Showing 3001 words to 6000 words out of 57925 words

Chapter 2 - kuyanga complete

masoyina .Ya mike yace mata "maza tashi kije kifara shiri indare yayi kizo muhadu

anan dan muyi sallamar karshe



Tayi murmushi tace " sallamar karshe kamar wanda xan mutu inmunje can



Yayi murmushi yace " ba haka nake nufiba, nasan wataqila da sassafe zaku tafi kinga ai zaifi kyau mukadaita mu dade tare mukara yin wata hirar soyayyar ko

?

Tagyada kai tana dariya



Ya daga mata gira tareda kanne ido yana kallonta



Harya tafi yabar gun bata daina kallon saba tabbas MAHBUB yahadu rashin gata ne da yanayi yasa cikar kamalarsa bata fito ba harsai ankura ido ake hanga atattare dashi



Ta girgiza kai

kawai takara gaba tabar gun tayi dakinsu

Tana shiga Taga Aminiyarta ZULAI



Zulaihat tace "Hhhmmm inata nemanki ai saikuma nahangoki acan lambun soyayya.

KUYANGA



Tayi dariya tareda dukan kafadar Zulai tace "harkin sakawa gurin zaman namu lambun soyayya lall

ai Zulaihat ke "yar sa ido ce.



"Ba wani sa,ido gaskiyace ba lambun soyayyar bane?



"Eh bashi bane, to ai ba soyayyar akeba.



Cewar *KUYANGA* Tana dariya

Zulaihat tace "kifadawa keya yarinya kowa yafahimceku ingaya miki duk wanda yaga yanda kuke tabbas zaigan

o ckn mintina batareda yasha wuya ba."Hhhmmm to inma soyayyar akeyi saime? Ko bamu daceba.



Zulai takama baki tace "ho! Ni na isa ince baku daceba aji haushina to walh bari kiji kundace da MAHBUB tamkar danjunanku akayoku ina kuma Son tarayyarku.



Zama *KUY

ANGA* Tayi kusa da ita tace " Zulai gobe zanketa hazo fa.Da sauri Zulaihat takalleta da alamar tambaya tace "hazo

kuma?kamar yaya?Nan Ta zayyano mata komai nagame da Rakiyar da Zatai wa Yarima Turai

Zulaihat tace "wayyo Allah na inama ni aka zaba.KUYANGA T

ace "tabdijan !kenan har wani son tarayya kike yi da Yarima?mutumin dakowa yasan halinsa marasa kyau. To walh ni ckn bakin ciki nake ahalin yanzu da har aka zabeni



Zulai tace "Dan dai zakiyiwa MAHBUB nisa ne amma aikinsan zaki huta zakuma kisami hutu da Ai

kin gidannan ZEENATU kifa tuna mubayine bayinma kaskantattu wadanda



ba,a san inda iyayanmu sukeba ko suna raye?ko sun mace Allah shiyasani mudai muntsinci kanmune agidan nan Dan Allah kikwantar da hankalinki inkinje domin Allah ne yazabeki domin kihuta ked

ai kiyi biyayya dama ke me biyayyarce kowa yasani bakida surutu magana bata dame kiba inba sabo kikayi da mutum ba basawa ba hanawa dan haka ki ajiye soyayyar MAHBUB anan zuwa sanda zaki dawo kwacigaba



KUYANGA Tace "to inma ban ajiyeba yazanyi bayan askiya

zo gaban goshi gobe nefa zantafin dole inyi hkr da komai dama saiyau yabayyana min abinda ke ransa



Zulai tace "hhhmmm keda bakida gano abu da wuri aisaiyau kika ji kika gane amma ai kowa yagane manufarku tabbas muna muku fatan Alkairi kedashi.

KUYANGA



Tace

"mungode.

Nan KUYANGA Tahau shirya kayanta ckn wani Dan akwatin karfe me kyau dashi tana Ninka kaya tana sakawa tana ayyanota A turai shin ko wane Zama zasuyi insunje……… ???

Da Sassafe tagama kintsawa misalin Bakwai na safiya Aka aiko kiranta daga Fulani



Tana shiga Sashin Fulanin ta tararta atsaye Yarima na kusa da ita da akwatinsa babba guda daya da alamar zai dade din domin fam yacika akwatin da duk abinda yasan zai bukata duk da acan gidan nasa akwai kayansa na sawa UMMAH Ta daka masa Yaji ta

sa anyo ma

sa dambun nama ta soya masa gyada me gishiri duk abinda tasan dai yana matuqar So ta tanadar masa taxuba masa ckn Akwatin

Yana ganin *KUYANGA* Da akwatin yahau kallonta fuska ba fara,a yace "ke wannan akwatin irin na mutanen da kumafa? Kina nufin dashi zak

i bini? Kinsan kuwa Turai ?Bafa Me dile bace, maza jeki canzoshi kokuma kitafi ba kaya inmunje xan nasiya miki wasu kawai



UMMAH tayi murmushi tace "Yi mata hakuri Yarima ta canzo kasan sai ahankali kayi mata uzuri taje ta canzo kayan kokuma inshiga innema

mata cikin akwatina na



Yahau girgiza kai yana duba agogon hannunsa

"Barshi UMMAH saura mintina Jirginmu yatashi saima munyi wuta ahanyar zuwa Airport din don karmu makara



Yakalli KUYANGA



Yace "ke ajiye kayanki anan muje da najikinki inmunje zansai miki w

asu kiringa sanyawa.



C

i

k

i

n ladabi tace "to shikenan.

Ta ajiye akwatin karfen nata agefe tabi bayansa UMMAH tana musu Addu,u,a da fatan Alkairi



Wasu bayi maza ne suka kai masa akwatin nasa har ckn mota aka zura a boot KUYANGA



Ta shige gidan baya



Motar natafiya zata fuce agidan Sarautar saitaji wani iri aranta tabbas zatayi kewar MAHBUB yau ranar zata zamo mata ranar bakin ciki tunda ta taso kullum suna tare gashi yau zasuyiwa juna nisa kamar ance ta dago kanta kuwa tana dagowa takalli bayanta sait

a hangoshi ta glass yana dago mata hannu



Ta zura hannunta tahau daga masa itama



Ashe Yarima yana hangosu ta mirro amma baiyi maganaba yai shiru



a Airport kuwa da sukaje Dakyar ta iya daga kafa tahau matattakalar jirgi saida ta rintse idonta Jirine ma yaso

kadata Allah yaso ya kula yai saurin rikota tayo luuu jikinsa yatarota yamannata ajikinsa yahau da ita ahankali



Yasan arina tunda yasan ba taba hawa tayiba



Koda suka shiga ckn jirgi akusa da juna suka zauna



Kujerarsa na kusa da tata



Idonta akasa bata iya

hada ido dashi don kunyar abinda yafaru da kuma biyayya

Yakalleta yadauke kai yana so yai mata magana amma yarasa me zaice mata don baya son tana jin kunyar nan tasa shikam tana burgeshi amma baya son kunya shi faranse ne wayyayye



Gani yake duk kauyanci

n nan da zatayi masa bazasu shiryaba domin saiya wayarta kada tabashi kunya irin nayau



Da aka kawo musu abinsha kin dauka tayi saida yadaka mata tsawa

"Ke Dauki mana meye na kunyar!Tasa hannu ahankali tadauki lemon taja ta rike takasa budewa



Yana kallonta

tagefe taki budewa kanta akas!



Saida yashanye kana yakalleta yace "kawo inbude miki.

Ta mika masa ahankali



Yabude mata na gongwanine me gas



Taringasha ahankali kusan awa guda kafin tagama



Anyi rabin tafiya Tafara bacci takwanto da kanta kan hannun kujera

yatsura mata idanu yana kallon kyakykyawar fuskarta da dan bakinta yaji kamar yakai hannunsa yashafata saidai yana gudun kada tafarka



Can bacci yai mata dadi saiga kanta ajikinsa



Yarasa yazaiyi da ita saboda mutane nakusa dasu suna kallonsu



Haka yabasar

bai motsaba gudun kada ta farka takasa komawa

*******

Koda suka Sauka a England Kaitsaye suka hau mota ta haya har gidansa Tamfatsetsen gidane da maimartaba yasiya don kawai insunzo karatu suzo suzauna ackn sa



Daki guda mekyau da tsari yakaita yace mata nanne inda zata ringa kwana



Dayake kayan jikinta riga da zanine tasanya hijabinta hannunta rike da carbi



Tazauna zagwade abakin gado tana so tayi sallah gashi bata san yazatayiba nafarko bata san inane gabas ba

gashi Bandakin yawuce tunaninta batasan yanda zata sarrafa ruwa yazubo ba gashi ba agogo adakin



Data gaji da zama saita futo falon domin

tambayarsa



Ta dade afalon azaune bayanan yana ciki tajiyoshi yafito daga wanka



Tananan zaune harya kintsa yafito



Yakal

leta yace "Ya kika baro dakin kika dawo nananan Qalau ko?



Tace "Dama, Alwala zanyi inyi Sallah to bansan yazanyi ruwa yaxubo ba kuma bansan ina zan kalla ba gashi lokaci nakeson gani

Ya koma ciki yadauko mata agogon bango yadawo yace mata "Taho muje.Ta b

iyoshi abaya har dakin da yace natane



Suna shiga ya ajiye mata agogon Akan mirro me lado ladone xata gane shi



Yashige bandakin yana kiranta



Tabi bayansa yaringa nuna mata yanda zata kunna komai takashe ckn Sauki



Da yanda zatayi wanka da shaya dakuma yanda

intayi kashi zatayi fuloshin da duk abinda yasan dai zai gagareta



Saida ya tabbatar tagane komai kana suka dawo dakin yanuna mata Gabas sannan yace mata inta idar ta jirashi xaije yasiyo musu abinci yadawo



Kafin yadawo kuwa tagama komai don har wanka itama

ta sallo ta maida kayan jikinta taxauna ta takure agado tana jiransa don yunwa takeji



Daya dawo yashigo yakawo mata abincin na take away sannan yabata wata ledar kaya yace "Ga kayan sawa nan kala biyar na Siyo miki kafin nakaro miki wasu gaba



Takarba da b

iyayya tana godiya

Daya fita yabarta tacinye abincin tas tana santi kunnanta kamar yacire



Tayi mamakin ma data iya cin wannan kalar abinci domin a ido dai yaburgeta dama gashi abaka ma gwanin dadi bata taba ganin irinsa ko a hoto ba



Ta wanko hannun

tasha ruwa sannan tazo ga Ledar ta zaxxage kayan tana daddagasu daya bayan daya tana mamaki da yatsina fuska domin kayan basuyi mataba



Asalima tayi tsammanin ko canzan leda sukayi da wani domin kayan bana sawar "yar musulmi bane



Itakam ko da kudi bazata ta

ba sasu ba rigunan "yan bigil suke kanana wanda in an saka zasu damewa mutum jiki



Ga Wanduna pensil ga "yan

gajerun wanduna sai siket masu roba iya cinya da riguna marasa hannun harda bes tashan iska kayan sunyi kyau

Ga masu sawa Amma

😉😊

Ta maidasu cikin

ledarsu tana mamakin wannan kaya ai baxata taba iya sasuba haba aiko batada kunya wannan kayan sai a gidan mijinta yaushe



Sai bayan wasu awanni yashigo mata don ganin ko qalau take



Yana zuwa yaga kayan akusa da ita yahau tambayarta"Baki bude kayan bane?nak

ine fa nasiyo mk yakamata kigwada ma ingani don inga wanda sukafi miki daidai sbd xankoma siya miki irinsu nan gaba.Tace aranta "Aiki game k'areka.

Afili tace "kayi hkr nagansu baxan iya Sawa bane sunyi kanana dayawa.Yahade rai baya son kauyanci da Raini

fa

Yace "akan wane dalili tokisani nanba gida bane baxakiyi kauyan cinnan nakiba dolene kisaka su don awannan garin baruwan wani da wata dankin saka bame kallonki balle yaga laifinki kuma bazaki taba samini wadannan riga da zanin naku nagargajiya ba dan ha

ka maza kisaka su ingani nabaki minti biyar ina jiranki afalo



Yana gama fadin hakan yajuya yafuce

Wani qululun bakin cikine yatsaye axcyr KUYANGA



TABBAS tun daga yau tafara nadamar xuwa Turai lallai inko haka zata ringa shigar kayan arna gara bataxoba Gara

kuma taita zama dana jikinta

Tasaka kayan agaba tana kallonsu data kalli agogo taga saura minti biyu lokacin daya bata yacika saitayi saurin tashi ta janyo ledar taciro wata riga me karamin hannu tacire ta jikinta tasaka dakyar



Sannan ta sille zanin tasa

ka wani dogon wando



Bata iya cire dankwalin kayan ba tabarshi akan nata don kada yaga gashinta



Takalli kanta a madubi



Ai dasauri ta rintse idonta tana fadin "innalillahi wa inna ilaihir rajiun.

Yanzu haka xanje gaban namiji?yanzu haka zanje gareshi yaganni

n nashig uku yau naga takaina

🙆🏼

meye mafita ………………?

KUYANGA Tak'ara kallon kanta a madubi taga agaskiya bazata iya futa gaban Yarima ahakaba ai taxama mara kunya kenan inhar yaganta ahakan..."bashi yabaki umarni daki sakaba " bashi yakawo miki don ki s

akaba? Wata zuciyarta tace mata



Azancen gaskiya kayan sun mata kyau domin wandon yamatseta tsam !dam! Yafito mata da shap sosai abin gwanin burgewa dai



Ga rigar ta kamata tamkar ajikinta aka kirkireta dama ita ba ma,abociyar saka bra ba saiga nonuwa tsaye

tsar ! Me sifar kan tasa ga nipple nan tsir ya nuna kansa

Ita kanta abin bai mata tsari ba balle kyangani domin sifarta tafito tamkar komai awaje yake



To yata iya inhar taki futa taje gun nasa zaizamo hakan tamkar ta bujirewa maganar sane sannan umarni yab

ata ba zab'i ba



Kuma ita din akan bin umarninsa take zaune sannan babu musu ko k'iwa atsakaninsu akullum ita din baiwa ce makaskanciya agunsa KUYANGA me hidimta masa

Ta tuno kalaman mahaifiyarsa da take ce mata "DUK ABINDA YA UMARCEKI DAKIYI KIYI MASA DON

KI FARANTA MASA KECE MEYI MASA KOMAI ME KULA DA KOMAI NASA



Saikuma ta tuno da kalaman masoyinta MAHBUB da yake ce mata "KADA KIBARI AZALINCEKI KADA KIBARI ACUCEKI SBD KINA AMATSAYIN BAIWA KADA KIYI ABINDA BAI DACEBA ACKN BIYAYYA.



ta rintse idanu tana kwal

la tana fadin "MAHBUB kayi hkr gashi anfara, zankuma karya maka doka Zanyi biyayya ga abinda bai daceba zanbi umarnin uban dakina.



Tana gama fadin hakan tafuce gurinsa

Yana zaune afalon yadora kafa daya kan daya yana latsa waya



Tun daga nesa yakura mata id

anu itako kanta na kasa

Saida ta isa dab dashi tadago kanta taga ashe shid'in ita yake kallo saiTaji wata kunya ta mamayeta



Yai saurin kawar da ganinsa daga kanta yace "Very nice sunyi mk kayan daga yau sune Kayan sawarki kada nakara ganinki da zani dom

in nanba kauye bane ina mu,amula da wayayyu bazanso suga dawa nake tareba inhar ba kin kile ba tunda duk bakon danayi saikinzo kinyi masa hidima



Ta gyada kai kawai



Yace "oya muje kicin na nunnuna miki kayan amfanin da zaki ringayi akullum.Ya wuce gaba tabi

bayansa ad'arare



Yaringa nuna mata abubuwa komai har gas yanuna mata yanda zatayi amfani dashi domin acan gidan sarauta Manyan bayi ke girki ba yaransuba



Balle su iya komai su k'ananan Bayi saisun kai munzalin Aure ake fara Trenasu



Saida yaga ta

kwashe akwanyarta na wasu abubuwan kana yace suje su zaga gidan domin can ma akwai abinda zai nunnuna matan



Tana gaba yana bayanta yana karewa mazaunanta kallo



Yawu yake had'iya kawai domin yasha Mamaki aransa yarinyar ta da ita amma komai yaji Yakaita gur

in shukoki don yace ita yakeso taringa basu ruwa kana yakaita gaiding nanma yace hurumin tane

Cai !!

🙆🏼

ashe zaki wahala KUYANGA

Yakaita yanunata ga mai gadinsa domin su san juna sosai tunda ita zata dawo girkin gidan zata ringa bashi shima



Au ainaxaci g

adinma ita zatayi

Kwanan KUYANGA Biyar agidan takwashe komai akwakwalwarta ta iya kunna gas tayi masa sassaukan girki takan mikawa me gadi intayi



Girkinsa bai wuce indomie Cuscus da suyar dankali da doya da kwai sai sauran abubuwan da basuda nauyi masu S

aukin yi



D'an wahala shiyasa bakada k'iba iyakarta dakinta in yana falo bata yarda tafito inba abinci zata kai masaba shima a kunyace take zuwa sbd kare mata kallo yakeyi duk kayan kuma data sanya saiya furta cewar sun mata kyau



Magana me

tsayi bata hada s

u to me zatace masa ? Bayaga ina kwana ina wuni sai tambayar wani abun kuma

Cikin Sati biyu yazamto tafara sabo da komai hatta kayan datake sawa matsatstsu yazame mata jiki tasaba dasu tunda yakaro mata wasu yakawo mata dayawa



Tun tana kunya inta sakasu h

arta daina

Yakawo mata manshawa masu kyau da man wanke kai da sabulai nagyaran fata dai



Tana tsafta sosai tana gyara kanta dayake tanada tsahon gashi da cika saidai kullum yasha gyara ko tayi masa manyan kalba ta bazo jelar kalbar baya aiko takanyi balain

kyau dama ga fuska kamar ba india sosai kyanta yanata bayyana don hutu yanata shigarta ba koina take zuwa ba kullum bacci daga dakinta sai kicin sai falo



Sai intafuta kaiwa me gadi abinci ko aikin farfajiya



Zaman gidan yafara damunta to amma bayanda zata

yi tunda baice tazo tafuta wajenba aibaxata iya futa batare da izinin saba



Yakan futa tun dare sai tsakar dare yadawo tarasa wane aikine haka kamar na barayi

Hhhh bakisan club yake zuwa ba kenan to zauna wataran zaki sani



wata ranar Lahadi tana Daki akwanc

e tayi rub daciki tanata tunanin masoyinta MAHBUB Tasan akoina yake yanzun hakan yananan da kewarta



Kawai taji yashigo mata ba sallama



Ta tashi da sauri tace "Sannu dashigowa akwai abinda kake bukatane?



Yaja yatsaya yaruke murkar kofa yace "kitaso maza ki

dafa abinci ga bakina nan zuwa gidannan "yan Nigeriane amma anan suke karatu Abokina ne sosai Shi d'in Jinin Sarautane kitsaya kinitsu kiyi abinci me dadi bawai bamuda inda zamu ciyo bane akwai hotels kawai dai yafison abincin gidane nasan sa sarai C

i

k

i

n

ladabi kai akasa tace "to angama.Yajuya yafuta yana karewa "yar shimin dake jikinta kallo wanda agaban rigar aka rubuta *HOT KISS!* Da manyan Harufa



adaidai lokacin da bak'in nasa sukazo

adaidai lokacin Allah yabata sa,a tagama komai



Har juice ta hada na m

ango da Banana da kayan fruit dai



dayake yakawo komai yasaka afurji



Itako akwai basirar iya yin komai wani abunma ba koya tayiba datayi nazari aranta tsaf zata hada

Tab kaga KUYANGA "YAR Baiwa



ho Allah yabamu yataki zeenatu



Tayi musu sallama falon yarima

ne sai bak'in su biyu kawai kallo suke suna hira



Bakin suka bita da kallo



Ta dire akan table tareda durkusawa tagaidasu



Yarima yana kallon yanda suketa kallont

a

Saida takoma ciki Yarima yakaiwa nakusa dashi duka yana fadin "kai SAHABI kashiga hankalinka w

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login