Showing 21001 words to 24000 words out of 57925 words

Chapter 8 - kuyanga complete

yarinyar ckn kwana daya



Da sauri jakadiya tace " angama uwar dakina.



UMMAH takawo kudi tabata jakadiya tafuce da sauri

Amma ka

fin ta tafi gurin matsafiyar tasu dake bayan gari saida tafaki ido tashige Sashin MAMAH Takai musu Gulmar wai ga Yarima can yarikicewa Mahaifiyarsa waishikam yanzun *KUYANGA* Yakeso kuma ya amince cikin jikinta nasane



FAATU DA MAMAH sunyi mamakin wannan A

bu sunkuma Daukeshi arainin hankali yariman yazo dashi sunsan kuma TAKAWA bazai daukaba



Yo muma ba dauka zamuyi ba

Muje zuwa

JAKADIYA tana isa cikin Dajin tayita shiga cikin Ko tsoro babu atare da ita haka har tazo gindin wani tsauni ta haye daf !daf

!!daf!!! Ta nufi wata babbar bishiyar Kuka dake kan katon Dutsen



Tana isa ga bishiyar saita cire takalmanta ta tsaya gaban bishiyar tana fadin "Gafaranku dai manya da kanana na fadar GOGAL ga jaririya tazo tazo Neman taimako da cin Albarkaci ayi min

iso gurin Hakima mandiya shugabar matsafa Wani kuka taji yana tashi na muryoyin yara daga ckn bishiyar taitaji harna tsahon minti talatin can kuma taji shiru sai kuma ga amsa kuwwar Babbar murya tana fadin

" SANNUNKI DA ZUWA HATSABIBIYAR JAKADIYA GAMAND

I ME HADA WANDA TASO

Jakadiya ta hadiyi yawu domin kirarin nan bai mataba tasaba yi matashi,"Barkanki da isowa GOGAL



Cewar Jakadiya

GOGAL da ba,a ganinta saijin muryarta ta jikin bishiyar tace da jakadiya

"NAji zuwanki angayamin tunkina afarkon daji nasa

n meke tafe Uwar Dakinki ta aikoki akan Acirewa D'anta son da yakewa *KUYANGA* Daga zuciyar sa ko?



Jakadiya tace " E kwarai hakan yake.

Jakadiya taci gaba da cewa "Hakan data tsara nikuma incanza salon abun yazamo amaimakon ancire masa son yarinyar saidai

ma akara masa don ya axabtu sosai



Yakasa sakat yashiga damuwa akanta sakamakon yanda yasaka yarinyar adamuwa



Wata bunsurar dariya aka sheke da ita dg jikin bishiyar kukar



Daga can kuma akace da jakadiya " ko baki fadaba hakan za,ayi domin Baxan iya c

ire wannan soyayyar dake ransaba na duba naga ajiyar Allah ce ban isa in girgizata ba Dan haka zankara da Dora aikinki da kika bukata domin nima ayaune zanrama abinda YARIMA yataba yiwa Jikana yafita rangadi suka hadu ahanya YARIMA yabuge minshi da do

ki yafadi ko kulaminshi YARIMA baiyiba harya suma agun



Jakadiya tahau gyada kanta

Tana mamakin jin wannan labari na GOGAL duk da tasan zai aikata din Jakadiya tahau godiya tareda ajiye kudin da uwar dakinta tabata agindin bishiyar ta mike da niyyar tafiy

a



Sai taji ana mata magana da muryar tsohuwa ta jikin bishiyar

"Kema kibi lamuranki na gidan nan a sannu domin a irin zaqewar da kikeyi wataran zaki girbi kashinki ahannu

domin akwai abinda zaki aikata zaija miki babban aiki da kuma danasani HAHAHAHA

A

ka rufe da katuwar dariya



Jakadiya na kyarma tace " Ataimaka agayamin ko mene wannan Abu da zaijamin danasani don inkiyaye



Dariyar dai akaci gaba dayi mata babu wani Karin bayani



Tana kallo kudin data ajiye yabace sundauke



Difff! Taji anmata tasan bak

uma xasu karace mata kanxil ba shiyasa ta tafi da baya kamar yadda ta saba

*******

Yarima Yana kwance akan makeken Gadonsa yanata juyi yakasa controlling din kansa akan soyayyar *KUYANGA* Da take azabtar dashi arai



Hotonta ke masa gixo alokacin dayake ka

nta a time din suna Turai



Tabbas Yanda takeda tarin baiwa bazai iya barin taba saiyayi yanda yayi ya mallaketa baxai taba barin LAMIDO ya Aure taba



Can kuma saiya mike da sauri ayau saiya ganta kota halin kakane koda zai karya billensa yashiga ckn gi

dan bayin bazaiji wani Abu aransaba Sontane yaja



Yazira kaya ajikinsa dama dagashi sai gajeran wando da singilet



Yafito farfajiyar gidan yatsaya yana karewa kowa dake wucewa kallo duk Wanda zai wuce ta kusa dashi saiya kawo masa gaisuwa



Da ka kawai yak

e amsawa



Sarkin gida ya hango agurin ajiyar dokuna yana baiwa wani farin doki da LAMIDO kefuta dashi abinci

Matsawa yayi kusa da Sarkin gidan tareda kwalla masa kira



Da sauri yabar abinda yakeyi yataho gurin Yariman



Ya mika gaisuwa tareda tsayawa ckn

ladabi agefen yarima yanajiran abinda zaice masa



Yarima yace "Sarkin gida Inaso kaje ka kiramin *KUYANGA* Zeenatu



Sarkin gida yace " Tana tareda MAHBUB acan bayan Gamji da suka saba zama Yarima yadaka masa tsawa yace

"To intana tareda wani bazatazo ba ko

Yaya?shi wanin yafinine ?mijin tane ko waye dinta?

Sarkin gida yahau fadin " kayi hkr ba nufina kenan ba sanar maka nayi dai bata gida agarceni bari aje can akirata



Yatafi da sauri inda yasan zaisametan



Yarima yahau cizar yatsa jin wai tana can tareda

MAHBUB tabbas dole yadau mataki akan wannan Bawan dazai kawo masa tsaiko



Yananan har lokacin da Sarkin gida yadawo tareda ita tana biye dashi sanye take da zurmemen hijab harkasa



Yaringa kare mata kallo na yanda take tafiya anutse kanta akasa



Gabantane

yake faduwa domin batasan dame yazo mataba



Tana ZUWA gareshi tagaidashi tareda tsayawa gefe kanta akas



Yana murmushi yace

"Zeenatu dago kai kikalleni gani agabanki da kokon barata Nazo Neman yafiyar kin



Akan laifin dana aikata miki nayi nadama nakuma

karbi cikin jikinki domin tabbas D'ana ne ko "yata zaki Haifa jininane inason abuna ki kwantar da hankalinki kisaki kowa ki kamani domin rufuwar asirinki

Ta dago da sauri takalleshi ido cikin ido ayau Allah yadauke mata shakkarsa tace masa " Ai asirina y

agama rufuwa atun lokacin daka budeshi Allah yanufi Dan uwanka da rufeshi kuma abinda yaimin bazan taba mantawa dashiba bakuma zankishiba na aminta shi zan Aura....dasauri yakatseta



"Kina nufin kice Kinason LAMIDO?



Ta girgiza kanta

" zan Auri LAMIDO sbd

halaccinsa agareni da muhimmancinsa aguna da gun abinda zan Haifa sannan bazan bijireba INA ganin kima da daraja ta me martaba amma SO d'aya tak! MAHBUB nabaiwa shi

Kamar ta watsa masa wuta amakoshi yaji jinta Ambaci MAHBUB take so



Tabbas

Zeenatu tacanxa yaushe tayi baki haka yaushe tasan tagaya masa magana tsararo babu

taunawa tabbas babu musu MAHBUB ne zai kintsa mata komai akansa tunda suna tare yasan gunsa ta taho kuma saiyayi maganinsa



Yadubeta duba na tsanaki yace "Nayi alqawarin sa

ina raba zuciyarki da soyayyar bawa Mara amfani

Tace " agunkane baida amfani amma aguna yana da amfani



Tana gama fadin haka tajuya tatafi abinta



Ayanxu ji take komai zata iya gaya masa tunda yazubda mutuncinsa agunta

Yadade tsaye yana kallonta harta qule z

ancenta na masa yawo azuci kamar tadaba masa wuqa haka yaji tabbas ayau ba sai gobe zaiyi maganin MAHBUB shine sila nakomai datayi masa ayau



Kafin yabar gurin saida ya yanke shawarar abinda zaiyiwa MAHBUB



wasu fadawa Yasamu guda biyu dasuke girmamashi

ya yafito su suka taho da sauri suna zuwa yace musu



"Wani aiki zanbaku me tattare da hatsari amma zaku samu abin alheri me tsoka



Sukai farat sukace " indai zamu samu matsayi agunka da kuma abin duniya kowane irine zamuyi



Yarima yaji dadi yagyara tsaiwa

yace "nasan zaku iya daganinku anga jarumai Wani bawa nakeso kukashe adaren yau…



Yayi shiru yana so yaga wane action zasuyi ko zasu firgita saiyaga sabanin hakan ko gezau basuyiba da alamun zasu iya abinda yafi hakanma dama da ganinsu tantiraine



Yaci gab

a dafadin " dazarar kunkasheshi zanbaku gida ackn gari zanbaku kudi har naira Miliyan daya duk kuraba amma kuxama masu sirri so nake dasafe atashi da kukan mutuwarsa



Sukace atare "angama ranka yadade.

Yace " kutafi kujira zuwa dare da zaku aikata hak

an saikunyi natabbatar zanbaku abinda na alqawarta muku



Sukace "to shikenan Ranka yadade.



Suka tafi shima yajuya yashige ciki

Itama Jakadiya dataji komai akan kunnenta tajuya koma inda tafuto tana gyada kai mamakin abin fal ranta lallai Yarima yazama Ta

kaddari acikin gidan Sarki......

Kwana Jakadiya tayi tana Tunanin abinda kunnenta yajiye mata akan Abinda YARIMA yasa ayiwa MAHBUB tabbas indai suka aikata hakan Sai ta tona asirinsu



Da gaggawa wata zuciyar ta kwabeta

"Ke kinsan ko abinda kk fada?yarima

n zaki tonawa asiri toki tabbatar indai kika fada sunanki matacciya kema kokuma korarriya a gidan Sarki domin yarima da mahaifiyarsa babarinki zasuyiba



Ta tuno yanda mahaifiyarsa keji dashi da sangartashi da gudun Bacin ransaTa tuno rashin mutuncin Yarim

an

Sannan ta tuno Yanda za.aita bibiyarta ana Neman cikakkiyar sheda daga gareta dazarar ta tona asiri domin dolene saita kawo shaida inko bata kawoba za,a hukunta akuma koreta agidan dama UMMAH ce ta daukaketa agidan



Dataga jan bakinta tayi shiru

yafiye mata alkairi saitaja komai tasa agefe Dan yafiye mata kwanciyar hankali

********

Tashin hankali Wanda ba,asa masa rana domin abangaren bayi suntashi dashi



*KUYANGA* Da zulaihat suna kwance da Sassafe ihun da suka ringa jiyowa da koke koke agidan

shiya tashesu afurgice



Zulaihat tace da ita " munshiga uku wannan ihun kuwa na lafiyane.*KUYANGA* Tace "Ba lafiyaba gaskiya tashi muleko



Suna futowa bakin kofarsu sai suka hango dandazon mutane Asashin maza

Suntaru gefensu kuma mata ne tsoffi da yaran

mata sunata kuka



Zulaihat ta yafito wata yarinya Laminde da batafi shekara gomaba yar Aiken Uztaz MAHBUB

Laminde tana goge hawaye ta iso garesu



Zulaihat tace mata " Ke laminde meyake faruwa agidanne?



Cikin kuka laminde tace "Tashi kawai akayi akaga wai

UZTAZ ya mutu kuma ance kasheshi akayi da fullo....

" me!? Afirgice *KUYANGA* ta riketa tana tambayarta "waye yakashemin MAHBUB wayyo nashiga uku in Zeenatu

Ta Dora hannu aka tana kuka

Zulaihat da jikinta yayi sanyi takamo Zeenatu ajikinta tana fadin



"

kada kidaga hankalinki muje mutabbatar dai



Tajata suka karasa gurin tsoffin



Lantana wata sa,arsu ta matso da sauri garesu tana kuka tana fadin "shikenan Ankashe uztaz Ya mutu ancucemu munyi rashin mallam



Zulaihat ta kara yadda sai kuka itama



Wata tsohuw

a Iya Sha,awa mutuniyar Kirki tana son *KUYANGAR* ta maso da sauri gunsu ta janyo *KUYANGA* da taketa rufza kuka hannu aka tace mata " yi shiru Zeenatu kiyi masa addu,a Wanda kuma duk yayi wannan Abun Allah yatoni asirinsa



Zulaihat tace "wai iya me akayi

masane?



Iya sha,awa tace " antashi dai anganshi yana kwance ayashe akasan katifarsa ga filo akan fuskarsa

Awuyansa da alamar shaqeshi akayi yajigata ma kafin sukasheshin ba,a gano kosuwaye suka aikataba



Kuka sosai suka ringayi dagama jin wannan mummunan

labarin

Kaf kafatanin gidan sarki sun shiga tu,ajjibun abun



Banda wadanda suka aikata da yarima



Itako jakadiya ackn bakin ciki ta wuni



Gashidai tasan kosu waye amma badamar bayyanawa tana tsoro



Taji mutuwar MAHBUB sosai har kuka tayi itama



Yo muma mun

ji mutuwarsa

😭

fans kutaho muje gaisuwa gidan sarki

Matan Sarki kaf sun halacci bangaren Bayi domin yi musu gaisuwa Mai martaba yazo gun ansallaci mamaci amma sai yakoma fada akaci gaba da karbar gaisuwa acan



Suma bangaren bayi mata a bangaren Tsoffin

gidan

suka taru ake zaman makokin *KUYANGA* Tafi kowa agun damuwa domin jiyan sun Dade tare suna hira me dadi yana bata shawara na yanda zata zauna da rayuwarta tayi kyau inta Auri LAMIDO



sosai yaita kwantar mata da hankali yana gaya mata irin son da ya

ke mata

Ko zuwa kiran da yariman yai mata suna taren shiya takura mata saida taje ajiyan



Kwana tayi baci basha saida iya sha,awa ta takura mat

a

Sai aranar sadakar ukun MAHBUB sannan LAMIDO yazo bangaren Bayi ya aika tazo domin yai mata gaisuwa



Ta iso c

ikin hijab har kasa kanta akasa

Tagaidashi ckn sanyin murya



Idonsa akan fuskarta yana murmushi ya amsa tareda yi mata gaisuwa



Ta amsa tana yi masa godiya

Yace "Allah yajikansa yabaku hakuri da juriyar rashinsa



Ta dago da kanta takalleshi tace " Amin ngd

Yana murmushi yace "bakomai yiwa Kaine bari nakoma.



Yakawo kudi masu yawa yamika mata

" gashi kibada Sadaka

Takarba tana fadin "Allah yakarba.

Tajuya ta tafi tana zancen zuci " wato shi wannan nafahimci yana matuqar son yaga ya aikata aikin lada.

Tayi murmushi "yanada hali me kyau ga yawan fara,a

*KUYANGA* kodai kin yaba ne...??

*********

Sai ranar sadakar bakwai Yarima yazo mata shikuma Gaisu

wa



Fuskarta babu annuri tafuto gurinsa tagaidashi tayi shiru agefe guda kanta akasa

Yace mata " nasan kina cikin damuwa na rashin masoyi to amma yakamata ace kinsa hkr aranki domin Allah yafimu sonsa shiyasa yakarbi kayansa



Tayi masa banza don ba burge

ta kalaminsa yayiba



Yaci gaba da fadin "duk kinrame

Zeenatu Saikace Wanda mijinta yarasu



Bata dago takalleshiba balle tabashi amsa



Dayaga batada niyyar magana saiyayi mata sallama yatafi kawai yanajin farin ciki aransa



Yasan gaba dole zata soshi inta zam

a mallakinsa domin Saiya kauda LAMIDO shima inyaso ahakura abashi ita don bazai juri yaga tazama mallakin waniba alhalin ayanzu yana mata mugun so



Bayan wata biyar Cikin *KUYANGA* yana wata Takwas alokacin Yarima yazo mata da Kudi wai tayi sayayya na kay

an jarirai



Taso taki karba saikuma taga dacewar karbar dazatayi domin Allah ma take godewa da har Ya karkato da hankalin yariman kan cikin tunda wasu sunshiga zarginta afarko tunda yariman yace bacikinsa bane ake tunanin cikin wani n



YARIMA yazo da Sati

biyu *KUYANGA* ta haihu ta haifo D'anta Zankadede kyakykyawa Wanda tsananin kyansa yasa aketa zuzutashi agidan tamkar balarabe



Saidai kuma yadauko wasu abubuwan na yarima afuskarsa kamar kwayar idonsa da habarsa sannan wani ikon Allah saiga cindo ahannun

sa na hagu



Haka yarima yanada wannan cindo ahannun hagu

Wannan shiya kara tabbatarwa Al,ummar gidan lallai wannan yaro mallakin Yariman jinin sane ba haufi



Mai martaba ya Dade yana kallon Yaro



Yatabbatar da wasu abubuwan na yarima ajikin Yaron saiyaga

tamkar yarima yana Yaro

Wata kaunar yaronce taringa shigar Sarki yaji inama tahanyar sunna aka haifoshi



Koda yakebe shikadai kuka yaringayi waiyau shine da jikan dayazo bata hanyar Aureba yarima yacuceshi yabata masa suna



Yarima baidauko halinsa ba baiy

i shashanci ba yana saurayi Komai nasa da nutsuwa da kamun kai yayishi harsaida yayi Aure yasan mace to amma gashi Allah yajarabceshi da

abubuwan tir agidansa



Munjajanta maka Sarki Abdallah Abin arxiki FAATU da MAMAH suka hada sosai na kayan jariri ak

a kaiwa *KUYANGA*

Jakadiya tabazama ta gayowa UMMAH



Fulani tahau gyada kai tana fadin "munafukai nagama ganosu sunayine badan Allah ba saidon Neman suna da kuma Neman duniya agun Sarki



Kinaji ko Jakadiya nima zanhada kayan inbaki kikai badan Allah zanyi

ba saidan wadancan munafukan Dan aga banyiba sukayi tunda za.ace niya kamata nayi ko



To zan yi nima Wanda yafi nasuma yawa sannan ke zanbawa kikai harkudi zandora amma inaso kiyawaita kai kafa don hidimtawa mejego dakuma duba yaro inaso kinuna musu so

yayya tayanda inkin kashe Yaron baza,a zargekiba



Jakadiya tahau gyada kai

" angama ranki Dade.



Jakadiya nafuta ta wuce sashen su FAATU dontakai musu tsegumin abinda UMMAH tace na kayan da zata hada itama



Amma dai wannan jakadiya duk randa aka karya miki

kafar dama baxamuzo cetoba kuma ko jaje bamuzuwa

🙄😆

YAU jakadiya bata samu damar yin tsegumin ba tana shiga sashen nasu ta tararsu Da Baki ga LAMIDO yana nan



Dole tayi kwana takoma da baya

*KUYANGA* Tasa jaririn agaba tana kallo Abu biyu takeji akansa na farko Tsanarsa adalilin Haushin Ubansa da ta hany

ar da akasameshi tunda takasa manta yanda YARIMA yaringa mata karfa karfa akan saiya Santa a "Ya mace Ashe duk rabone Ke kira tabbas Banda ba,a Tara Sani ga Allah da tanada masaniyar samun ciki dashi da saita

bujire masa bazatayi masa biyayya ba koda zai

kasheta ko yaumata korar kare

Awani bangaren kuma tanajin Tausayin Yaron ta irin hanyar da yazo



Yanzu da ace ta hanyar sunna yazo da tuni gidan yacika da yan zaryar yiwa mutan gidan barka na xuwan jikan fari garesu



Wani makokon bakin cikine yatsay

e mata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login