Showing 102001 words to 105000 words out of 111738 words

Chapter 35 - Siyasa-ko-kabilanci-complete

08 Sep 2026

29

Ama......?"

"K'alau Fa'iza, mikika ganine?".

" kawai tun jiya nifa wani sukuku nake ganinki, tamkar wata mara lafiya".

Kanta ta kwantar jikin kafad'ar Aysha tana jan k'aramin tsaki, "kibari

kawai, nifa jikin nawane ma duk babu wani dad'i, kuma babu inda yakemin ciwo wlhy".

Da sauri Fa'iza tace, " tin yaushe kika faraji?".

"Yanaga kin wani tsorata? bafa wani abu bane".

Cikin dariya Aysha tace, " aimu fatanmu yazama wani ab

un, nifa wani k'yauma naga kinayi kwanan nan hajiyata, miye sirrin?".

Duka Ama... takai mata, Aysha ta goce da sauri tana dariya.

"To miye na dukanta? ba gaskiya tafad'aba? baby ALLAH yasa abinda muke fatane dai, amma koni wlhy naga kin k'ara

k'yau, maganace dai kawai banyiba".

" uhm kuma daina wahal da kanku, ni banida komai, kawai inaga malaria keson kamani dai".

Dariya suka mata, akadai bar maganar ahaka, kowa kuma ak'asan ransa yana addu'ar ALLAH yasa abinda suke fatane

😊

.



Kwana biyu dayin wannan maganar Ama.... ta tashi da zazza6i mai zafi, gashi ranarma Uncle ba d'akinta yakeba, yana wajen Aneesa.

Har zasu fara break fast babu Ama...., dayake weekend ne.

Uncle ya kallesu yana fad'in wai Khadija fa?".

An

eesa tace, "Wlhy nibanga tafitoba tun d'azun, Siddiqa ma tashiga tafito tace barci takeyi, tona d'auka ko gajiyace tahanata tashi da wuri".

Fateema ma tace, " ni wlhy kwana biyunnan ma sainaga kamar Auntyn yara batajin dad'i sosai".

"Nima n

ad'an zargi hakan, harma Na tambayeta amma tacemin babu abinda ke damunta, bara dai Na dubata kawai".

Sukace to.............

Manage please

😎

One luv

😻😻😻

[1/25, 12:25 PM] Aysha Galadima: *_Typing✍

🏻

_*

*_HASKE WRITER'S ASSO..._*

πŸ’‘

_{

home of expert and perfect writer's}_

*_SIYASA KO K'ABILANCI_* ⁉

_(Hattara matasa)_

*_Bilyn Abdull ce

πŸ€™πŸ»

_*

____________________

*_Number 39/40_*

____________________

Tundaga falo jikinsa yafara sany

i, dan babu alamar tayi gyara, da sallama yashiga bedroom d'in, babu amsa, ya kalli gadonta, tana k'udundune a bargo tarufe har kanta, da sauri ya k'arasa ya yaye bargon.

"Khadija lafiya kuwa? da uban zafinnan kika lullu6........"

Maganarsa ta

tsaya a mak'oshi saboda yanayin daya ganta, ga jikinta zafi zauu, har wani huci ke fitowa.

"Ya salam my best!" yafad'a yana zama gefen gadon, hannu yakuma kaiwa a wuyanta ya ta6a, tarik'e hannun da sauri tana rawar sanyi, "Uncle please bar ta6ani, han

nunka sanyi".

"dama bakida lafiya amma baki fad'aba Khadija? kuma har tadaki nazo nayi da asuba".

" Uncle sannan zazz6in ya saukane, banyi zaton zai dawoba da safe".

"Dashi kika kwanama kenan?".

Kanta tad'aga masa tana wani lumsh

e idanu dakuma dunk'ulewa waje d'aya saboda bargon daya cire mata.

Tashi yay yashiga bayinta, yahad'a ruwa maid'an zafi sannan yadawo, ya taimaka mata tasakko tanata rawar sanyi da fad'in "Uncle please kabarni Na kwanta, ina ganin jirine".

" Sorr

y my best! Bara namiki wanka kiji d'an k'arfi saimuje Asibiti".

Tirjewa tayi tana tura baki gaba, "nidai Uncle basai munje asibitiba, danasha parasitemol zan warke".

" to naji shagwa6a66iya, muje dai ayi wankan first ".

Da kansa yamat

a wankan, ya taimaka mata suka fito, a bakin gado ta zauna, ya d'akko Vaseline ya shafa mata, tanata langa6e masa itafa jiri take gani, hakadai ya lalla6ata yasaka mata doguwar riga bak'a.

Fita yayi itakuma takoma ta kwanta harda jan bargo takuma lull

u6a, taji dad'in wankan, dan ciwon jikin saitaji yaragu harma da zafin.

Yana fitowa suka hau tambayar miya faru da Ama.... d'in?.

"Batada lafiya Ashe, zazzabi takeyi, Aneesa had'a mata break fast d'inta".

Sun nuna jimamainsu akai, Aneesa

ta had'a break fast d'in ta d'auka da kanta domin kai mata, Fateema da Uncle sukabi bayanta.

Da k'yar tatashi tasha kunun bayan su Fateema sunmata yaya jiki, ta amsa dak'yar tana tambayar ya yara suka kwana.

Uncle yayi yayi tatashi suje kod

a camix ne tunda yau babu aiki amma tak'i, itadai yabata perasetimol tasha kawai.

" nifa bazan baki maganiba kai tsaye, nasani ko ALLAH ya share kukanmu ne, kokuwa salon nama kaina ganganci".

Baki ta turo masa tana matso hawaye, "amma Uncle ko

fa masu tsohon ciki sunasha, kuma babu abinda yake musu, tunda a asibiti muna badawa aii".

Shiru kawai yayi yana kallonta, yama rasa mizai cemata, daga k'arshe dai saishi ya hak'uran, yabata tasha takoma ta kwanta.



Zazza6i dai yak'i sauka,

saidai jikin ya huce yakuma dawo, ba Uncle ba hatta su Aneesa duksun damu, dan tasaba ranar weekend sunta shagalinsu da yaran agida kafin su tafi islamiyya, su Kansu yaran duk sunyi sukuki.

Da daddare dai abinda batason dole akayi, Uncle yakira doctor

Shu'aibu yadubata, gudun karya bata Magani suyi 6arna yace tayi gwajin tsinke.

gwajin farko ya nuna mumsami baby

πŸ’ƒπŸ»πŸ˜€

.

Murna wajen Uncle ba'a magana, babu kunya ya rungumeta a gaban Doctor Shu:aibu, Ama..... kam hawaye kawai takeyi, dukda

tad'an dad'e tana zargin cikine dama, soboda aikintane, (dan kunsan doctor Ce fannin mata insha ALLAH anan gaba kad'an zata zama kwararriya

πŸ’ƒπŸ»

).

Su Fateema Kansu dai murna sukeyi, kodan k'aunarda Ama....kema 'ya'yansu dolene su tayata farincikin sam

un NATA itama, kuma ko kad'an basuji kishin farin cikin da mijinsu ke nunawa akan cikinba.

Doctor Shu'aibu yace, "dama nasan itama tasan tanada, kawai dai ta 6oye mukune".

" Uncle ya kalli Ama..... yace, "wai haka my best!?".

Kanta ta

6oye cikin bargo tana murmushi.

Duk sai sukayi dariya, Uncle yaraka Doctor sannan yadawo suka cigaba da farimcikinsu.

Ranar dai dole Aneesa tayi sadaukarwa na kwananta ga Ama....., Uncle yakwana a wajenta saboda jikinta. (Anee kin biyamu kwannamu

πŸ˜‚

😜

).

Hummm kafin kacemi maganar cikin Ama....Yazagaye dangi makusantansu, har 'yan jos an gwargwad'a musu, murna dai ba'a magana, 'yan dubiya su Anty maijidda dasu Asiya su Nazeefa mai jego, ita Ama... Kunyarsuma takeji, duk kuma d'okin son samun ci

kin saiya 6uya yanzu da'aka samu d'in.

Babama yayi murna, hakama innani, dukda bata fito ta nuna a filiba, amma takanas shehu yakawota tazo ta duba Ama.....

Amatullah nashan wahalar cikinnan, dan laulayi takeyi sosai, dolene kaganta Tabaka taus

ayi, dukta rame sai uban haske data k'ara, dukda kasancewarta bak'a.

Girki dai su Fateema sun sauke mata, saidai ta kwana da miji, wataranma idan abin yay tsanani hakura suke da kwanan Nasu ya kwana a d'akinta, tanashan k'arin ruwa kam tamkar wata ga

llon

🀭

, kullun cikin zirara mata akeyi.

To Ama...ALLAH yaraba lafiya.

***********

Kwanci tashi babu wahala wajen Ubangiji, ga Ama.... cikinta yashiga wata na 7, yafito d'as kuma yamata k'yau, tanata karatunta hankali kwance, dan Alhmdllh tunda cikin

yashiga wata na 5 tasamu sauk'in laulayin, saidai abinda ba'a rasaba, harma taje jos tayo sati biyu acikin d'an hutun dasuka samu, tazaga dangi sosai dukda ba wannane zuwanta Na farkoba, har anguwarsu taje ta gaida makwafta dasuke mutunci dasu kafin rasuwa

r su baba, dukda ma wasunsu sun rasa rayukansu a lokacin wancan rikicin, wasu kuma sunbar garin gaba d'aya, har kuka tayi dataga kufan gidansu, Dan tuni Uncle yanemi shawarrata akan ayi masallaci ko islamiyya awajen, domin ladan yadinga kaiwa ga iyayenta,

takuwa amince, yasa akayima wajen gyara bayan an rushe, masallaci akayi k'arami da islamiyya mai aji hud'u k'anane amam, sai Bohol da akayi mutanen anguwar NATA d'ibar ruwa, dama basudashi. Wani son Uncle Yakuma ratsa ruhinta saboda wannan hidima dayay ga

mahaifanta, (kowa yasan anason sadaka mai gudana ga mamaci). a zuwanne takejin labarin d'aure Ramzaki da akayi, saboda kashe wani da Mr Pam yasa sukayi, kuma aka kamasu, koda sukace shine yasakasu aka kirashi saiyace shibaima ta6a ganinsuba ballantana ya s

ansu, k'arya suke masa, hakanne yasa aka kaisu Court, hukuncin shekaru 25 aka yanke musu a prison. Amatullah dai jitayima INA itace alk'alin , da ratayesu zata sakama ayi take anna, amma hakanma tayi farinciki koba komai zai d'and'ani azabobi kafin yaje wa

ken ALLAH kuma. Satinta biyu tadawo Kano ta koma school aka cigaba da bugawa.

Rayuwar gidansu nanan yanda take, saidai 'yan canje-canje daba'a rasaba, amma sunan akan tattalin mijinsu da kishinsa, kuma hakan bai hanasu k'yautatama junaba.

Haka s

hima mijinsu mai gajiya da basu soyayya mai tsaftaba, kowacce gwargwadon iko yana nuna mata tattali da soyayya, yana k'ok'arin adalci a tsakaninsu, wadda yafi so kuma yabarma zuciyarsa.

Maganar K'UNGIYARSU kam saimuce Alhmdllh, yanzu haka suna k'ok'ari

n had'a wani gagarumin taro na k'asa, domin wayarma matasa dakai a kan za6en dake tunkaro k'asar, Wanda bai wuce saura kwanaki k'alilanba a gudanar dashi.

Sai dai kuma a wannan tsakaninne wani Abu Mara dad'i yafaru

😒

, shine Rasuwar baba, adaren juma'a

ranar alhamis kenan jikinsa yay tsanani, hankali tashe Innani takira Uncle kusan 1pm, harma ya kwanta, dan ranar a d'akin Amatallah yake, suna tsaka da barci tana kwance a jikinsa, yayinda hannunsa ke rungume da cikinta, da k'yar ya iya lalubar wayar a k'a

rk'ashin filo, batareda yaga mai kiranba yad'aga dafad'in "please wanene?".

Muryar data daki kunnensa tasashi wartsakewa babu shiri, innani yajiyo tana fad'in " maza kazo gida Muhammadu jikin babanku ya rikice".

A firgice ya wuntsilo daga ga

don, haryana bigema Ama.... cikinta, Wanda zafinne yasata farkawar dole tana fad'in "wayyo ALLAHNA".

ina Uncle bai sauraretaba, sorry kawai yace mata yafice da sauri.

Dukda azabar da Ama... keji haka ta tashi zaune da k'yar, mamaki yacikata, tabbas

babu lafiya, dan ko juyi zatayi cikin barci saiya farka, kuma zai taimaka mata ta juya cikin lalla6awa, amma yanzu ji yanda ya maujeta bai kulaba, sakkowa tayi tafito tana d'an cije baki, dan har yanzu inda ya bigeta bai daina zafiba, yaran cikinta sai mo

tsawa yakeyi alamar shima yaji zafin maybe (

πŸ˜‚

lol).

Tana fitowa falon yana fita shikuma a rikice, ya canja kayan barcinsa zuwa farar jallabiya, hakan yakuma rud'ar da Ama... ta tada su Fateema duk ta sanar musu.

Jigum-jigum sukayi, kowa yana sak'e-

sak'e da tunanin mike faruwa? dukda wani 6angaren tunaninsu yana kan babane k'ila, saboda jiya jikin nasa yad'an motsa har sukaje suma suka gaidashi.

Kasancewar titi babu motoci sai tsilli-tsilli yabama Uncle damar zabga gudu, lokacin dayaje gidan

lamari ya 6aci kam, danba baba ba hattada Innani tafita hayyacinta, Aysha sai kuka takeyi, hakama gwaggo Rakiya.

Dole adaren suka tafi asibiti, sai daifa babu tsumi babu dabara, kafin asubahi rai yayi halinsa

😭

, ALLAH ya d'auke kayansa.

Mutuwar dat

a zamema Uncle ta uku dabazai ta6a mantawa da itaba, duk yanda yaso ya daure ya rarrashi su Innani yakasa, shima kansa yakifa akan gawar yafashe da kuka

😭

.



😭

hakanne nima yasani kukan, danna tuna da rasuwar nawa mahaifin

😭

, ALLAH ka gafarta musu, ka y

afe musu, muda suka bari ALLAH ka d'auki ranmu muna a masu imani da tsonka ya rabbi, ya ALLAH ka k'ara mana soyayyar manzon ka tsaftatacciya a rihinmu

😭

.

Marayu ALLAH yabamu hak'uri kunji, inayinku a duk inda kuke.

😭🀝🏻

.

To anyita ta k'are, baba y

atafi ya barsu Uncle, yanzu shine babban wa, shine kuma Uba.

Washe gari misalin 10am akayi jana'izarsa wadda ta tara d'unbin Al'umma, kodan d'ansa yatara, dan matasa dama dattijan sunta tururuwar halattar wannan jana'iza domin nuna hallaci ga Alhaji

Muhammad Ahmad Labbo.

A kwana Ukun data gabata ba'a cewa komai, dolene kaga Uncle dasu Ya Jabeer subaka tausayi, barema su Nazeefa da Shehu da Anty maijidda, hakama su Amatullah duksun jigatu, amma Yaya za'ayi da ikon rabbi, saidai hak'uri.

A

LLAH sarki Innani, mace mai hak'uri da k'ok'ari, tasha jiyya harta tsawon shekaru kusan 7, ALLAH yabata ladan jiyyar datayi ta adalin mijinta dattijon kirki mai yakana da dattako.

******* ******* *******

Tun bayan rasuwar baba abubuwa sukaima

Uncle cak, Yakoma sai a hankali, kasuwama yadaina waiwayarta, wajen aiki kam danya zame masa tilasne, sauk'in sama ba kullum baneba, K'UNGIYA kanta tasan jagoranta yazama abin tausayi, dole sai Alhaji Sabi'u ne yacigaba da tafiyarda shugabancin kafin komai

ya daidaita.

Su Kansu matsansa saidai Addu'a suke binsa dashi, amma komai nasa yayi sanyi.

Ahaka dai yauda gobe har zuciya tafara sanyi da hak'un dangana, yafara komawa kan harkokinsa dakuma jan 'yan k'annensa a jiki, yakuma ninka kulawarsa ga ma

haifiyarsu Innani, wadda ayanzu itace Uwa Uba kuma, itama kanta dukta fita hayyacinta, ga girma na tsufa.



Cikin Amatallah yashiga watanni na tara kenan, haihuwa yau ko gobe, dolene kaganta tabaka tausayi, gawata kumbura datakeyi, Uncle dukya d'aga h

ankalinsa, koda yaushe cikin kiranta yake a waya, a d'an tsakanin dole tad'an jinkirta dazuwa Asibitima, tasamu Hutu harsai ta haihu.

Idan tana zaune haka zaita mammatsa mata k'afafu, idan kuma bayanan Aneesa ko Fateema zasuyita matsa mata, saikuma in

yara sundawo makaranta, Amatallah tazama 'Yar gata, ai babu abinda zatacema ALLAH sai godiya, itadai ana gudun KISHIYA ita k'aunar nata takeyi, da godema ALLAH dayasa sune abokan rayuwarta, idanma taji mace nafad'in batason KISHIYA saitace amma bakida way

o wlhy, ai KISHIYA abar soce, ta 6angarori masu yawan gaske, mai dogon nazari da hangen nesane kawai zai fahimci hakan, musamman idan ALLAH yabaka mai hankali da sananin yakamata, amma inka samu mai burin korarka aika Shiga tara (

πŸ™

ALLAH karabamu da irin

su to).

Ranar wata talata da rana kusan 1pm Amatallah tana kwance barci yad'an figeta wani azababben ciwon Mara ya tasheta kuwa, aiko a firgice tatashi tana kuka dakiran Ammi da baba.

Fateema na kicin tajiyo kukanta, a rikice tazo 6angarenta, h

alin data isketane ya tada hankalinta, tashiga rambad'ama Aneesa kira, itama a guje tazo.

Basu wani 6ata likaciba suka memo taxi sai asibiti.

Suna isa aka shiga bama Ama.... taimakon gaggawa.

Ganin anshiga da ita suka sami damar kiran Uncle su

ka Sanar masa, mintuna k'alilan saigashi ya iso shida Shehu, isowarsu kuma babu dad'ewa ALLAH ya sauki Ama..... lafiya, ta sunkuto baby girl d'inta, saikuma ga baby boy babu zato.

Nanfa murna da farinciki mara misaltuwa ya kaure, kafin kace mi labari y

a karad'e dangi makusanta.

Ganin ta sauka lafiya zuwa yamma aka sallesu suka tafi gida tareda dangi dasukazo tayasu murnar wannan haihuwa.

Uncle baki yak'i rufuwa dan dad'i.

πŸ˜ƒ

.............✍

🏻

Uncle nima bara na tayaka to

😁😁

, nasan masu karatuma

zaru tayamu.

πŸ’ƒπŸ»

One luv

😻😻

.

[1/25, 4:04 PM] Aysha Galadima: *_Typing✍

🏻

_*

*_HASKE WRITER'S ASSO..._*

πŸ’‘

_{home of expert and perfect writer's}_

*_SIYASA KO K'ABILANCI_* ⁉

_(Hattara matasa)_



*_Bilyn Abdull ce

πŸ€™πŸ»

_*

____________________

*_Number 41/45_*

____________________

Uncle bai samu damar ke6ewa da Ama... ba sai dare, yashigo d'akin da sallama, gwaggo Rakiya tana zaune a falo tagama sakama macen kayan sanyi dan shirin barci,

ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login