Showing 42001 words to 45000 words out of 57925 words
yaita musu tuni da Sauran zafafan Addu,o,in dake bakinsa Wanda G.Zeenatu tabashi wasuma ajiya
yasansu
Ganin yanda ya tunkari wannnan Qurar data ke gabansu babu tsoro yasaka suka rufa masa baya suma cikeda karsashi
Suna tunkarar Qurar data turnike samaniya suna addu,ar ckn ransu
Saida sukai dab da qurar datayi jajir gabansu kana suka tsaya ganin ub
an tafiya yatsaya
Sunyi tsaiwar minti biyar saican sukaji ankwashe da wata mahaukaciyar Dariya wacce ka iya fasa dodon kunnen Wanda ya warke daga cutar bebenta
Saida fadawa suka toshe kunnensu shiko jarumi ko gezau baiyiba idonsa ckn Kurar yake Dan kada a
shammacesu
Aiko dai kafin kiftawar ido saiga wani katon Aljani me katon kai da fala falan kunnuwa da ido daya akusada gajeran hancinsa ga bakinsa katoto tamkar ashana yar hamsin
🤣
Yanda Lamido bai tsorata ba to haka suma fadawan basu tsoratanba sbd Sun
san arina domin wannan qurar datayi jajir ba banzaba
Aljanin nan ya nuna LAMIDO Da wani takobi yana fadin "kai yaro katsira da kanka ta wata hanyar amma ba tanan ba inhar kana son ranka to kaja yaranka Ku koma inba hakaba yanzu zandau ranku baki daya.
LAMI
DO cikin Jarumta yace " Meye hadinka damu ?kabamu hanya muwuce domin kuwa bazamu komaba tunda ba gurin ka mukazoba kuma kasani munfi karfinka domin muna tareda tasirin dayafi naka
Aljanin nan yayi wani gurnani yayo kan Lamido gadan gadan da
wukar nan dake
hannunsa tana sheki zai soka masa
Aiko LAMIDO yayi azamar gocewa dayake yanada zafin nama tun yana karami ya haddaci zafin nama Wanda ba kowa keda wannan baiwarba
Anan sukaita artabu daya kawo suka saiya goce hardai LAMIDO yakai kasa karfinsa yafara yin l
ow
Fadawan sukai azamar yin sufa sukayo kan Aljanin da sara da takubbansu
Take takubban suka lankwashe
Yajuyo Kansu afusace
Qaribu shine kakkarfa yadungule hannu yakai naushi ai take hannu ya qame yaki motsawa
Shiko Labahani kan Aljanin yayi da
kabbara abakinsa
Aitake Aljanin yayi taga taga zai fadi
Labahani ya kai masa angaza saiko yafadi
Amma dasukai kasa tare sai Aljanin nan yakaiwa Labahani naushi daya take Labahani ya suma
Shiko LAMIDO ta maza yayi ya mike Tuno takobinsa da Gimbiya Zeenatu
tabashi wacce tace tayi rubutun Ayatul qursiyyu ajikin takadda ta daure ajikin mariqarta wai tana so wukar takasance cikin tsari kada aljanu su saceta kuma zatayi masa amfani domin ta wanketa cikin Rubutun datayi da tawada na ayoyi ta tsuma Takobin ack
A
iko wata sufa dayayi kafin Aljanin ya daga Labahani yadawo kansa tuni yadaukota ajikin siddin. Dokinsa
Aljanin yayo kansa yana haniniya yana gunji
Take Lamido ya Kai masa sara akansa
Saijin Tasss!mukai kai yarabe biyu bai barshiba yasake kai masa Sara
ahannunsa saiga hannun dama akasa
Rigibbbb!Aljani yazube akasa matacce jini na zuba ta koina
Lamido yayi hamdala aransa
Ya maida Takobin ma,ajiyarta ya sakale jikin doki yanufi su Qaribu da Labahani donkai musu agaji sun jigata
Kan Labahani yafara zuwa gan
insa sheme akwance yasuma
Ya bubbugashi yaga ba motsi sai tafi da sauri yadauko ruwa a gorarsu katuwa
yazuba ahannunsa yaje yashafa masa afuska
Take Labahani yaja ajiyar zcy ya bude idonsa
Ganinsu Lamido kansa yai saurin tashi Zaune yana kiran sunan Allah
abakinsa
LAMIDO yace dashi "Sannu kaji mun Auna arxiki da bai kashe kuba kunyi kokari nagode
Yatafi da sauri gun Qaribu Wanda ke Zaune kamar mutum mutumi yana zare idanu hannunsa asage yakasa motsawa
Yarima ya kama hannun yaja iya karfinsa hannun yakasa m
otsi Yayi mamaki sosai wato Aljanin tsafencesu yayi kenan
Take yatuno da addu,a tuni yahau tofe hannun
Ckn ikon me sama,u saiga hannun na motsi qasss!!qass!
Kana jin karar kamar ana karya rake
Ckn mintina saiya dawo daidai Basu tsaya wata wataba suka mike
suka haye dawakai akaci gaba da tafiya ganin hanya ta washe ba sauran qura
Anan LAMIDO yakara yi musu nuni da irin karfin da ayar Allah ke dashi kuma suma sunga amfaninta garesu
Sunata tafiya suna hutawa har sallahr azahar suka tsaya sukayi jikin wasu
dogayen bishiyu sannan bayan sun idar suka kara gaba
Can LAMIDO yahau murmushi ganin inda suka zauna da tsohon da suka gudo tare daga gidan da aka tsaresu kuma daganan dazarar kadance da inda tsohon yace masa Bukkar dayasaka mutumin daya tsinta aka kamashi
akansa ba nisa
Sai yaji inama aranar yabishi yagano bai biyewa gajiyar da yayiba da saurin dayake nason komawa gidaba da tuni yanzun ba kwatancen dayai masa zaibiba
Can gabansu yafara hango wasu bukkoki Jere sunkai biyar da alamar itace tunda dama tsoh
on yace masa bukkarsu guda biyarce agun
Da murnarsu suka nufeta zasu tunkareta kawai saiganin gabansu sukai wuta naci haikan akan bishiyu
Ga wani kara daya cika dajin ana kwallawa sosai duk don su firgita Amma jajirtattu ko gezau
basuyiba
LAMIDO yace mus
u "Ku ankare kada kumanta da addu,a kusani fada da Aljani sai anshirya muko bamuyi shirin fada da aljanba tunda bamuyi zatoba Dan haka Da ayar Allah zamu yakesu
Sukace " kwarai Ranka ya Dade muna sane
Suna rufe bakinsu saiga wuta tadira agabansu acure tan
a tiriri da nishi jajir
Take sukahau addu,a ckn ransu
Wutar ta hade ahankali suna kallo har tazama suffar mutum wani basamuden kato amma fuskarza kuyas karama da muryar tsoffi yahau fadin "Ku koma kujuya ko yanzu inkaddamar muku zankoneku inkuma je in kon
a Wanda kuka zo dauka.
LAMIDO yacika da mamaki yace"Tayaya akai kasan wani mukazo dauka ?
Yabushe da dariya me futar da feshin wuta yana fadin "Aikomu akai mukashesu Ku Dan kar kuyi nasara Dan haka saimun cika aikinmu
LAMIDO yace " karya kakeyi saidai muk
ashe ka baka isa kayi mana komai ba makiyin Allah ta,ala
A take Aljanin yayiwa LAMIDO feshin uban wuta Lamido yayi tsalle gefe guda tareda Fara addu,a yatofa ackn wutar saita baje saiga toka agun natashi
Aljanin yayo kan Lamido yana feshin wutar
LAMIDO ya tunkareshi ba tsoro shima da tokobinsa yana kabbara ya shigeshi kawai
Aljanin yakurma ihu ya baje gefe saiga Lamido yafito ta cikinsa lafiyar Allah ko girgiza bai yiba
Aljanin yace "kai yaro kayi gaggawar mika kanka fa fada dani ba dadi
Lamido y
ace " Baka isa kayimin komai ba muje zuwa
Aguje yasake sihigarsa baifasa addu,ar dayakeba ya saita takobinsa cikin wutar
Aiko take wutar tayi tartsatsi tayi sama ta dawo kasa ta baje ta zama toka saiga bishiyun dake ci da wuta suna hayaqi
Lamido faduwa
kasa yayi sakamakon ya shiga aguje Ammafa
jikinsa ya gaya masa don kasa tashi yayi saida sukai maza suka dagashi suna karkade masa jiki suna masa sannu
Labahani yabashi ruwa abaki
Aiko yanasha yaji karfi ajikinsa ransa yayi dadi
Suka mike kowannensu yahay
e doki sukaci gaba
*WAI INA LABARIN "YAN AIKEN YARIMA NE?*
Tunda suka biyo bayansu suna ta binsu in sunyi suma suyi ins LAMIDO sun tsaya suma su tsaya duk Dan karsu gansu ason samunsu sunfiso saisu LAMIDO sun zauna hutawa saisukuma su sad'ada su shamma
cesu ko in sunyi baccin gajiyar hanya saisu cimmusu su cutarsu
Saidai kuma hango Guguwar data taresu LAMIDO da irin yanda suka hango a artabun arangama nafada da Aljani tuni suka tsorata suka juya jiki asanyaye don komawa gida da nufin insunje suce ai su
nkaddamarwa su LAMIDO da fadawan tunda sunsan dajin zaiyi hadarin da mashiginsa bazai fitoba sai tsananin rabo
😅🤣
yo ai da kunje dai
***********
Suna isa bukkar suka hango ta tsakiyar hayaqi yana fitowa DG cknta
Da addu,ar dai bisa bakinsu suka nufe
ta sun dauka lamarin Aljanun ne ciki
To Ashe tsohonnan ne yakunna murhu ya Dora ruwa yanata furfita hankalinsa kwance ga Wani can kwance kusa dashi
Suna shiga da sallama tsohon yatashi ya kallesu zaiyi magana kenan sai yayi shiru yana kallon LAMIDO dake m
asa murmushi
Shima saiya saki fara,a daya tuno da fuskar LAMIDOn
Ya bashi hannu suka gaggaisa tareda nuna musu gurin zama bakin gadon bonon
Suna zama yahau fadin "Bawan Allah Ashe zama dawo kwana kusa?
LAMIDO yace " walh dalili me karfine yadawo dani domin
bayan rabuwar mu natafi gida dazuwana gida sainatarar da mummunan labari wai
mahaifina yarasu amma ansace gawar annemeta sama ko kasa
To ganin sunce anyi bincike akaf ckn garin ba,a gano inda takeba yasa natuno da labarin da kabani na tsohon nan daka ce k
ataimaka Wanda mutanan nan suka kawo bakin ruwa suka yar har kai kuma ka daukeshi ka kawoshi ckn bukka ka ajiye....
Tsohon yahau gyada kai yana nuna na kwancen yace "aiko dai anyi hakan akaganshi can kwance yana bacci wato tunda nadawo yana nan inda nabars
hi dayake anyi masa wani siddabaru ne nayin dogon baccin awanni bai farkaba sai shekaran jiyan Wanda daya farkama naga baida cikakkiyar lafiya maganar ma bata fita shiyasa nadage akansa inata masa taimako na magunguna dayake na naqalci sanin saiwowi da ita
tuwan magungunan gargajiya tun akauyanmu sana,atace rashin kowa nawa yasa nadawo nan ina rayuwa nikadai sbd anci garinmu da yaki
Da Sauri LAMIDO ganin yana motsa kafarsa yahango wandon jikinsa na sakin kayan sarauta ya mike yanufeshi yana fadin " Anya w
annan ba mahaifina bane ?Kai!! Wannan Takawa ne
Yana mirginoshi shikuma yana farkawa yabude idonsa ahankal
sukai ido biyu da *Sarki Abdallah*...
Tamkar Anzuba ma LAMIDO ruwan sanyi azcyrsa yaji yasaki murmushi ya rukumkume mahaifiyarsa yana fadin "Tsarki
yatabbata ga ubangijin sammai da kassai Allah nagode maka da zato na yatabbata Ayau da mahaifina yazamto da ransa nayi ido biyu dashi
Takawa ma murmushin yasaki yahau shafa fuskar LAMIDON
Ba bakin magana lafiya tayi masa karanci muryar bata fita sosai
bakin dai yaketa motsawa shima
godiya yake ga Allah
Tsohonnan yadubesu yace " ikon Allah kenan Ashe dama D'an nan wannan mutumin mahaifin kane bamu saniba muka rabu?tabbas Allah me yanda yaso to nagodewa Allah da Allah yakawo Ahalinsa domin kullum cikin t
ausaya masa nakeyi dama domin alamu sunnuna wani mugun abun akayi masa
LAMIDO yace "Ai yanzu bamuga ta zamaba baba daukarsa zamuyi mutafi dashi sbd dajinnan yanada matuqar hatsari Allah ne kadai yakawomu qalau ckn kulawarsa amma munyi gwagwarmaya DA Aljanu
da alama kuma turensu akai mana karfin Addu,ane ya tseratar mu
Baba tsoho yamike yahau hada kaya yana fadin " ainima binku zanyi kafata kafarku domin zanso inkasance kusada bawan Allahn nan domin taimaka masa da wasu magungunan tunda naga sunfara masa ai
ki fiye da farkon haduwata dashi
LAMIDO yace "ba matsala shirya kayanka muje dakai din
Adokin LAMIDO suke tafe da Takawa yana bayansa Baba tsoho na rungume dashi LAMIDO na cin uban gudu da doki TAKAWA na tsakiyar kenan domin ba dama abarshi shi kadai abaya
n LAMIDO saiya fado tunda jikinsa yasaki ba karfi lfy wala
😊
**********
Sai bayan magriba kana suka shigo ckn garinsu bakowa yaganesuba sbd duhun d gari yayi
Saida suka shigo cikin unguwane ma sannan mutane suka fara gane kosu waye
Aiko take
Unguwar akaita binsu ana murna mata da maza ana ga MAI MARTABA ga SARKI Na 1
Kan kace kwabo Har fadawa dake can afada sunfirfito taryensu
Har Ckn sashin Takawa aka rakosu kana mutanen suka koma da fadawa
Koda Zancen bayyanar sarki tajewa Waziri ba karamin
murna da farin ciki yake ciki ba duk da lafiya bata ishe shiba amma ahakan ya gangaro yataho ganin TAKAWA
LAMIDO yasa wani bafade yaiwa Baba tsoho jagora har makwanci yabada umarnin anemo abinci akai masa
Waziri harda kukan murna domin burinsa akullum ya
ga ranar da zai nemi yafiyar Takawa ya yafe masa sbd dinbin laifin daya aikata masa duk d komi daya faru Dole Fulani take masa
Kan kace kobo manyan malaman Sarkin sun hadu dasu Zagi,sarkin fada,liman,da sauran masu fada aji
Suko iyalan sarki kafatanin su
sun taho sashin nashi a sukwane da labarin ya iskesu kowa murna yake na dawowar LAMIDO da Takawa gidan banda Fulani da Danta Yarima
Zcyr Fulani zafi take mata domin tasan katsewar farin cikinta yazo arayuwa tasan shikenan dole asauke Yarima a karaga
Gan
in ma Takawar baida lfy yasa ta danji sanyin ranta domin ta nak'alta aranta saita bashi guba don yakarasa kawai
Shi ko yarima mamaki yaringayi na ganinsu sun dawo domin yagama fidda rai dasu tabbas saiya hukunta fadawan nan nasa tunda har sukayi masa kary
a da cewar sunkashe LAMIDO da "yan rakiyarsa
A fuska ya nuna murnarsa ta dawowar takawa gida har fadi yake abainar jama,a
" wannan Abu da mamaki yake mutum ya mutu anemi gawa arasa amma yanzu ace angano Shi da ransa awani daji kai akwai ayar Tambaya anan
.
Fulani tayi karaf tace "Yarima kana mamaki da ikon Allah kenan...
MAMAH tace" wannan abu saidai lamarin jinni faFulani ta kwada mata harara
Itako FAATU batace kanzil ba saima ta dubi LAMIDO tace "Dan Albarka tashi kawuce sashin ka kayi wanka ka huta kaji
Allah yabiyaka da Aljannah kayi kokari haka akeson D'a dan halak
Fulani taji qunar wannan kalami na FAATU domin gani tayi ma kamar gugar zana tayi mata tabbas da ace ansan da cewar Yarima Ba jinin takawa bane agidan da zatace da ita takema
G.Zeenatu ta mike asanyaye tafuce LAMIDO naganin futarta yatashi yabi bayanta
Da one by one kowa yafuta aka bar takawa yana bacci shi kadai
******
Ta rungumeshi tana cewar " mijina kai jarumi ne gwarzo Wanda cikin maza sai an shekara za,a sami shigen irin
ka cikinsu tabbas banida fargabarka inza,a futa yaki tun tafiyarka jikina ke bani zakayi nasara Allah yasa kafi haka Allah kuma yakarawa takawa lfy
Ya kara mannata da jikinsa ya tsotsi labbanta yace "Amin, INA me farin cikin dace da Matar Aure da nayi kin
a son mahaifina dolene insaka miki da Alkairin abinda kikai min amma in tambayeki mana
Tace " inajinka mijina tambayeni na shiryi baka amsa
Yace "shin wai a ina kika koyo zafafan addu,oin da kika koya min da har ayau nake fahari da jin Dadin sune suka cece
ni alokacin Dana shiga musiba atafiyarmu
Tayi fari da idanunta masu haske tace " Allah yajikan MAHBUB shine malami na daya koyamin komai na addini shiyasa baxan mance dashiba
Ya jinjina kai "Allah yajikansa nayi Alqawarin inhar kika Haifa min D'a namiji s
unansa zansaka
Tayi murmushin jin Dadi " nagode
Yashafa cikin nata yana fadin "yaushe zaki bani babyn nema dai?Ta rufe idanu '" nima ina na Sani
Yace "kinsani mana.
Tace" kai!kamar Yaya ?Ai Allah ne da sanin
Yace "to naji na yarda Dan Haka ki shirya nan d
a kwana uku zan shirya mana Visa muwuce England Ni dake da Takawa inaso musake amarci sabo acan abani baby D'an can amma kishirya yin karatu acan domin inaso kiyi karatu na shekaru biyar ko hudu akasar waje
Ta zaro idanu zata ce wani abun
Ya Dora hannuns
a akan lebanta yace " haka na tsara domin karuwarki Ce
Hhhhmmm dama daya barta tayi masa wata tambayar ai
muma maji ko fans? Amma yakatseta to muje zuwa maji anjima insunje gado ko zata fada muji muma
Ba Karamin kaduwa wadannan Fadawa da suka kawowa LAM
IDO Sarki na biyu kayan marmari sukaiba domin sunsan ayau dai me fitar dasu sai Allah
Kusan fadawa majiya karfi su biyarne suka tasosu agaba suna ingiza keyarsu suna fadin "Munafukan Allah ta,ala saikun gaya mana inda kuka samo wannan gwaiba dahar kukai nu
fin kashe Sarki na biyu
Sukam dai tsoro da fargaba ya hanasu magana sai zare idanu suke kuma muzuransu bazai taba futar suba
Da aka kawosu gaban LAMIDO sai suka zube suna masa ban hakuri tun kafin ma yakai ga tambayarsu
Shi abinma mamaki yabashi saiyace
musu " Waye yasaku Ku aikata min hakan?
Sukai shiru Kansu akasa da alamar Bazasu iya fadaba ko suna jin tsoro kokuma nauyin fadin Wanda yasasu
LAMIDO sbd ya tsoratarsu zaiyace "kunsanda kun aikata babban kuskure na laifin kisan kai tunda ni kukai niyyar ka
shewa ta hanyar sakamin guba a Abu inci sai gashi Allah yatsareni bawana yaci Shima Bai mutun ba amma yana kan gaba kufada waya saka Ku aikatan hakan ko kuma insaka akashe ku
Sun tsorata amma sbd kafiya da taurin kai irin nasu babu Wanda yayi niyyar fada c
ikinsu
Da LAMIDO yaga hakan saiya fusata yace atafi dasu a hukuntasu hukunci me tsanani harsai sun fada
Nan danan karfafan fadawan nan suka ingiza keyarsu domin cika aiki
Kan