Showing 54001 words to 57000 words out of 57925 words
tayi karatu shiyasa Lamido yaga dacewar yatsaya tsayin daka yag
a tasami zuzzufan ilimi duk da shi takawa yafison yaga anyi mata Aure itako matsalarta daya da bata kula samari ita samarin ma haushi suke bata
Ko Kawa batada, domin harta kammala sakandare bata taba jonewa da wata diya mace ba amatsayin suyi wani wai kaw
ance ba sbd Ita din ta dabance bata daukar rainin hankalin mace ko nmjn kuma tanada zafin zuciya
Agun Kakanninta su MAMAH da FAATU taji labarin Fulani da irin kitimirmirar da akayiyyi abaya Wanda Ance mata kuma duk fulanin ce ta haddasa komai takumaji lab
arin Jakadiya da yanda bayan ta fito a furzin tabar garin baki daya tayi nesa da gidan sbd tsananin kunyar mutanen gidan da takeji
Haka waziri yayi nisa shima da gidan domin koda yafito shima daga gidan yari Bai yadda yazo ya hada ido da Takawa ba Don kuny
a duk da Takawar yace masa ya yafe masa abinda yai masan domin yaci albarkacin Amintakar da sukai tun suna yara
Yarima ne ma tasanshi domin tun tasowarta takan ganshi ya zozzo gidan shida iyalansa amma basa dadewa suke komawa
Wanda Har suka jone da Autar H
indu wacce shekara biyune tsakaninsu me suna Khairat
Ita kanta G.Zeenatu tayi mamakin yanda Khaleesat tasaki jikinta da khairat har suka kulle tabbas tasan khairat taciri tuta tunda Khalisat din akwai Shariya
Ciroma Ya girma yaxama Saurayi karatunsa yake
yi a can Kasar da suke Da zaman Kuma da Allah yataimaki Yariman Sai Allah yabashi Yaron da hankali yanada girmama Na gaba dashi yakanzo gidan Yace Hutu yazowa Takawa sbd shikam baida kakan daya wuceshi ko Kaduna baifiya xuwa ba gidansu Hindu mahaifiyarsa
Ko kusa bayada labarin Wani waziri sbd iyayansa sunajin kunyar sanar dasu Gidansu Fulani kuwa yakanje yayi kwanaki agidan idan yazo kasar
********
Fara karatun Khalesat mahaifinta Lamido yasai mata mota Panadol EXTRA one door sbd zuwa sch
Alokacin datayi
shekara Biyu ne da fara karatun nata mahaifinta Lamido yashiryi yi mata Party Na Cikar Shekara 20 Wanda yatanadi Ranar amatsayin ranar farin cikinsa sbd shima aranar yacika shekara hamsin 50
😳
tab lallai Lamido ansha miya
Yayi gayya sosai har
gidajen Radio aka kai sanarwar Sbd taro sosai za,ayi kuma aharabar gidan za,ayi Wanda ko mutane Dari biyar ne zasu iya cika agun batareda gun yacushe ba
Hatta Yarima dayaji saida yasako iyalansa agaba sukazo Nigeria domin halartar wannaan gagarumin Taron
Birthday dayake alokacin Ciroma da Khairat sunyi Hutun sch Dan haka da murnarsu da Doki suka biyo iyayansu Nigeria
Aranar Taro Ancika tun safe guri yayi guri kujeru farare aka ajiye sunfi a kirga mata da maza sunzozzo
Dayake mawaqa sunyi mata wakoki guda b
iyar saiya zamto anata jin wakokin kafin fitowar iyayan taron gurin
Lamido yayi matuqar mamaki ganin SAHABI abokin Yarima shima yaziyarci gurin shida iyalansa
Me dakinsa Na kusa dashi da D'ansa MA,ARUF Wanda suke matuqar kama shida SAHABIN kwabo da
kwabo t
amkar antsaga duk kyan SAHABIN ma,aruf yadauko
Yarima da iyalansa Na kusa da SAHABI Wanda suke a gefen da aka ware Na manyan baki
Dama yariman ne yasanar masa ta waya dayake suna zumuncinsu tamkar wani Abu bai taba faruwa dasu abaya ba
Saida guri yayi d
amqam da mutane ancika makil kana Lamido da Gimbiya zeenatu da Gudaliyar "Yar tasu suka fito suna wani tashin kamshi da kayan sarauta abin sha,awa sunjero Very Cute Family dazarar kungansu masu karatu saikunji inama kuna cikin familyn nasu
Aka hau tafi ak
a saki wakar Birthday wacce Nura M inuwa ya rera mata
Idon kowa nakan khaleesat yanda take taku cikin kasaita tabbas idan za,a bata sarautar garin Taskira zata iya Action da izzar da sarakai keyi alokacin da suke kan mulki ko in mulkin ya motsa
Saida suk
a zauna sannan salon wakar Birthday ta canza aka sako ta Ogah Umar m shariff
Saida akasha waka ana jin dadinta ana rangaji ana gyada kai yanda Umar din yake yabon khaleesat da kuzuzuta ta ckn waken nasa saika rantse da Allah dama yasan halayyarta da komai
nata yanda yatsara hhhmmm kawai baiwar wakarsa ya baje
MC ya mike ya fara Godiya da Allah daya kawosu ranar da suketa jira da kuma jawabin maqasudin taron nasu sannan ya bukaci Khaleesat data tashi tafito fili tayi jawabin Godiya tareda yiwa bakin dasuk
a halarci walimar tata Godiya da fatan Alkairi
Ta mike ta fito tana takun kasaita tana rangaji dama gata akwai diri gata dai abin ba magana komai yaji gashi har gadon baya tasha tsadaddun kaya Na sarauta da akai odarsu a waje
Ta karbi bututun
magana tafara mgn da zazzakar muryarta dake amsa amo agun dacewa " Da farko ni Khaleesat INA me Godiya gareku "yan'uwa da abokan arxiki da kuka halarci wannan gagarumin taron da Mahaifina abin sona yashiryamin domin farin cikinsa na cikata shekara 20 daid
ai aduniya Ina Godiya ga Allah INA kuma Fatan Allah yakaro mana shekara masu albarka yakarawa mahaifina da Kakana Takawa sarki Abdallah Nisan kwana sannan ina me mika Godiya da jinjina ga mahaifiyata Gimbiya Zeenatu Na tsayawarta tsayin daka wajen bani kya
kykyawar tarbiyar da takeyi sannan itama ina me jinjina gareta Na yanda taga rayuwa tayi kuma gwagwarmayar rayuwa tareda karbar kaddararta hannun bibbiyu amatsayinta Na marainiya sannan mace me hankali da hkr da kuma zuzzurfan tunani da hangen nesa Sai Kak
annina MAMAH da FAATU tsofaffin Kirki ina mika Godiya garesu suma saikuma Manyan baki Ina musu barka da zuwa UNCLE SAHABI da UNCLE YARIMA Allah yamaida kowa gidansa lfy amin
Tana gama fadin hakan ta mika Lasifikar magana ta juya ta koma mazaunin ta
Aka hau
tafa mata RAF!RAF! RAF!!
Matuqa ta burge kowa Na gun baga iyayanta ba da suketa murmusawa Na yanda ta burgesu suma suke kuma Alfahari da samunta
Mutum biyu agun bayaga burgesu da tayi ta tafi da hankalinsu ta sace musu zuciya tun tasowarta dataxo gun MA,
ARUF yakasa sakat tun zuwanta gurin kafinma tafito fili tayi magana ta tafi dashi haka tunfata maganarta yatsira mata idanu kalamanta da zazzaqar muryarta Na tsumashi
shima CIROMA Khaleesat ta tafi dashi matuqa yaji duk duniya ayau inba khaleesat ba Sai r
ijiya
Tabbas Yaga Matar Aure ayau dama akwai Matar da Dadynsa yaso ya manna masa wai sunason ya Aura diyar
ubangidan Yariman ce shiko baya sonta duk da musulmace baida ra,ayin son Yaga ya Auri Baturiya
Dayake tsakaninsa da Mahaifinsa Yarima babu Yar boye
boye ko qunbiya qunbiya tuni ya karkato gareshi ya rada masa sirrin zcyrsa ackn kunnensa
Yarima yayi murmushi yace dashi "bakada Dama Son kamanta akwai maganar Lailah akanka kadafa kazama me Zara mana
Ciroma yace " Dady walh bazan boye maka ba bantaba son
Lailah ba umarni dama xanbi kuma zanshiga quntatuwa Dan Allah kataimaka min kada Na cutu kashigen gaba Na mallaki Khaleesat amatsayin mata kaima Auran soyayya kukayi katallafamin nima nayi Auren soyayya a Aurena
Yarima yace "naji kwantar da hankalinka zan
yi yanda kakeso tunda amma kasani Sai inkayarda zaka Auri Lailah din kada ka watsan kasa a ido ka aminta da lailah inyaso Sai in Mara maka baya kasami khaleesat kafara Aurenta Sai daga baya ka Auri Lailah din
Ciroma ya murmusa yace " Na amince Dady farin c
ikinka nawa ne tunda kanada burin kyautatamin nima zan bi umarninka inhar katsayamin nasami Khaleesat tabbas bazanki Lailah ba
Yarima yashafa bayansa yace "Sha kuruminka kamar anyi angama kafin mutafi zansami Takawa bayan taro
Ciroma yayi Murmushi yana God
iya ga Allah domin jin burinsa zai cika nan ba dadewa
Shiko Ma,aruf damuwa yashiga yakasa sakat gashi yanajin nauyin mahaifinsa yakasa gaya masa agun
Tsam yatashi yabar gurin yaje can bayan wata bishiyar mangwaro ya hada fuskarsa da bishiyar Khaleesat
nayi masa gizo alokacin datake jawabi tana murmushi
Ji yayi andafa kafadunsa
Yajuyo ahankali Dan ganin ko waye
Yayi mamakin ganin Abban sane yabiyo bayansa
SAHABI ya harde hannaye akirji yana kallon Ma,aruf Wanda ke a ckn dmw
Ma,aruf yakakaro murmushi ya
ce da Abbansa " Abba ya akai kasan nan nataho?
SAHABI yace "Tun tashinka kabar gurin Na fuskanci wani Abu atare dakai kacanza bakamar yadda mukazoba fada mini meya sameka ko bakada lfy ne?
Girgiza kansa ma,aruf yayi yace " Abba bazan boye maka ba Allah n
e yajarabceni ta hanyar sakamin son Khaleesat araina ckn lokaci kankani walh nashiga damuwa ne sbd nasan bazan sameta ba ada kafin naganta naji INA sonta walh banida tsari Na inyi soyayya da Yar gidan masu kudi ko jinin sarauta sbd cika burinka da kadauko
aranka ada can amma hakan Bai yiwuba to damuwa ta kenan Abba tunda nasan burina bazai cikaba kuwa dole indamu
SAHABI yayi murmushi yace "Kada kadamu ma,aruf ina matuqar sonka sbd ka kasance yaro me kishina ka cire wancen batu aranka domin nima Na
cireshi tun aranar Dana Auri mahaifiyarka Na mance komai domin da talaka dame kudi duk Na ubangijine kaima banso mahaifiyarka ta labarta maka labarina ba indai Kuma Khaleesat ce kasa aranka tamkar kasameta tunda inada labarin kakanta Na matuqar kaunarta da
nhaka ta gunsa zanbi Don ganin kasameta nasan bazan sha wahalaba kaima kuma bazakasha wuyartaba sbd ita dinma kamar kai tanada nutsuwa da hankali sannan nasan Takawa Adalin sarkine shi kansa Lamido baida matsala kaidai kayi addu,a akai zansami Takawar anji
ma tunda naji yana sashensa Bai fitoba sbd baki da yake tare dasu suna ganawa
Ma,aruf yaja ajiyar zcy ya ce " nagode Abba Allah yasa nayi SA,a
SAHABI yace "Amin,Allah yashige mana gaba
Suka koma mazaunin su Wanda adaidai alokacin da suka komane Khaleesat t
a Fito itada iyayanta suna yanka CAKE wakar da Adam Zango yayi mata Na tashi agun
Bayan Anwatse Taro SAHABI da iyalansa suna Guest house din da aka saukesu Na Lamido shiko Yarima yana can gidansa da iyalansa dama insunzo
can suke sauka dayake Takawa Bai ka
rbi gidanba ya mallaka ma Yariman
Kamar yadda SAHABI ya qudirta Na Zuwa samin Takawa ayau
Aiko dare nayi yafito yanufi gidan Takawa
Cikin ikon Allah yasami zantawa da Takawa anitse kuma da taimakon Allah saiga Takawa Na murna da wannan batu
Ya nuna amince
warsa yace da SAHABIN yaturo masa Yaron nasa zuwa safe zai hadashi da Khaleesat din
Aiko dai hakan Da dokinsa ma,aruf yaje ga Takawa yakai gaisuwa tareda bayyana kansa amatsayin Wanda keson jikar tasa
Takawa yayi murna da hakan tare da aikawa aka kira ma
sa Khaleesat
Da farin cikinta tafito ta taho gun Dan tsoho me ran karf
e
Data shiga dakin bata kula da Ma,ARUF ba kozama batayib
tahau tsokanar takawan
Kamar yadda tasaba tsokanarsa
" meye ka aika kirana da farar safiyar nan ko sona ne ya motsa maka ga mata
nka can amma kaga yarinya danyen jini son kowa ka like mata
Takawa yahau murmusawa yana fadin "eh naji kigama tsokanarki ki zauna kinutsu kiga mijin danayi mk kona huta da halinki
Ta zauna tana kallon takawan tana fadin " miji kuma?haba saikace wacce tayi
kwant.…
Gyaran muryar da ma,aruf yayi ne yakatseta tayi shiru da sauri tana kallonsa
Wani shock ne yashigeta ta daidaita zamanta bayan kare masa kallo tayi kas!! Dakai jikinta yayi sanyi zuciyarta ta narke Kyansa ne yafara harbota "wow wannan balaraben fa
?ina takawa ya samoshi?saidai yana min kama da Uncle SAHABI toko kanin sane? Tahau tambayar kanta saidai ma,aruf yakatseta da fadin " Sannunki dai Sarauniyar Mata
Takasa masa magana
Takawa yace da ita "wannan da kike gani Dan kawunki SAHABI ne kuma yagani
yana so babu boye boye kada ki watsamini kasa a ido kidaukeshi tamkar Dan Gida kinji ma,aruf sunansa mahaifinsa yasameni da zancen Dansa ma,aruf yarikice da ganinki yana sonki Don haka yanaso
anema musu yardarki dan haka yaya kika gani ? Bazan miki dole b
a jikalle
Tayi shiru kanta akas tana zuba murmushi bazata taba kin amincewa ba domin yatafi da zuciyarta shima
Shiko Ma,aruf addu,a kawai yake azuciyarsa Allah yasa Khaleesat ta amince dashi.....
Saida Takawa yaga yahada kansu adakin nasa kaf daga MAMAH da
FAATU da LAMIDO da Gimbiya Zeenatun da khaleesat din kana yanemi jin ba,asi gun Lamido na Auren da yake so ya qulla atsakanin Khaleesat da Ciroma wanda baiyi shawara dashiba
Lamido yahau sosa keya yana mai kwantar da murya yana fadin "kayi hkr Allah ya h
uci zcyrka naga ai abin duk na gidane Ciroma yana son khaleesat kuma tamkar dan uwanta yake koma ince Dan,uwan natane tunda har kullum yarima dan gida yake tunda Asalin mahaifinsa waziri gidannan kuma bana so a ture bukatunsu dan kar suga annuna musu banba
mci
Takawa yahau gyada kai yana fadin "naji kabadata kafin kaji ta cewata balle kaji ta bakin yarinya Alhalin ni anawa bangaren nima na badata ajiyan nan harma sun fuskanci juna da ita da yaron dama yau nake jira in gaya maka yanzu yaya kenan za,ayi zaka t
ure naka bukatar asa tawa data yarinya kokuma taka za,ayi alhalin naga tun ba,aje koina ba har anfara kai ruwa rana kaida iyalinka ita matar taka bata so ma?
Lamido yadago kai idonsa awaje yacewa Takawa "waye wanda kabatan har suka daidaita kan nasu ?
Taka
wa yace "Ma,aruf ne dan wajen SAHABI kuma na aminta dashi haka yarinya ta amince itama dashi.
Wata ajiyar zcy Gimbiya zeenatu taja abayyane ta nuna farin cikinta harda fadin "masha Allahu Allah ngd maka.
LAMIDO ya kalleta kawai fuska adaure yasake duban kh
aleesat yaga tana zuba murmushi itama amma suna hada idanu tayi saurin gimtse fuska sbd shakkun Daddynta da takeyi dan kada yaga zaqewarta da dokinta akan Ciroman
MAMAH ce tace "kai wannan Abu yayi mana dadi Allah yasa ayi damu
muma mun amince Ma,aruf ai y
arone me mutunci ga kamunkai kuma kowa yasan asalinsu agidannan halinsa sunada mutunta Al,ummah Allah yasa alkairi
FAATU tayi murmushi tace "Amin,Allah yasa ayi damu
G.Zeenatu tace ,Amin,acan kasan makoshinta domin taji ddin ganin yadda surukanta suma suka
ji ddin hadin dama tana kaunar ahalin sahabi sai gashi sun kara haduwa itakam me zasuyi da ahalin yarima?Lamido cikin Sanyin murya yace da Takawa "To amma Allah yaja da kwana kana ganin idan aka ki basu Auren khaleesat yarima bazai yiwa abin fassara ba tun
da nasan halinsa dukda abokinsane Sahabin amma nasan dole saiyaji haushinsu
Takawa yace "sun dade basuji haushin suba duk ma abinda zasuce inajira katuromin su daga ciroma har yariman domin baxai yiwu wannan sun rigashi atsallakesuba sbd sunfi matsayi ackn
gidan ina!
G.Zeenatu tace "Allah yakara nisan kwana inaso kayiwa mahaifin nata magana da babbar murya ya kyaleta yasa mata albarka a ckn lamarin domin nikam naji dadi nakuma amince da abin shima ya amince kawai dan idan ba fada kayi masaba zai riki abin
aransa ko kuma yayi mata dole sbd yana kaunar Yarima aransa shiko tuno abinda suka masa abaya baiyiba.
Murmushi takawa yayi yace "Zeenatu ai tunda na amince anwuce gurin bai isa yayi komaiba
Yakalli Lamido yace "ko kanada ta cewa akai?daga yau bana so inj
i wata magana ta yarima da D'ansa akan zancen Auren khaleesat maganar ma,aruf nake sonji dan haka katuromin yariman da Ciroman kafin su koma
Lamido yace "Naji na amince nima Takawa abinda duk kazartar shi za,ayi tunda naga dukanku kun amince ina ganin d
a Alkairi a ckn Auren nasu insha Allah bazan zamo muku matsala ba zanyiwa Sahabin waya inbasu lokacin da yakamata su turo ayi Auren nasu ko bata gama makarantar ba inyaso ta karasa acan
Khaleesat ta lumshe idanu jin anfaranta mata tabbas tana son ma,aruf
domin ya canza mata tsari da akala na rayuwarta tunda ada can kafin ta sanshi batada burin tayi soyayyya ko Aure sai dogon karatu to amma yanzun da anyi maganar Aurenta wani nishadi ke shigarta to kodon tana son sane?Ta tambayi zcyrta wanda kafin ta samo
amsar tambayar taji Takawa ya sallami kowa na gun angama magana
Tana barin sashin takawa ta garzaya dakinta da sauri tadauko wayarta ta turawa Ciroma sako cewar kamar yadda yasami karbuwa da fada,gurbi da amincewarta haka ma yasamesu duka ackn gidansu
Yay
i farin ck matuqa bayama da aranar Abbansa yayi masa Albishir cewar mahaifin khaleesat yakira yabasu lokacin turawa dan tsaida maganar Aure
*********
A bangaren Yarima da Takawa yakirasu ya zayyane musu komai na maganar Aure dake kan khaleesat da
ma,aruf basu wani nuna masa jin haushinsuba asalima murmushi Yarima yayi yace da takawan "wannan ba abune ai najin zafi ko aji haushi araiba Alhalin duka gida ne ai tunda abinda yayini shi yayi SAHABI dan haka Allah yasanya Alkairi Allah kuma yabaiwa Cirom
an wata
Ciroma har suka baro gurin takawa uffan baiceba sai faman goge hawaye yake kamar yaron goye ashe haka yake da raguwr xcy ko duk son khaleesat ne yashshi kasa jurewa
Momynsa Hindu tayita tausarshi tana ce masa ya shirya suje can familynta kaduna ya
zaba tunda akwai yammata masu kyau kuma