun qarawa parlourn kyau kowanne an rubuta world Bestie's tayi murmushi tana me maida hankalinta ga kallon hotunan.
Ji tayi an zagaye weast dinta da hannu anyi kissing dogon wuyanta tare da shaqar qamshinta tayi saurin janyewa lkcn da yake sauke a
jiyar zuciya tace “kace inzo zaka bani lkc ka saurareni na roqeka da girman Allah kada ka qara tabani J Wakil ko bance maka komai ba Allah zai sakamin domin Kaine namiji na farko da kataba hada jiki dani"
Lumshe idonsa yayi ya bude yace “gdannan
ya dace dake My Bestie dama ace kin shigo kenan" kalmarsa taso bata dariya ta dai dake ta maze tace “meye dalilinka na tozartamin Bestie na bayan ka cire Mata darajarta Kuma kake burin mayar da ita qaramar bazawara?" Takowa ya farayi gabanta tanaja da baya
yana sake binta saura qirin takai qofar yayi maza ya shammaceta ya danna Mata key taja numfashi tare da
zuba masa ido jikinta na rawa sai hawaye sharr tayi saurin zamewa ta zube aqasa shima ya zauna yakai hannu zai riqo nata ta janye yace.
“Kina tsoronan
e? Meye kike tsoro game da mijinki mijinki ba fasiqi bane Kuma ko Ina fasiqanci bazanyi dake ba kinada matsayin da sunnah ce ta dace dake ba zina ba Rafi'ah ki amince da buqatata wlh cikin wata daya zaayi komai a gama ke ni idanma wata dayan tayi Miki nisa
zan iya ko gobe a daura mana aure saina daukeki mu tafi Indonesia bazamu dawoba Saida bebynmu Kinga lkcn kowa yayi surutunsa ya gama saimu fara sabuwar rayuwa ko?"
Gabadaya kallon mahaukaci takeyiwa Ja'afar Wakil bata bashi amsa ba taja fasali
tace “bestie ce tasani zuwa gunka ba zuwan kaina bane tace nabaka hqr Kuma ka fadamin laifinta munyi maka alqawarin gyarawa da qarfin buwayar zatin ubangiji...." Hannunsa ya aza ya dago habarta ya zuba idanunsa cikin nata tayi saurin lumshe nata yayi murm
ushi yasan duk taurin kan mace indai zata kalli qwayar idonsa saita rusuna yace.
“Naqasunta baya damuna domin nasan dama wacece ita ba wata bace sai yar gidan Hajiya Sahura qawar Hajiya Fatsum Iko mahaifiyata iyayen da basa kwabar yayansu musamman Mata sa
nnan basa basu horon zama da miji sukw dauka cewa izza da iko zasu siyi zuciyar miji nop duk ba wannan ne damuwata ba damuwata shine ki amince dani ki karbi soyayyata idan kin amince wlh na amince zan dawo da qawarki gdannan a daren nan zata zauna albarkac
inki Kuma zan wanzar da adalci tsakaninku sannan zanyi hqr da duk wani lapse nata nayita mernege har zuwa lkcn da zan shigo dake matsayin Mata ranar da zanyi asalin angwanci zan huta iyakar hutawa ranar da Prince Ja'afar zai kwana yana wanzar da qauna me y
ado a zuciya a gurin daya dace"
Harara ta maka Masa tare da miqewa tace “idan Kuma ban amince bafa?" Murmushinsa na Isa yayi ya miqe ya zare doguwar rigarsa idanunta ya sauka a faffadan qirjinsa me yalwataccen gashj tayi saurin dauke idonta shikam bai dam
u ba ya dauki wandonsa na yadi yasa ya dauki rigar ya sanya yasa hula ya matso gabanta yanata zuba qamshi yace “kofa baki amince ba kin amince Rafi'ah dolene ki aureni domin nasani kowama yasani ni dake mun dace sosai"
Dagowa tayi tace “ban amince
ba Amma zaka dawo da Bestie na Ja'afar inada Wanda nakeso wlh harma munyi alqawarin aure nifa bantaba sonka ba hasalima wlh natsani namiji irinka mara sanin darajar alaqa Ja'afar Wakil please kada kaja alaqar nan har kayi yanda duniya zata fahimta Allah y
asani bazan taba iya wannan cin amanar qaunarba bestie ta aminta dani ta dauki amanar kanta da duk wani sirrinta tabani munyiwa kanmu alqawarin rayuwa tare mutuwa tare Amma kana neman kawo mana tasgaro cikin tafiyarmu munyiwa junanmu alqawarin hada yayanmu
aure idan Allah yaja rayuwarmu Ja'afar kada ka zama makamin yanke kyakkyawar alaqarnan kaji?"
Ta qarashe mgnr tana durqushewa a gabansa inda idanunsa yake kanta yace “kinason farin cikinta?" Saurin daga masa Kai tayi ya sake cewa “meyesa kika yarda kizo
gdana saboda ita?" Sunkuyar dakai tayi yace “talk mana" dagowa tayi idonta cike da qwallah tace “saboda inason ta dawwama cikin farin ciki tare da abinda
takeso" murmushi yayi yace “to ita meyesa bazatayi Miki wannan sallamawar ba?" Dagowa tayi suka hada
ido ya qanqance qananun idanunsa ya nunata da yatsa yace “duk da cewar zuciyarki taqi gasqata Miki cewar kinasona Amma ni inaji a jikina jikinki da ruhinki sun karbeni Ni'imah itace qaddarar da take wahalar damu babu wani abu naki da yake boyayye a gurina
kinason namiji me irin siffata to kin samu nine Rafi'ah nine Ja'afar Wakil ki karbeni kawai a wucce gurin babu wanda ya usa canza qaddarar Allah fah dagani harke babu abinda muka isa mu canza dole mu karbi duk hukuncin da ubangiji yayi akanmu"
N
umfashi ya sauke yace “kada ki damu muje a daren nan zanyi Miki abinda kikeso bazaki kwana da ciwon mutuwar auren Bestienki ba Amma kisani a gobe zan sanar da manyana halin da ake ciki dama rashin samun dama daga gareki ya hanani furta musu koma...." Wata
tsawa ta daka mishi data sanya gabanss faduwa tace “karka kuskura kada ka fara wlh bazan taba yarda da wannan haukan ba kuma ma Ina katabajin anyi wannan sakarcin to nidai bada yawuna ba idan kuwa ka sanar Kaine da kunya na rantse da Allah saina kashe kai
na na huta kowama ya hut...."
Wata fizga yayi Mata ya hadata da jikinsa ya matse yana lalubar bakinta ta fara tureshi ya sake daidaita qirjinta a nasa yanajin yanda dukiyar qirjinta take gugar nasa qirjin, jin yanda electric din jikinsa suke wani touching
yasashi saurin sakinta ya zauna a hannun kujera yana cakuda numfashi inda itama tayi baya da sauri tanajin wani shorck a cikinta da bata tabajiba daqyar ta daidaita nutsuwarta yana kallonta yanajin wani sabon baqon yanayi miqewa yayi da sauri yana korar
shaidan da a'uziyyah ya dauki key din motarsa yace “muje ko?" Babu musu tabishi tana fita ta fada tata motar baiso hakan ba amma Babu yanda ya iya da ita haka ya shiga taja suka fice jikinta har yanzu wani yammmm yakeyi Mata tanajin wani yanayi da bata tab
ajiba, gidansu Ni'imah suka nufa Kai tsaye suka shiga tayi parking ta fita ta shiga gdan shikam baima fito a motar ba tana shiga Hajiya Sahura ta washe mata baki tace “da daren nan Rafi'ah lfy" numfashi taja tayi qasa ta gaisar da Mama tace “bestie fah M
ama" sama ta nuna Mata tace tanacan tanata aikin kuka kamar kanta ka fara yo bandama abinta mijin da ya sakeki har yana fads Miki Wai sabodakene burinsa bazai cikaba meye na damuwa basai ta qyaleshi ya cika burin ba mugani"
Itadai miqewa tayi tace
“tare muke dashi yana waje yace ta fito su tafi ya wucce" miqewa Mama tayi tace “tabdi Amma yakai riqaqqen dan iska bama zai shigo ba...." Kafin ta rufe bakinta sai gashinan ya shigo sai Kuma tayi shiru harda washe masa baki suka gaisa Dad taje ta Kira a
sama yazo suka zauna Rafi'ah ta Kira Ni'imah tana ganinta ta rungumeta tana dariya me hade da kuka tace “da gaske ya mayar dani Bestie wayyoh dadi kema Allah yakaimu ranar da zan saka Miki yana Ina?" Janyo hannunta tayi cike da tausayin qawar tata suka fi
to ya dubeta ya kawar dakai ita kuwa sai wata kwarkwasa takeyi Masa shi Kuma rabin hankalinsa nakan Rafi'ah Dad ne ya lura da satar kallon Rafi'ah da Ja'afar yakeyi inda yayi gyaran murya zai fara mgn tayi saurin daga wayar qarya tana cewa “ok Ammi ganinan
zuwa ki basa hqr" miqewa tayi ta dubi Ni'imah tace “zan wucce Bestie ki kula da kanki don Allah Allah ya kiyaye gaba" zuruf Ja'afar ya miqe yace “bari na rakata ki shirya ki jirani Ina zuwa"
kafin ma wani yayi mgn ya fice suka kalli juna ita da Ni'imah Ni
'imah tayi Mata murmushi tace “na gde Allah yabar qauna kema ki kulamin da kanki"
Har bakin motar ta rakota ta shiga yaja suka fice suna fita ya dubeta yace “amaryata me kikeso" ko kallon tsiya bai samu ba balle na arziqi mgnr duniya taqi tankasa
sai latsa wayarta da takeyi taji yayi parking batare da ya sake mgn ba ya fice taja dogon tsaki tare da cewa “shashasha kawai" Bai wani jima ba ya dawo ya zuba kayan daya siyo a kujerar baya ya sake zama yaja ya nufi hanyar unguwar tasu yana parking ko sal
lama bata tsaya sunyi ba ta fice ta nufi cikin gda yabi bayanta dake jujjuyawa da kallo ya sauke numfashi ya bude ya dauko kayan yabawa megadi ya shiga dashi shikuma ya fice ya samu sahu ya hau ya nufi gidansa ya bawa driver mota yace yaje ya dauko Ni'imah
a gda.
Lkcn da ta shiga ta tarar da Abba suka gaisa yace “ya jikin bestie din" amsawa tayi a gajarce ta haye sama ta cire rigarta da taketa zuba qamshin turaren Mr Ja'afar Wakil ta daura towel ta fada wanka taji an shigo dakin koda ta fito sai taga anti
Murja ds kaya ta dubeta tace “anya wannan mutumin ba maye bane Rafi'ah?" Tabe baki tayi tace “dan wahala ba wlh na tsaneshi" murmushi anti Murja tayi tace “ni bawai shi na tsana ba tashin hankalin da zaayi idan ya fadi qudirinsa nake tsoro" batace komai ba
ta shafamai a lallausar fatarta ta zura rigar bacci ta kwanta bacci me dadi ya dauketa yauma mafarkinta irin dai wanda tasabane sai ta yanzu take fahimtar inda ya dosa watoar wannan mutumin da take yawan gani ba kowace bane Ja'afar Wakil ne.
Da
safe da wurwuri ta tafi makaranta saboda batason damuwa wayarta ma kasheta tayi ta jefata a jaka ranar bata samu zama sai dare ta kunna wayar ta sake sata a silent ta shiga karatu tana ganin kiraye kiraye taqi dagawa sai saqonni sukayita tururuwar shigowa
Suma bata budeba tayi kwanciyarta Saida safe ta duba wasu duk shirmen Ja'afar ne taja tsaki ta qara kashe wayar.
Suna garden suna dan tattaunawa wani abokin karatunsu yazo yace “kinada baqi fah Rafi'ah" dafe qirji tayi tace “waye?" Batare da yabata wani
attention ba yace “naga motarsa ansa JMW" iska ta furzar tace “kacr bakaganni ba kawai" zaro ido yayi yace “tabdi wlh bazan iyaba wannan guy din yana mgn kamar anyi masa dole" harararsa tayi ta tashi ta koma wani bangaren can nesa ta zauna wata flower ta
rufeta taci gaba da karatunta ya akayi ya akayi saiji tayi an qwace littafin ta dago a tsorace.
Numfashi taja tare da miqewa ya zuba Mata ido yace “kina wahalar dani Rafi'ah da wanne zanji ne abubuwa sunyimin yawa fah inason samun sauqi ta bangarenki Amm
a kinqi tausayamin ya zakiyi da haqqina ne meye laifina don nace inasonki ni bada wani abun banza nasoki ba da aure fah Rafi'atuh meye laifin masoyinki?"
Miqewa tayi tana tattare takardunta tace “meye laifina Nima don nace banasonka bakuma zan ta
ba sonka ba nikam bantaba ganin mayen mutum irinka ba ka rabu dani ka fita a rayuwata kaqi bafa ayinso dole to me kake nema danine maci amanar
qauna?" Sosai yaji dacin kalamanta Amma bashida meyi shine ya kawo kansa dole ya jure iyakar wuya watarana sai la
bari.
Murmushi yayi yace “albishir nazo nayi Miki yau naje na samu Dad mahaifin Ni'imah na sanar dashi inasonki da aure yaje ya sami Mai Martaba ya sanar dashi Kuma inason komai ayishi a game cikin one month kamar yanda akayi na aminiyarki saboda haka dag
a yanzu ma zaki iya fara shirye shiryenki Nima zan fara daga yau bansan ra'ayinki ba zaki zauna a gidan sarauta ko Kuma Zaki zauna da bestie dinki"........
_Vote_
_Comments_
_Share_
_Please_
*_Ummuh Hairan_*
[1/4, 10:07 AM] Mrs AA F
ansah: *_My Bestie's Husband_*
*_Ummuh Hairan_*
*_Wattpad-realfauzahtasiu_*
*_13-14_*
_Ina mamakin mutane da basawa rayuwa uzuri, shin Ina tunaninmu yake tafiya da muke manta komai yana gudana ne bisa iko da sahalewar Uban
giji bawai ra'ayinmu da_ _iyawarmu ba? Am sorry to say sisters and brothers mgnr addini babu ra'ayi a cikinta, idan har kunya zata saki kibar halal to shakka babu aure shine Abu na farko daya kamata ki bari saboda babu abinda yafishi rashin_ _kunya a duniy
a Amma Kuma shi Ubangiji da kansa yake cewa_ _(WALLAHU LA YASTAHAYI MINAL HAQ) tabbas Allah bayajin kunyar gaskiya saboda haka mu cire son rai mu tunkari gaskiya komi dacinta da ciwonta, Oum hairan ba son rai take rubutawa ba gaskiya take rubutawa wannan k
aron
🤗
_
___________________________
___________________________
Miqewa tayi tsaye ta zuba masa manyan idanunta masu saukar masa da kasala a mamakance take kallonsa yayi murmushi ya juya yana tafiya yana cewa wani abune zaikaini Indonesia Amm
a dole zan bari sai angama komai na bikinmu saboda bazan ballo ruwa nabarki da tarewa ke kadai ba, tabbas bakida laifi a cikin wannan lamarin amma duniya bazatayi Miki adalci ba hakanne yasa na shirya sanya qafar wando daduk Wanda ya nemi uzzurawa rayuwark
i"
Baijira cewarta ba ya fice daga garden din Nina dake zaune tanajinsu ta taso tace “tabdi nidai bantaba ganin nataccen mutum irin JMW ba shi ko tsoro bayaji baya ko tunanin me zaije yazo?"
Jinjina Kai tayi tace “so yake ya yankemin duk wata walwalar ra
yuwata Nina yacika son kansa da yawa duk wani Abu da zan nusar dashi ya kasa ganewa wai har takai ga yaje ya fadawa Dad mahaifin Ni'ima wannan haukan nasa...." Zaro ido Nina tayi tace “wht? Da