Showing 27001 words to 30000 words out of 57925 words

Chapter 10 - kuyanga complete

ranka ya Dade Allah yaja kwana yakara lfy



Yace "Amin

Fatima. Inkin futa kituromin LAMIDO



tace "To.



Bayan futarta tazarce Dakin MAMAH domin takai mata wannan batu sbd duk abinda take ciki saita sanarta kuma bata zartar da komai saida izininta



Jakadiya na zaune kusa da MAMAH tana mata hira



Shigowar FAATU yasa ta tsahirta tareda gaisata



FAATU ta amsa ta

reda zama kusada MAMAH



Ta zayyanewa MAMAH komai na abinda Mai martaba yatsara na bikin LAMIDO da *KUYANGA* Da kuma bikin nada LAMIDO Sarki da za,ayi



Jakadiya na qunsa tafuce da rawar jiki ta nufi dakin UMMAH Donkai mata Rahoto



UMMAH taga shigowar Jakadi

ya hankali atashe

Ranta yai matuqar baci dajin wannan kalami daga bakin Jakadiya kamar ta Dora hannu aka tayi kuka taji



Inama tana da damar da zata hana wannan Nadi



Jakadiya tace "Kibar komai ahannuna domin nima bazanso adora Lamido INA gani ba zans

o ace Yarima ne zaizama sarkinmu



UMMAH ta gyada kanta tana fadin "Nagode jakadiya nasan ke me qaunata CE



Jakadiya taxo futa adakin kenan sukai kicibus da Yarima shima yashigo dakin UMMAH



Kallon kallo sukaiwa juna ko gaidashi Jakadiya ba tayiba kowa ara

nsa akwai abinda yake

ayyanawa akansu



Yaxauna akan kushin yana fadin "UMMAH naxo gaya mikine zantafi turai nan da kwana biyu nagaji da zama agarinnan babu masu sona

Tace "Kamar yaya babu masu sonka baya gamu nida mahaifinka



Yace "Hhhmmm adane kike son

a amma ayanzu kam dagake har TAKAWA babu me kaunata kinrabani da gudan jinina kinkuma ki sanyawa Takawa ya yafemin yafaina fushi dani

Tace "YARIMA kai kake janyo komai gashi yanzuma zaka tafi kuma kasan bason tafiyarka yakeyiba Danhaka tafiyarka daid

ai take da karin wani laifin kanka sannan kuma abinda nayi daidaine agunmu nidakai domin inhar Yaron ya girma xai iya tasowa ackn wani yanaya na mugayen halayya ko kuma muzama abin kwatance



Inaso kacireshi aranka kafuskanci abinda ke shirin Kasantomu n

a Nadin Sarauta da mai martaba zaiyi akan kaninka LAMIDO

Yarima ya gyara zama da firgici akan fuskarsa yace "Da gaske UMMAH yanzu haka Takawa zaimini SBD yabakanta min rai. Tabbas saina dauki mataki sosai akai



Waye ya kawo miki wannan labarin?



Tace "JAK

ADIYA CE



yace "shikenan.

Yafuta yanufi Dakinsa yadebo kudi masu yawa aljihunsa yafito yanufi sashin da Jakadiya take



Cikin ikon Allah Yatararta Ita kadai kuwa



Tanaganinsa gabanta yafadi ganin irin kallon da yayi mata dazu tana ganin ko akwai manufarsa ta

hakan



Yakalleta ba fara,a afuskarsa ya mika mata kudi ahannunsa yace "Karbi wannan !

Jiki na tsuma ta karba



Tace "na menene wannan?



Yace "Nakine aiki zansaki



Tace '"aikin meye hakan? Wannan uban kudi yafi karfina



Yace "Yanda kika zama makisiya shine nake

so ki kashemin wani nima



Ta zabura "Baxan iya ba walh

Yadaka mata tsawa "zaki iya !! Waishinma kinji kowaye?

Tace "waxan kashe?



Kaitsaye yace mata "LAMIDO!!



taji dirar Kalmar akunnenta tadira gefe tana miko masa kudin "karbi kudinka bazan iya kashe

LAMIDO ba ka kaiwa wadanda sukai maka aiki akan MAHBUB suyi walh bazan iyaba



Yadaka mata harara yace "babu Wanda zansa yayi saike don haka kisani k'in yinki yana daidai da tonuwar asirinki

Yana gama fadin haka yajuya yabar ta tsaye atsorace take da wanna

n lamari ina ita ina iya kashe LAMIDO to yanzu yazatayi gashi tana bukatar kudin sbd yawansu yakai ace tagina kanta da rayuwarta na wasu shekaru toshin yanzu Yaya zatayi ? Rana zafi inuwa Quna!!



Mafita ce tazo mata arai gara taraba kudin biyu taje tasami

Fadawan da taga yasa su kashe MAHBUB tabasu sutayata aikin

******

Abin Duniya yadami Yarima gashi da gasken Gaske Mai martaba yajuya masa baya ko gaisuwarsa baya amsa masa don hakan ma ya qudiri niyyar kawar da LAMIDO domin yazamo dolen sarki yanad'

ashi agaba yakuma Auri *KUYANGA*



Shawara ya yanke natafiya Turai tun agobe domin in aka kashe LAMIDO kada adora zargi akansa gara ayi bayanan



Da safiyar Lahadi ya daga ko sallama da Mahaifinsa baije yayiba yabarwa UMMAH sallahun tagaya masa



Itako dama

ranta baiso ba



Da kuwa taje ga sarki tagaya masa ko uffan baice mataba shiru yayi mata dole tabar maganar yariman ta tafi



Amma ta qudurci yin aikin Asiri atsakaninsu domin janyo soyayyar yariman azuciyar sarkin

Yarima Yana dira akasar waje Allah yahadas

hi da wata bakar fata Ta nuna tana muradinsa azahiri bama tasan shidin Dan sarki bane saida taga alamomi a Dan zaman da sukayi na mintina a Airport



Hindu "Yar Minister ce

a jahar Kaduna mahaifinta me kudine sananne Alh Khalid Baffanyo



"Yar boko ce

gata da jijji da kai da dagawa Amma yau sai Allah ya damketa duk yanda take wulakanta samari a garinsu sai gashi ayau Allah yasa mata Soyayyar Saurayin da batasan asalin saba tashi guda

Dayake yariman ma na mamajo ne tuni ya afka cikin sonta shima tar

inga kanainaya da kissa don yasota takuma yi sa,a



Har rakiyarta yanema gidansa takuma bishi



Saidataje gidansa ta tabbatar shidin Dan babban gidane ta gane dawa take tare Domin tafahimci da alamar Dan gatane kamar yadda take yar gatan babanta



Saida s

uka kadaita sannan yahau tambayarta meya kawota England ?Tace masa tazo Hutu ne gun kawunta Wanda shiya riketa alokacin datayi karatunta acan



Takuma gaya masa asalinta da matsayin data taka na aiki domin tana aiki da Ministry of Health itace Director

asashen kula da Asibitocin Shiyyar Su



Ya jinjina kai yace " Ina sonki zaki Aureni?



Da zakuwa tace "Kwarai kuwa inhar da Gaske kake na amince maka amma kada ka yaudareni bani da dadi



Yayi dariya yace " nima ba Dadin gareniba.



Tayi dariya kawai



Aranar ta t

ayashi kwana agidan sunyi romance amma basu zarta nan ba don ya ayyana aransa ita zai aura takwanta masa



Aranar sun tsaida magana zaizo nanda sati biyu Kaduna yagaida iyayanta zai kuma tura magabatansa



Tunda suka tsaida magana da Hindu shikenan soyayya ta

dinke atsakaninsu akullum suna tare awaya ba dare ba rana Shaquwa sukai sosai in basuji muryar juna ba basajin dadi



Tana daga Kaduna amma kowa nata yasan da Fara soyayyarta da yarima



Iyayanta harsun San da sunansa domin ta gaya musu tuni



Dama ita kada

i suka Haifa itace shalele sunaji da ita basa son bacin ranta



Yarima yakasa sakat tuni yahado kayansa sai Nigeria



Amaimakon yadiro Kano saiya zarce Kaduna



Kai

tsaye yabi kwatancen d tayi masa



Ta aika da mota aka daukoshi aka kaishi gidan



Yaji Dadin tar

bar da tayi masa da yan gidan

Yai mamakin ganin shankwamen gidansu kamar gidan Gwamna ga tarin motoci kamar ana saidasu



Akaita kawo masa gaisuwa ma,aikatan gidan aka cika gabansa da kayan ciye ciye A main falour aka saukeshi



Mahaifiyarta taje taku

ma yaba da zabin diyar tata



Saida yajira mahaifinta Alh baffanyo yadawo suka gaisa ckn mutunci



Dayake mutumne wayyaye tuni yace yabashi ita yakuma bashi sati yaturo magabatansa



Yarima yai na,am



Sunyi soyayya kafin yatafi da yamma yai mata sallama yabi

jirgi yataho Kano

Yaringajin kamar karsu rabu tamkar Wanda tayi masa asiri yaringaji



Ransa Dari qal yasami Matar Aure yasan yanzu dole maimartaba zai sauko inyaji zaiyi Aure



Da Isar yarima gida kai tsaye gun mahaifiyarsa ya nufa



Tayi mamakin zuwansa bai

sanar mata ba



Yana murmushi yace "UMMAH dawowar gaggawace tasameni adalilin Matar Aure dana gamu da ita



UMMAH da mamaki tace " Matar Aure kuma yarima ?a INA?



Yagyara zama yazayyane mata komai



Tahau gyada kai tana jin farin ciki aranta domin jin yarinya

r yar masu dashine kuma hakan yayi mata arai tafiso shima yariman yayi Aure kamar yadda LAMIDO zaiyi domin Aure yana karawa mutum martaba da kima a idon Al,umma abin tinkahon tane ace tayi suruka Yar babban gida ba "yar Bayi ba dama



Tasawa abin

albarka tareda karfafa masa guiwa " na amince maka kayi Aure adaidai wannan lokaci Yarima domin makiya suji kunyar abinda ake shirin maka tunda nasan duk don abakanta maka aka shiryi Auren su balle anga kafito da maitarka karara ka watsar dasu zuwa gab

a mushirya kutunguila akansu inhar Aka nada LAMIDO sarautar

domin baxamu barsuba



Ya gyada kai yace "Nima akwai shirin Dana shirya akan LAMIDON, UMMAH saidai zan ajiye komai agefe sai bayan nayi Auren tukunna amma kiyi kokari Takawa ya karbi abin da muhim

manci ahada ayi tareda na LAMIDON domin iyayan yarinyar da Gaske suke asatinnan zasu Zuba idon ganina



UMMAH tace " kada kaji komai Aure fa kamar anyi Angama

******

Koda UMMAH tajewa da Mai martaba wannan zance Murna ma yayi domin yasan yin Auren Yarim

an kamar wata hanyace zatazo masa ta shiriya don haka saiya nuna amincewarsa da gaggawa tareda tsayar mata da maganar zai tura aje akai kudin Aure tareda tsaida musu rana daidai Dana LAMIDO



Taji dadi tayi masa godiya takoma yiwa Yariman Albishir



Da fari

n ciki yakwana jin antsaida masa ranar Aure sati uku masu zuwa



Yaiwa Amarya Hindu albishir



Ai ihu taringayi Dan dadi da farin cikin data tsinci kanta aciki



Tuni ta gayawa iyayanta tamkar suma sungaji da itan saigashi suma suna murnar



Ackn Satin kuwa

Mai martaba ya Aiko batun nan Aure



Galadima ne da Liman Amintattun Sarki sukaje kai kudin Aure Dubu Dari biyar



Da kwatance suka sami gidan domin mahaifin Hindu fitaccene babu Wanda baisan Gidan Minista ba a A T/wada Kaduna



Anbasu an amince musu nanda sat

i ukun Dayake kanin mahaifinsa ne da Yayan mahaifin nata da Amininsa suka karbesu agidan Ministan



Anbasu tukuici me tsoka tareda karramawa domin da tsaraba aka rakosu da zasu koma



Kaji da cake da lemuka da turarika da shaddoji haka aka zubasu a but di

n motarsu



Koda suka koma suka rattabasa sarki abinda suka gano cewar iyayan yarintafa Sunada mutumci da Halin girma



Sarki yaji dadi yasawa abin Albarka



Zancen Auren yarima da LAMIDO yazagaya gari anata irgen kwanakin dasuka rage sbd irin shagulgulan da a

ka shiryi

yi sbd nad'in da za,aiwa LAMIDO na zama sarki da zaiyi



Lefe ma yarima A England yatafi yahado



Shiko LAMIDO dayaje gun *KUYANGA* tambayarta yayi



"Gimbiya!

Takalleshi da murmushi kan fuskarta tana murza zoben hannunta da MAHBUB yabata kafin yara

su



Tace ahankali

" Harna zama gimbiyar ?ai naga Gimbiya Matar Sarkice wacce yakeso kuma



Yayi murmushi dama shidin ma,abocin murmushine yace "Zeenatu kenan ai kamar kinzamane Tunda saura kwanaki daga lokacin da Aka daura mana Aure nima naxama Sarki Kema ki

nzama Gimbiya tunda aranar za,ai Nadi Ta gyada kai tanajin annashuwa aranta da kuma sonshi ackn zcyrta

s

hima hakan yakeji aransa agame da itan



Yakatse shirun nata dacewa " Awace kasa kikeso ahado miki lefe?



Takama baki "Ni na isa? Wacece ni tab ahad

o anan



Yasha mur! Yace " keko kika isa kuma ke me matsayice da kima don haka daga yau kidaina ma daukar kanki maqasqanciya agidannan domin kintashi daga *KUYANGA* kindawo *GIMBIYA ZEENATU*



Tayi murmushi ita kanta sunan yayi mata dadi



Yaci gaba da fad

in"kinaji ko zamuje Sudan ko Dubai inhado miki komai acan nida Abokina Safwan tare mukai karatu dashi acan mahaifinsa ne liman na gidannan tare TAKAWA ya biya mana zaizo kugaisa



Takawa yana sonki Zeenatu ki godewa Allah jarabtar da Allah yayi mk arayu

wa tazame miki riba da ci gaba domin ayau yakirani yakaramin kudi akan Wanda yabamu na siyayya nida yarima yace ke tadabance inyi miki siyayya mekyau



Yakarasa maganar yana kallon kyakykyawar fuskarta yana murmushi



Itama murmushin takeyi tana fadin "Na

ji dadi nagode ayiwa takawa godiya



Yace " To ni zankoma



Tayi masa yar rakiya da baifi taku biyar ba ta koma tana waigensa



LAMIDO ya burgeta tabbas yanada aji ga iya magana da kalami duk macen dayace yanaso dole ta amsa domin shi din abin sone



Tana

sh

iga Daki tafada akan gado tana fara,a



Zulaihat tabita da kallo tana fadin "Yarinya tashiga kogin soyayya tafito



Dafatan kinyo iyo kinkamo kifi?



*KUYANGA* tayi murmushi tareda tashi tazauna tana fadin "Zulaihat kifaye ma nakamo ba kifiba tabbas LAMIDO

yatafi dani kamar yadda nima natafi dashi



Allah nake godewa da yabani wannan baiwar ta zama matarsa gashi Yace Takawa yana sona yakara masa kudi akan Wanda yabasu da yarima na soyayyar lefe Mahaifiyarsa kawai nakeji bansaniba ko itama tana sona kamar

yadda Sarkin ke sona?

Zulaihat tace "Hhhhmm Zeenatu kenan aike abar soce itama banajin zataki sonki tunda ta tako har gidannan tazo miki barka da gaisuwa Dan haka kigodewa Allah kawai

" Allah nagode maka.cewar *KUYANGA*Zulaihat tace "Ga magunguna can i

nji Iya Sha,awa tace kada kiyi sake da kowanne masu kyaune akwai nasha da nono dakuma nasha da Zuma anjima zata kawo miki na tsugunno

*KUYANGA* takama baki " oh maganin mata kuma tun yanzun?



Zulaihat tace "Eh aishine daidai hakan kinga abin xaifi kamaki

Sosai

" Hhhmmm Allah dai yasa ba daci



Zulaita tace "koma me gareshi haka zakisha tunda kinsan Halin tsoffin nan insuka bada Abu ba,ashaba fada zasuyi suce suna mana gata muna gocewa



*KUYANGA* Tayi murmushi tadauki magungunan tafara hada wa xatasha

******

Yarima yadauki wayarsa yalalubo nambar abokinsa SAHABI da suka Dade basuyi wayaba



Acan bangaren SAHABI yana ganin kiran Yariman yayi murmushi yadaga yana fadin" Dama kana da nambata kamance dani



Yarima yace "inada ita mana fushi nayi dakai na abinda kayi

min amma yanzu na huce Dan haka Ina gayyatarka Aurena karshen wata



SAHABI yayi murmushi yace " Allah yasanya

Alkairi nima Auren zanyi nanda sati mezuwa kafin nakama



Yarima yace "Shegen kaya wato banda nakira bazanjiba kenan ?lallai na yarda karikeni arank

a SAHABI



SAHABI yace " ba haka bane yarima Aurenne ba Wanda nakeso ba Hadani akai da yarinyar diyar kanin mahaifina ce ita ke sona



Dariya yarima yabushe masa yace "sunmin daidai walh domin insun kyaleka " yar talakawa zaka dauko musu banza me sakaran

ra,ayi



Sahabi yace "kai " yar INA zaka aura?



Yarima yabashi labarin Hindu da yanda suka hadu a Airport a England



SAHABI yace "Hhhmmm to bagiringirin ba dai tayi mai



Yarima yace " oho dai nafika tunda ni Auran Soyayya zamuyi



"Nima bawai kinta nakeba

tunda yar 'uwa tace Ina Zeenatu naji ance abinda ta Haifa yarasu



Yarima yace " Eh, Sunkusa Aure da LAMIDO...SAHABI yakatseshi da sauri "ya akai hakan dama soyayya sukeyi?Nan yarima yazayyane masa komai

SAHABI yace " Gud ammafa naji dadi LAMIDO yaburgeni

Allah yasanya Alheri



Yarima baikulaba yai masa sallama



Acan kasan ransa soyayyar Zeenatu na nan baxai mantawa

Anata shirye shiryen biki akowane bangaren



Shi yarima agidansa na cikin gari zai zauna baiyda ra,ayin zama acikin gidansu wai kada atakura masa

shida amaryarsa

Shiko LAMIDO sashi guda aka gyara masa agidan me dauke da dakuna agidan gidan yasha gyara babbane dama ba kowa ciki

Aka zuba komai na alfarma agidan



Lefe yazo daga Dubai akwatuna goma Sha biyu cike fal da kaya tsadaddu



Komai dozinne ciki koina acikin gidan da wajen gidan zancen kayan lefensa akeyi domin sunhadu sunburge kowa



Saida aka kaiwa takawa yagani yace sunyi yasa albarka kana mata suka hadu s

uka dauka bayan Su MAMAH DA

FAATU sun gani aka kaiwa KUYANGA



Tsoffinsu sunsaka albarka sunyaba Angyagije Zeenatu anfiddata kunya dukda sunsan arina

Shiko Yarima karya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login