Showing 171001 words to 174000 words out of 363627 words
ko ina daukansu akeyi wasu na jifansu daqyar aka samu wucewa dasu ciki.
Yan media kuwa sai qara yadawa akeyi koina case din na
yade koina.
A daidai wannan lokacin Zaadens na kokarin ganin daidaituwar Dad sai kawai katsam labarin ya bayyanar musu a tv wanda ya sakasa Dad din qarasa rikicewa gabaki daya yana fita hayyacinsa.
Hankali tashe suka kwashesa zuwa asibitin zaadens
wadda akai gaggawar karbansa.
Karban wayar mama Maheer yayi ya kashe sbd bayason taga komai,
Saleem da shima kansa ke neman juyewa da Abinda aketa fada a labarai da kofofin yada labaran kasa fahimtar komai yayi dayaga yana neman rasa hankalinsa shima k
ashe wayoyinsa yayi,
Ammar ma dashi aka taho asibitin duk da kan nasa haryanzu da saura amma ya dawo daidai a yanzu dan haka shima yana samun labarin shida Maheer neman zaucewa da tsananin tashin hankalin da ba damar nunawa sukeyi ga dad a kwance rai ha
nnun Allah ga daddy mahmoud baya duniya ga anny a hannun huguma.
Idanuwansu sunyi wani irin jajir kaman zasu zare kowa yayi shiru babu wanda baya cikin tsananin baqin ciki da damuwa da tashin hankali me tsananin girma a zaadens din.
A daidai wannan
lokacin Jannah na toilet tayo wanka ta fito ta shirya kenan ta zauna tana kunna qatuwar flat screen din dake dakinta hoton Abraham ne da ken suka bayyana da abinda ake zarginsu dashi.
Wata irin mummunan bugawa kirjinta tayi ta gyara zamanta ahankali ta
na ajiye remote tana daukan wayarta ta saka kiran Dad dinta switch off,
Wayar Mimi ta kira itama haka,
Ta saleem ta kira shima kashe,
Ta Maheer ta kira tana silenta bai daukaba,
Wayar Ammar zad ta saka kira wanda koda kiran ya shigo wayar na hannunsa
yana kokarin hada musu tafiya gabaki dayansu zaadens su bar qasar su koma inda suka fito.
Kallan sunata da hotonta daya bayyana akan wayar yayi yana jin bugun zuciyarsa na sauyawa.
Numfashi ya sauke ahankali kafin ya dauka a natse.
Cikin damuwa t
ace
"Lafiya kuke ku dukanku kuwa?
Inata kiran kowa bana samu"
Numfashi ya sauke ahankali tareda bude baki yace
"Muna asibiti ne Dad ba lafiya"
Miqewa tsayi daga zaunen datake zuciyarta na harbawa ba daidaiba tace
"Dad? Meye samesa?
Tin yau
she?
Ina su Mimi?
Meya samu dad din??
Take idanuwanta suka ciko da wasu irin hawaye masu tsananin dumi suna saukowa fuskanta sbd a rayuwarta yanda take tsananin kaunar mahaifinta bata hadasa da komai da kowa ba,
Shine na farko a zuciyarta dayafi kowa
,
Tin tana yarinyarta ta taso da girmama tsananin girman kaunarsa a ranta,
Kaman yanda yafi tsananin kaunarta fiyeda kowa da komai da rayuwarsa haka itama take tsananin kaunarsa fiyeda kowa da koman da kanta din.
Ammar numfashi ya sauke me zafi yana
bude baki zaiyi magana ta datse kiran tana miqewa ta sauya kayan jikinta zuwa doguwar riga ta zari key din motarta ta fice batareda sanin kowaba.
Kasa bude mata kofa securities sukai suka kirasa suna kokarin sanar dashi motarsa ta iso gidan.
Ana bud
e masa gate kafin ma motarsa ta sako kai ta fice gate din da gudu kawai tana barinsa da bin bayan motarta da kallo.
Baice komaiba suka shigo kawai.
Ko data isa kallo daya tayiwa familynta taji jikinta ya mutu da wani irin damuwa da tausayin kansu me
tsanin gaske.
Idanuwan Mimi gabaki daya sun kode sun jeme sbd kuka da damuwa,
Saleem idanuwansa sun fada sosai gabaki daya ko abincin kirki ya dena ci a yanzu,
Maheer duk jajirwa da jarumtarsa ya koma kalar tausayi damuwa da qunci tareda rashin ma
fita da madafa sun sakasa gaba.
Ammar kuwa kai tsaye ya koma rabi lafiya rabi juyewan kai,
Dukkaninsu sun rame kaman ba masu taqama da class da wayewa da arzikiba.
A sanyaye ta iso ta zauna kusa da Mimi tana saka hannunta cikin na saleem daya bude m
ata hannunsa idanuwansa jajir.
Shiru sukai babu me iya cewa komai sai saike ajiyan zuciya da numfashi kawai sukeyi.
Ammar kuwa cigaba yayi da hada musu shirin barin qasar.
Acan asibiti ta wuni sai dare ta dawo gida shima sbd Mama sunzo tareda fa
laq da Fiddausi ne sun duba dad din sai suka koma tare.
Koda suka dawo gidan shigewa tai zuciyarta kwata kwata ba dadi tai wanka daqyar taci abincin da mama ta takura mata taci tai sallolinta ta kwanta.
Kwana tai tana yiwa mahaifinta addua sbd batasa
niba ko zata iya rayuwa idan ta rasa mahaifinta.
Tashin hankalin da zaadens ke ciki na Dad dayake sake nisa ya saka kwata kwata suka aje maganar kama su Abraham da akai kokarin barin qasar sukeyi da dad dinma gabaki dayansu.
Su Abraham kuwa kwana s
ukai ana basu azabar data wuce hankali sbd sun kasa magana hakama har lokacin LIMBA bai fito ya shiga cikin case dinba kaman yanda basu bada evidence gaba daya ba wanda zai nuna zaadens na ciki sbd so yake su fada da bakinsi su waye sukewa aiki.
Washe g
ari Dad ya farfado amma yana cikin matsanancin ciwo har lokacin,
Karfe goma da rabi AZIZ LIMBA ya iso asibitin wadda yayi alkawarin bazata qara sati batareda anrufeta an konataba.
Dukkanin Zaadens na ganinsa zuba masa idanuwa sukai harya qaraso suka
gaisa dashi da sauran girmamawa.
Mimi juyawa tayi ta fice a natse jikinta a sanyaye bayan sun gaisa,
Saleem ma bayanta yabi sbd ganin bata iya tsayuwa daidai.
Ammar da hannuwansa suka fara rawa zuciyarsa na wani irin tsalle da tafasa har cikin kwa
kwalwansa ya kalli AZIZ din ya bude bakinsa dayake zafi kaman zai fidda wutar datake neman kashesa a zuciyarsa yace
"Kanason qarasa shima kaman yanda kayiwa Daddy mahmoud?
Tinda ka shigo rayuwarmu alkhairi ya dena shigowa cikinta,
Meye laifin ko illan
da mukai maka kake bibiyar rayuwarmu kake illata mu???
Dago idanuwa AZIZ yayi Ahankali ya saukesu akan Ammar din suna sauyawa ahankali zuwa ja me bayyanarda tsananin ciwo da daci tareda fushi da tsana me karfin gaske ya bude baki yace
"Kana buqatar
sabon sani ne bayan wanda kake dashi na ni din waye?
Kana buqatan sake sanin fuskan waye akan tawa fuskan?
Kana buqatan sake sanin fuskan da kuka kwantar kuka fedewa kirji kuka zarewa rayuwa dan raya wata rayuwar?"
Wata mummunan faduwa gaban Maheer ya
yi yana kallan Ammar da sauri kafin ya kalli AZIZ din wanda idanuwansa sukai jajir hannuwansa na wata irin rawa.
Dad dayake kwance shima cikin azabar ciwo bude idanuwansa yayi da karfi akan AZIZ numfashinsa na neman sarkewa.
#MAMUH
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
mamuhgee
A DUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo
Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi
Shedan biya
09033181070
Or mtn vtu at
09032345899*_KALBIM_*
_Mamuhgee_
8
4
*UMMU_MAHNOOR LUXURIES*
(Best luxuries shop)
08034469681
08135142610
Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini?
Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitira
r alfarma e kika saka?
Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu?
Sitirar Alfarma kikeson sakawa?
Sitirar da kike ganin manyan mata da ita?
Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota?
To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida,
Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu,
Nidai Mamuh nace duk wadda ke son
a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta
💯💯
Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun ma
ta masu aji yan gayu sune;
Atampopi
Laces
Shadda
Materials
Shoes
Bags
Veils
Trolleys
Jewellerys
Oil perfumes
Numbers
08034469681
08135142610
Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Faceb
ook ummu_mahnoor_luxuries
***********
Maheer ma matsanancin shock dayafi na Dad ya shiga bakinsa na bushewa,
Shi kansa Ammar dayake tinanin hakanne yasan waye AZIZ LIMBA din jin maganar daga bakin AZIZ din sai daya mugun girgizasa ya kallesa da sa
uri idanuwansa na yin jajir harda cikowa da wasu hawaye masu tsananin karfi.
Dad kirjinsa tsananta ciwo yayi idanuwansa sukai jajir ya rintsesu ahankali zafafan hawaye masu tsananin zafi na gangaro masa,
Kallansu AZIZ din yayi da jajayen idanuwansa d
aya bayan daya tsananin ciwon dayake shimfide a zuciyarsa yana tasowa,
Akan Dad da idanuwansa ke tsiyayo hawaye masu tsananin ciwo yayi kafin ya saka hannuwansa biyu ya kamo wuyan rigarsa ya dagosa da karfi ya jijjigasa yace
"Kana hawayene sbd yarka
datake hannun wanda bazai taba yafe abinda kukaiwa tasa 'yar ba?
Wannan radadin dakake ji a zuciyarka ko kadan baiyi zafi da ciwon wanda kuka sakamin ba"
Wurgi dashi a gadon AZIZ yayi yana dawo da kallansa kan Maheer daya isa da sauri ya tare Dad day
a fado gadonsa numfashinsa na neman yankewa sbd zuciyarsa dake neman bugawa da tashin hankali yace
"Jinin Limbas a tsarkake yake baya da tsatsa ko daya,
Bana bata hannuwana da imanina da jinin kowa amma lalata rayuwarku da tabbatarda kun nema kisan kan
ku da kanku shine abinda bazan taba barin qasar ba saiya tabbata,
Ban taba so ko kaunar sadakar da kuka ban ba,
Amma bazan taba dawo muku da itaba saina mayarda ita masu aikin gidana ma sun fita daraja da kyan gani"
Ammar ne yayo kan AZIZ din cikin ts
ananin bacin ran da ko gani bayayi zai miqa hannunsa ya kama wuyansa Wani lafiyayyan marin daya sakasa juyawa gefen Maheer baya gani sosai ya sauka fuskansa daga Sayd wanda yasha gabansa a hankali yana masa kallan tsana me tsananin gaske,
Sake juyowa Am
mar din yayi yana fita hayyacinsa zai sake nufar AZIZ Sayd ya sakar masa wani mahaukacin marin tareda kama hannunsa ya sake sakar masa wani marin idanuwansa ba rufewa shima zuciyarsa na tafasa tako ina jin yake ayau da suka fuskanci juna a matsayin su din
babu boyo kaman zai iya kashe Ammar yakeji sbd radadi da tsana me karfi ce yake dannewa da boyewa tsawon lokaci amma banda yau.
Kasa dena tasowa Ammar yai sbd gabaki daya ya fita hayyacinsa AZIZ yakeson shaqewa ya rabasa da duniya ko zasu samu salamar r
ayuwarsu daya riga ya lalata masu su duka kaf zaadens.
Sayd da shima nasa idanuwan suke a rufe da zuciyarsa duk motsi daya idan Ammar yayi na yunqurin matsowa mugun naushin dayake fasa hancinsa yake sakar masa yana jin zuciyarsa na kasa samun sassaucin
abinda yake ji ko kafan.
Maheer dayake riqe da Dad dake neman rasa ransa hawaye ne masu tsananin radadi da ciwo shima suka gangaro masa ganin yanda hancin Ammar ke fidda jini.
Juyawa AZIZ ya fice sbd shima zuciyarsa gap da sakasa hawayen tsananin ciw
on dayake ransa....
Sayd kuwa saida ya tabbatarda Ammar ya zube qasa yana neman taimako kafin ya juya ya fice daga dakin hawayen d suka cika idanuwansa suna zubowa kan fuskansa ahankali.
Barin asibitin sukai,
Suna ficewa Maheer ya buqaci likitoci su
yi gaggawan zuwa ga dad,
Ammar ma gaggawar ficewa akai dashi daga dakin ana wucewa dashi inda zaa dubasa,
Mimi kallo daya taiwa Ammar ta kusa yanke jiki ta fadi Saleem yayi saurin riqeta yana shiga tsananin mamaki da tsoron meya faru shima,
Jamian
tsaro likitocin zasu kira Maheer ya hanasu yana cewa su barshi issue din cikin gida ne.
Hankalinsu dawowa yayi kan Dad da aketa kokarinsa ceto rayuwarsa datake nisa,
Ammar ma aka gyarawa fuska duk bandage dawowa yayi dakin suka zauna zaman jimami da
qunci sbd babu me iya magana idan ba ganin sukai Dad ya farfado ba,
Maheer wasu hawaye ne masu zafi ne suka ganganro masa ahankali yana jin zuciyarsa na neman mutuwa,
Idan dad bai tashi ba baisan ta ina zai fara rayuwarnan ba da sauran familyn da nauy
insu zai rataya akansa baida mai jagoransa,
Ta ina zai fara fuskantar babbar matsalar da suka aikata su da yawa a wayi gari ace shi kadai ne zai fuskanceta sbd Ammar dai ya riga ya samu tabin kan da ba lallai ya karba hukuncin komaiba,
Tayaya zai iya
kubutar da jannah daga AZIZ shi kadai?
Innalillahi wainna ilayhi rajiun"""' shine abinda zuciyarsa ke maimaitawa yanajin kaman zuciyarsa zata fashe.
Mimi bata iya magana a yanzu karfinta ya qare tas tayi weak sosai batajin dadin zuciyarta ko kadan,
Saleem ma kusan baida abin cewa ko tambaya sbd komaima a yanzu kamar baida amfani,
Dukkaninsu qasar suke son bari su koma inda suka fito rayuwar zatafi musu dadi acan,
Zasu bude sabuwar rayuwa su sake gina sunansu cikin kwanciyar hankali da Aminci.
Ganin jikin Dad din yana sake nisa sai kawai Maheer ya kira jannah daya san dad din zaiso ace ya bude ido yayi mata ganin karshe.
Koda Maheer ya sanar da ita ana sallar ishai lokacin dan haka sallar ta samu kawai tayi jikinta na dan rawa zuciyarta na w
ani irin rawar tsananin tsoro da tashin hankali.
Ko mama bata tsaya fadawa ba ta fita hannuwanta na wata irin rawa.
Ganin yanayinta ya saka falaq hanata driving tace suje da driver su kaita tinda dad din baya nan.
Bata musa ba sbd bata cikin cikak
kiyar nutsuwarta matsanancin tsoro ne ya rufeta sbd batasan tina mutuwa akan mahaifinta da shine rayuwarta.
Tausayinta sosai falaq takeji sbd tasan irin tsananin so da kaunar datakewa Daddynta shi Jannah kewa Dad dinta dan haka kwatanta rayuwa babushi a
bune da shi kadai zai iya zarar da kai.
Koda suka isa asibitin falaq bata fita motar ba ta bari jan din ta tafi ita kadai sbd ta fara ganinsa ta samu nutsuwa tukuna.
Jannah na isa dakin a sanyaye ta bude ta shigo dukkaninsu suka dago jajayen idanuw
ansu da duk suka jeme suka zuba mata.
Sanyi qafafunta sukai ta tako ahankali hawayen cikin idanuwanta na saukowa ta nufi gadon Dad din wanda yake kwance kamar ba rai a jikinsa yayi mummunan jemewan data sakata rintse idanuwanta tana zaunawa bakin gadon
ta dora hannunta akan nasa tana fashewa da kuka mara sauti.
Tsit dakin yayi kowa ciwon ransa na qaruwa kukanta na ratsa kunnuwansu.
Mimi ce ta bude baki Ahankali batada ko wani karfi sosai ciwon dayake cin zuciyarta na bayyanuwa cikin mutuwar jiki ta
ce
"Mahaifinki bai hada soyayyarki data komai da kowa ba amma ayau mijin da kika zaba kikace shi kikeso wanda a hakan mahaifin naki ya zabi farin cikinki akan familynsa shine yake neman neman ganin bayan mahaifinki da ahalinki,
Me ahalinmu sukai masa d
ayake neman ganin bayanmu?
Wane irin miji ne zai cakumi mahaifin matar dayake aure bayan yasan baida lafiya sosai???
Jannah me kikeyi da wannan mijin?
Me zakiyi da miijin dayake neman rayuwar ahalinki?
Kalli fuskan Ammar kiga abinda yayi masa,
Wanna
n shine mijin da zuciyarki ta zabar miki akan ahalinki da suka zabeki fiyeda rayukansu?
Wannan shine sakamakon soyayyar da mukai miki tin kina yarinya?
Dago jajayen idanuwanta tai cikeda mamaki da tsoro harma da fargaba me tsanani tana kallan Mimi ka
fin ta maida kallanta kan fuskan Ammar da sai a lokacin ta lura nade take da bandage mummunan duka ne a fuskan ba kyan gani.
Waya Ammar ya fidda ya nuna mata hotinan da yayiwa AZIZ a lokacin daya shaqo Dad ya zubar.
Mummunan faduwa gabanta yayi ta da
go cikin slow ta kalli Maheer wanda idanuwansa suke jajir ya kasa kallanta.
Kan Saleem ta maida kallanta wanda ya saukar da idanuwansa da sukai jajir shima a hankali yana jin ciwo da radadin abun har qasan zuciyarsa.
Wani irin nauyi me girman gaske t
aji yana danne kirjinta ta juya ta kalli mahaifinta hawayen baqin ciki na gangaro mata tareda da jin soyayyar AZIZ LIMBA na sauka daga zuciyarta ahankali tana zubewa.
Ammar kuwa bude bakinsa dayake rawa sosai kamar me koyan magana sbd kansa dayake a juy
e tin dazu da azabar duka ta tayar da ciwonsa yana bubbuga kansa da hannunsa idanuwansa na sake rinewa da ja yace
"AZIZ LIMBA makashi ne,
Shine ya kashe Daddy mahmoud,
Shine yake kashe kowa,
Shine ya kama su Abraham,
Shine yakeson kashe dad,
Idan
ya kashe dad zai kashe kowa,
Kema jannah yace saiya kashe ki,
Zai kashe kowa,
Bazai dena ba saiya kashe kowa dayake zaadens sbd Qanwarsa,
Qanwarsa ce a kirjin jannah,
Qanwarsa ta mutu,
Yace saiya kashe kowa,
Ya fada da bakinsa.......
Shiru sukai
dakin ya sake daukan shiru maganganun Ammar na futa hayyaci ne kawai suke tashi ahankali kuka na zuwar masa.
Maheer zuciyarsa ta gama saddakar da komai vazan iya hana ammar maganar data saka su mimi shiga tinani ba sbd komai dai yazo karshe da alama.
Mimi gabaki daya hawaye take tsiyayarwa na baqin cikin jin Ammar na magana a zare basuda abinda zasu iya yi,
Saleem ma baqin ciki da ciwon zarewan Ammar din ne ya hanasa fahimtar abinda Ammar din yake fada.
Falaq dake tsaye kofa isowanta kenan taji
dukkanin maganar da Ammar yake fada akan Daddynta wata irin mummunan bugawa kirjinta yayi kafafunta suka dauki rawa zuciyarta na kasa dauka ta shigo idanuwanta na cikowa da hawaye masu zafi tace
"Daddyna ba makashi bane bazai kuma taba zama makashinb i
nsh......."
Ammar da dukkanin jikinsa ke rawa kanta yayi idanuwansa na rufewa ya shaqota yana bugata da bango da karfi bakinta ya fashe da jini ya saka hannuwansa biyu ya shaqeta yana cewa
"Saina kashe AZIZ LIMBA,
Saina kashesa saina kashesa kaman U
mmitah,
Saina kasheki,
Ai kene AZIZ LIMBA......
Mimi,Saleem da maheer da tsananin tashin hankalin dayafi wanda suke ciki sukai kansa suna kokarin kwace Falaq wadda bakinta ke jini sosai tana kokarin riqe numfashinta dake kokarin saka zuciyarta dena bu
gawa sbd bugun zuciyar ya