Showing 75001 words to 78000 words out of 111738 words

Chapter 26 - Siyasa-ko-kabilanci-complete

08 Sep 2026

22

nasa yau kowacce taji jiki wajen kar6ar hauhuwa.

A falon k'asa yazauna yayi break fast d'insa, kafin yatashi zuwa d'akin Amatallah, har yanzu barci ta takeyi, waya yad'akko yafito babban falo.

Baban Fateema yakira kawu yakubu, ya gaidashi a

ladabce kafin ya Sanar mass ansami k'aruwa, kawu yakubu yamasa barka da addu'a ga jaririya kafin suzo.

Daganan Anty maijidda yakira itama, saikuma Nazeefa Dan bazai iya fad'ama Innani ba, baba kuma bayama iya waya sosai saboda ba'ajin maganarsa da k'y

au. Dan danan dangi aka rud'e da farin ciki.

Sai wajen 10 daga Aneesa har Amatallah suka tashi, hakama mai jegon kanta, shima hayaniyar su Nazeefa ne ya tadasu, dan danan gida ya kacame da surutu saboda dangi dasuka fara cikashi.

Dole Uncle yay

shiri yabar musu gidan zuwa kasuwa.

Can d'inma manyan kasuwar yasamu suka zauna meeting akan kafa k'ungiyar matasa, dolene kowanne abun alkairi akwai k'alubale acikinsa, a tashin farko Uncle baisamu had'in kan wasunsuba, dukda dogon bayani Na gamsarwa

dayay musu, wasuma saisuka fara d'auka Siyasa yakeson shiga kawai, dukda ransa ya6aci haka ya danne, yasamu mutane hud'u kacal acikinsu dasuka aminta da tafiyar tasu, hakanne kuma yad'an rage masa 6acin ransa.

Bayan sun kammala yakira Alhaji Sabi'u ya

labarta masa yanda sukayi.

Hamdala Alhaji sabi'u yayi, yace, "to inaga zuwa yanzun saimu zauna kuma mu tattauna kafin tsare-tsare su biyo baya, yanzu dai munada manyan mutane kusan 10 kenan, kuma kowannenmu babu matsalar rayuwa dazata takurasa yakasa

fidda d'an wani Abu Na taimako koda 5k ne kacal aduk wata".

" wannan gaskiyane".

"Yawwa to saimu zauna kenan a tattauna, insha ALLAH zan shigo wajjen naka zuwa dare nayi barka, daganan saimu tattauna".

" babu damuwa Alhaji ngd sosai, saik

azo".

Daga haka suka yanke wayar.

Badan Amatallah tasoba taje makaranta, tasha tsokana wajen su Fa'iza kuwa wai itama insha ALLAH bad'i iyanzu itace zata haihu musu, ai ko ranarma dai zee tasha harara kamar kullum da Amatallah kemata (itako zee ba

tama San Amatallah tana yiba ma

😜

.)

Bayan antashi suka ajiye magana akan ranar asabar zasuzo musu barka, dan gobe Friday basuda lectures ma ko d'aya.

____________________

Washe gari kuma Aneesa ta kar6i girki, Amatallah tashan kallo, kai kace

Aneesa zata canja gidanne, saboda shirye-shiryen kar6ar boss.

Washe garima Aneesa Nata rawar k'afa, ko kunyar 'yan barka bataji ma, saima shi Uncle d'in take bari da kunyar.

Su Fa'iza dasukazo barka sukace kinga yanda ake tattalin miji aii,

wlhy kimik'e idanma zaki mik'e, yanzu dai mijin nakune Ku biyu, tunda Uwargida tana jego, nanfa suka shiga fanfata da koya mata abubuwa, su goodness masu ido bud'e kam ai salon yanda ake soyayya iri-iri suka shiga koya mata, Fa'iza tasaki baki tana saurare

n ikon ALLAH itada Amatallah, duk da tarigaya tasan yan dama rayuwar k'abilunnan take, baruwansu iyashegensu sukeyi tun suna a waje, saikagama yarinya tabaro k'auyensu tazo takama d'aki a binni wai tazo neman kud'i, kuma bazata ta6a amsa sunan ita karuwa

baceba (ALLAH ya k'yauta dai), Fa'iza kam girman Kano Ce, bakomai tasani gameda suba sosai.

Haka dai sukasha hirarsu suka tafi.

Bayan Aneesa tagama kwanakinta Uncle yadawo hannun Amatallah, tabbas yaga canji a wannan karon, danta rage tsorata ida

n ya ta6ata, kuma tasaki jiki dashi babu laifi, dukda haka kuma bai nemi komai gareta ba ya had'iye kwad'ayinsa Dan bata lokaci, Duk da kuma acikin muguwar zak'uwa yake da son kasancewa da ita d'in, hakanne yasaka Ama... Sakin jiki dashi sosai, aganinta ya

barta bayanzuba, k'ilama saita kammala karatunta

🀭

(zaki bayani lol

πŸ˜†

).

***********

Akwana atashi babu wahala wajen Ubangiji, yau kam kwanan Fateema shida da haihuwa, gobene sunan baby, a yau d'inne kuma Uncle zaidawo hannun Amatallah bayan yagama k

wana biyu ga Aneesa.

Nazeefa data dawo gidan tun haihuwar Fateema ta fahimci babu abinda yashiga tsakanin Amatallah da yayansu, hakkane yasata k'udirin kafa musu tarko yau sudukansu, tasamu Anty maijidda ta sanar mata cewar sutafi plan B akan Amatall

ah d'in, dukda bata fito fili ta sanarma Anty maijiddah komaiba, amma itama tadad'e da fahimtar Amatallah har yau batasan mijiba, kodan yanda bata kishin matan yayansu sosai kamar yanda su suke kishi da ita.

Dawuri ranar Anty maijiddah tazo gidan s

aboda aikima.

Hummm fad'a muku yanda Anty maijidda tagyara Amatallah ranar ai 6ata lokacine kawai, saidaifa hummm!! Ina mai tabbatar muku yau Uncle bai Isa iya control d'in kansaba, gashi dama kwana biyun dayay d'akin Aneesa ma tana Off.

Kusan 5

pm tashiga kitchen d'inta domin yin girki, Kitchen d'in tsakar gida su Anty maijiddah sunata aikin abubuwan daza ayi Na suna gobe, Dan haka tanufi kitchen d'inta danyin girkin dare, yau kuma ne rana ta farko fazatayi girki a cikin d'inta, ta fiddo tukwane

a kwali ta wanke daduk abinda tasan zata buk'ata, kafin tafara had'a miyar Agusi d'inta datasha busashen kifi ga wadataccen naman tantakwashi, tunifa gida ya d'auki k'amshi su Anty maijidda sai fad'i suke Amatallah zaki kashemu da k'amshi.

(Nima dai A

matallah zata kasheni da kwad'ayi Anty maijidda

πŸ˜‹

lol)

Batasanma sunayiba aiki ya d'auke hankalinta, ta had'a lemon kankanarta dayasha madara da kayan k'amshi, ta fere doya mai k'yau ta d'ora, harga ALLAH bazata iya daka sakwarar mutane kusan 15 ba, Da

n bayansu Kansu da yara sunkai goma ga kuma Anty maijidda nazeefa sai yayyen Maijego biyu da kanwarta zaliha ga gwaggo rakkiya, ga kuma wata dattijuwa k'anwar Maman maijegon, kuma duk gidan zasu kwana, yayyen fateemar ne kawai tasan komin dare k'ila zasu w

uce, Nazeefa Amatallah takira domin Neman shawarar yazatayi.

Dariya Nazeefa tayi tana fad'in "amma ke ragguwace, kina nufin Yaya kawai zakiba sakwara? to bamu yardaba".

" kai Anty Nazeefa ki tausayamin, ALLAH ba abune mai sauk'iba dakan sakw

ara".

"To Na tausaya miki 'Yar Uncle, yanzu dai dafa doyan saiki d'iba iya wadda zaki daka masa, nikuma sainakai sauran babban kitchen ahad'u adaka gaba d'aya".

''Yauwa Anty Nazeefa ngd, shiyyasa nake sonki".

Dariya sukayi gaba d'aya Nazeefa

tafice.

Zuwa magriba ta kammala komai, suma su Nazeefa sun daka waccan, ta had'ama Uncle abincinsa ta d'auki tukunyar miyar duka ta kaima Anty maijidda.

Abincin ta d'auka takai samansa, takuma saka turare kamar yanda Anty maijidda tace mata, said

a taga komai yayi dai-dai har ruwan wanka ta had'a masa Dan tasan yana gab da dawowa, ta had'ashi da zafi sosai yanda sanda zai dawo yayi daidai wanka.

d'akinta takoma ta shirya itama, dama tayi wankanta tunkan tayi sallar magriba, kwalliya tayi mai

sauk'i tayi d'aurinta mai k'yau yanda Fa'iza ta koya mata, (Amatallah duk irin wad'annan abubuwan bata iyasuba, saboda batada k'awaye gakuma yanayin inda ta tashi, barta dai da tsafta ga nutsuwa, amma irin dai iyayi Na 'yammata bata iyaba

πŸ˜„

).

K'amshi t

ake tamkar tayi 6arin turare a jikinta, kodai mace taji k'amshina nan nata saita firgita balle kuma.....humm.

πŸ™ˆ

lol

Ana kuwa idar da sallar isha'i Uncle yashigo gidan

Yarane kawai a falon, dan haka suka iso da gudu suna ihun murnar masa oyoyo, rungum

esu yayi yana murnar ganinsu shima, harma da yaransu Anty maijidda, zaliha dake tare da yaran a falon Dan tana fashin salla ta gaidashi, cikeda fara'a ya amsa yana fad'in "autar mama kamar kiyi zamanki tare damu kawai".

'Yar dariya tayi tana fad'in

" Yaya aikuma makaranta".

"Anya kuwa ba wayo bane?".

" ALLAH kuwa Yaya".

"Shikenan to na yarda". yay maganar yana nufar hanyar 6angaren Fateema, bayan Sahib ya kar6i ledojin hannunsa yanufi samansa dasu.

Ya iskesu Anty maijidda zaune a

falon Fateema, Mariya Na salla itada gwaggo rakiya, risinawa yayi ya gaida inna Nafi dake zaune tanama jaririya wanka, su Anty maijidda suka gaidashi suma itada Anty maimuna, sunata d'aura kayan rabo.

Anty maimuna tace, " Yaya Muhammad fatin tana ci

kifa".

Murmushi yayi yanufi bedroom d'in Fateema, Anty Mariya data idar ta kalli su Anty maijidda tana murmushi "kai ya Muhammad Na birgeni saboda kunyarsa wlhy".

Duk dariya sukayi , Anty maijidda tace kad'anma kikagani Indai ya Muhammad ne.



A zaune ya tadda Fateema tana ware kayan fitar suna dayay musu suduka, amma ita kala biyar, sukuma su Amatallah uku-uku itada Aneesa.

Murmushi sukaima juna kafin ya zauna kusada ita ya rungumeta yana mata kisses zafafa a wuya, a hankali yace, " I mis

s you my sweet tee....".

Duk da taji dad'in maganarsa hakan bai hanata yin 'yar dariya ba, ''kai Nurrina harda zolaya abin? Kaida keda sabuwar Amarya fil a hannu".

Wani k'asaitaccen murmushi yasaki yana shafar gemunsa dakuma manna mata wani kiss

d'in, "humm My tee... Amarya daban ke daban ai".

Murmushi kawai tayi batace komaiba, 'yar hira sukayi da tattaunawa gameda sunan gobe, yakuma bata za6in sunan datakeson asama baby.

" duk wanda kasaka yayi Nurri, nidai nabaka za6i kamar ko yaush

e".

Yay d'an murmushi yana mik'ewa, "to shikenan ALLAH ya raya Ameenatu".

Itama murmushi tayi tace, " Amin Nurrina lallai Anty Mariya zataji dad'in wannan karamci sunan Iya babu zato".

Baice komaiba yafita yana dariya.

Ya tarar Aneesa d

a Nazeefa da Amatallah ma sunzo falon, Nazeefa ta gaidashi, Aneesa ma da Amatallah suka masa sannu da zuwa.

Fakar idon jama'a yayi ya kashema Aneesa ido d'aya sannan yafice.

Tayi murmushi kawai tacigaba da abunda takeyi.

Anty maijidda ta kall

i Amatallah "madam atashi ko".

A kunyace Amatallah tatashi tafita, sukayi mata dariya banda Aneesa da tayi murmushin yak'e kawai saboda kishi, ga Amatallah tasaka hijjabi kan kwalliyarta babu maicewa ga yanda take, sai uban k'amshinta daya baje falon.

A hanyar 6angarensa ta iskeshi tsaye yakama k'arfen benen idonsa a k'ofar Falon Fateema.

Hakanne ya tabbatarma Amatallah fitowarta ya tsaya jira.

Suna had'a ido yad'an sakar mata harara sannan yafara takawa yana hawa.

Bayansa tabi tana

gumtse dariya................✍

🏻

_gaskiya 'yan bauchi state muna matuk'ar godiya da goyon bayanku ga shugaban k'asarmu mai kishinmu baba buhari, nabaku page d'innan k'yauta saboda farincikin dakuka Sani yau, ALLAH ya maida shugaban k'asa gida lafiya da

dukkan 'yan uwa dasuka halacci wajen campaign d'in, ALLAH kabamu shuwagabanni nagari

πŸ™πŸ»

._

Bauchi inayinku irin Trillion's d'inan

πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°

❀❀❀❀❀

πŸ‘πŸ»

πŸ€©πŸ‘ŽπŸ»

One luv my sweet Fan's

πŸ₯°

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*

πŸ˜­πŸ™πŸ»

[1/16, 9:01 PM] Aysha

Galadima: *_Typing✍

🏻

_*

*_HASKE WRITER'S ASSO..._*

πŸ’‘

_{home of expert and perfect writer's}_

*_SIYASA KO K'ABILANCI_* ⁉

_(Hattara matasa)_

*_Bilyn Abdull ce

πŸ€™πŸ»

_*

*_Special gaisuwa gareku Haskakakku_*

_N

ana Diso. Pherty xarah. Asmy b Aliyu. Maman khady. Miss Xoxo. Nuceey luv. Zainab bawa. Hafsat rano. Jiddah Aliyu. Kdeey. Slimzy. Khaleesat Haidar. Billy Galadanci. Saffiyya Huguma. Ayusher Muh'd. Ai'sha d'ansabo. Ummu basheer. Ummi Ai'sha. Hajjace. Faxy fa

shion. Feedhom. Bilyn Abdull (nima Na gaida kaina

πŸ€­πŸ˜‚

)_

*ALLAH ya k'ara haskakaku!*

*HASKE WRITERS ASSOCIATION kenan gaba d'aya masoyanmu*



πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ₯°πŸ˜˜πŸ€πŸ»πŸ‘πŸ»

____________________

*_Number 30_*

____________________

Tashiga be

droom d'insa da sallam, harya fara k'ok'arin cire babbar rigarsa, saida yagama cirewa ya ajiye sannan tace, "sannu da zuwa Uncle".

Ya amsa yana k'ok'arin fara cire mafallan rigarsa ta ciki, juyawa tayi tana fad'in " Uncle bara inje, idan ka gama s

aina daw........"

Da sauri yarik'o hannunta tadawo baya, yad'an had'e fuska kad'an idonsa akanta. Maida nata k'asa tayi tana kallon k'afafunsu, duk kuma saitaji babu dad'i, ta marairaice murya kamar zatayi kuka dan ganin ya rik'eta kuma yayi shiru.

"Uncle please miya faru?".

Ta d'anso bashi dariya amma saiya kanne, yasa yatsu biyu ya d'ago ha6arta.

idonsa taga ya k'ank'ance yana mata wani kallon da yasha banban dana kowacce rana, da sauri ta janye daga kallonsa.

Yad'anyi gyaran murya.

Hakanne yasata dole takuma kallonsa.

Girarsa d'aya a d'age yace, " Khadeeja kinason kishiyoyinki su rainaki ko?".

Cikeda mamaki tace, "Uncle kamar ya?".

" kamar yanda kike nuna halin ko inkula akan mijinki. Haka kikaga su Aneesa nami

n? Sai dafa akace ki biyoni kika taso, Daba ace ki bizoba ma baki zuwa kenan ko?".

Kanta ta girgiza masa alamar a'a.

"To miyasa ke bakya koyi dasu? Ina kallonki kamar mai wayo amma ba haka bane ashe".

A shagwa6e kamar zatayi kuka tace,

" ALLAH uncle inajin kunyane, amma kayi hak'uri bazan sakeba zan canja insha ALLAH".

Sai yanzu taga yasaki wani lallausan murmushi yana shafa gemunsa, murya k'asa-k'asa tamkar mai gudun ajisu yace, "Kunyace kawai matsalarki my babie? Karki damu zan ca

njaki da kaina ma kafin ki canja kanki".

A kasalance ta d'aga masa kanta, saboda dukkan illahirin jikinta yamutu murus da salon Na Uncle.

Ya d'an murmusa tare da bata sumbata a goshi, ya saki hannunta yacigaba da cire ma6allan rigarsa, itadai

Amatallah kanta a k'asa takasa kallinsa.

Tsaf ya cire komai, dagashi sai vest da boxer, yatako a hankali zuwa gabanta, duk'owa yayi saitin kunnenta, har tanajin saukar numfashinsa a dokin wuyanta, yace, "indai kunyace yau d'innan zan cireta kowama ya

huta". yana gama fad'a yashigewarsa toilet yana wani murmushi mai k'ayatarwa.

Rufe k'ofarce tadawo da Amatallah hayyacinta, tabi k'ofar da kallo tana cigaba da juya maganganunsa, sometimes takanyi mamakin Uncle da halayensa, gaba d'aya ya canja mata ya

nzu, kai tsaye yake mata abubuwa ko kunya babu, maganarsa ta k'arshe tafad'o mata arai, sai kuma taji gabanta ya fad'i. a fili ta furta ''ALLAH yasa ba abinda nake zaton bane".

Bata bar wajenba saida taji motsin zai fito ta gudu falo.

Baiyi mamak

in rashin ganintaba, dan yasan dama bazata tsayaba, d'an murmushi yayi yacigaba da goge jikinsa da k'aramin towel.

Amatallah Na zaune afalo ta k'urama TV ido, saidai azahiri hankalinta bama akansa yakeba, yana kan tunanin maganar Uncle ne, dukda wani

6angare Na zuciyarta yana fad'a mata ba haka bane.

Jin anjawota yasakata yin firgigit tadawo hayyacinta, da sauri ta kallesa dukda daddad'an kamshinsa ya tabbatar mata shine. baiyi maganaba, sai hijjabinta daya cire.

"Kai my best! wai ina kika s

ami turaren nan mai narkar danine?". Yayi maganar cikin kunnenta.

Hannu tasa tarufe fuskarta tana murmushi, ''kai Uncle naka ai yafi nawa dad'i".

Ya murmusa a karo Na barkatai tare da kuma jawota sosai a jikinsa yana shinshinar wuyanta, tuni ya

fara sakar mata wasu zafafan kisses, daga haka aka koma (abinda Malam ya hanani fad'a

🀭

).

Tunfa Amatallah Na kallon lamarin a matsayin k'arami harya koma fin k'arfin, turarenta, gaba d'aya yagama birkita boss bayaji baya gani, ya mantafa (Khadija c

e d'iyar brother), saida ya rud'ar mata dadukkan jiki da.......sannan ya fara Ankara a falon suke, kuma koyaushe cikin yaran wani zai iya shigowa dan k'ofar abud'e take. daga ita harshi tagwayen ajiyar zuciya suke saki, jikin Amatallah sai 6ari yakeyi, ta

duk'ar dakai ta kasa kallonsa ko sau d'aya.

Shikansa kunyace takamashi, amma saiya Fiske ya sauka k'asa yana fad'in ''sakko kibani abinci yunwa nakeji my best". Yay maganar murya a shak'e tamkar mai Mura.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login