Showing 75001 words to 78000 words out of 96103 words

Chapter 26 - RAGAYAR DUTSE BOOK 1 COMPLETE

25 Aug 2026

60

nan, ba dai kashe kuWi ba."

Sadik ya ce, "zamu gwada Mama, in zamu iya to, in baza mu iya ba sai mu canja waje" ya faWa yana shiga da motar, suna sake kallon asibitin dan wajan ajjiye motar ma wani waje ne mai zaman kansa da kansa.

Suka fito a sanyaye suna takawa a hankali zuwa ?ofar da zata shigar dasu.

?ofar automatic slide glass door ce, kana zuwa kusa da ita zata buWe, tama buWewa zaka ka ji ?aramin sauti ana cewa welcome to Nadira Hopital. Sanyi da wani shegen ?hamshi ya ratsasu, Islaha ta yu saurin saka facemask Winta, dan sanyin zai iya yi mata yawa.

Babban reception ne mai kyau, ga kujeru lafiyayyu an tanada, ga tv da duk abinda ya kamata a wajan.

Table Win ma'aikatan suka ?arasa ita da Sadik. Islaha ta ce, "barkan ku da aiki."

Baturiya ta Wago ta ce, "you are welcome Ma'am, hausa kaWan kaWan."

Islaha ta yi murmushi, ta canja yare zuwa turanci ta ce, "akwai mara lafiyan da aka kawo yanzu, ko zamu iya sanin inda aka kai sa?."

"Yana emergency, kafin ku je zaku cike form, sannan za ku cike file da payment."

Islaha ta cike komai da sunan Baffa da duk abinda za a yi. Bayan ta gama ta mi?a mata, Sadik ya mi?a Atm Winsa dan a cire kuWin file Win da aka cike.

Bayan ta saka ta mi?o masa ya saka pin yace ya ji wayarsa ta yi ?ara, ya zaro ido ganin uban kuWin da aka cire masa kawai na kuWin file.

Ya kalli Islaha ya ce, "Matar Hamma anya asibitin nan zai zaunu a wajen mu? Kalli fa."

Ta kalli alert Win ta zaro ido ta ce, "kai! Iya wannan kuWin file ne ko harda ganin likita?."

Kafin ya bata amsa ta juya tana tambayar matar dan ta tabbatar, ta bata amsa da na file ne da ganin Dr a emergancy.

A sanyaye Islaha ta ce, "ina son haWuwa da Dr...." Sai ta kalli takardar da Sadik ya bata ta ce, "Dr Esma'il."

Matar ta ce, "A nephrologist?."

"Yeah."

"Office Winsa yana sama, floor 2, office number 4." Suka yi mata godiya suka fara zuwa inda Baaffa yake ko zasu ganshi. Basu samu damar ganinsa ba, hakan ya saka Islaha da Sadik suka wuce wajan Dr.

Suna zuwa inda aka faWa musu suka gansa ya fito daga office Win. Sadik ya ce,  Dr barka da aiki. ya bashi hannu suka gaisa, Islaha ta ce, "mun zo daga general hosptal ne" ta faWa tana mi?a masa takardar.

Ya karSa ya karanta ya kalle ta ya ce, "Dr Habib?."

"Shine."

"Ina mara lafiyan?."

"Yana emergency."

Ya girgiza kai ya ce, "zan je in gan shiyanzu." Daga haka ya bar wajan su kuma suka biyo bayansa.

Ta wani section suka zo wucewa daidai inda zaka hau elevator ka koma floor 1, ta gasecurity guard a wajan a tsaye alamun akwai babban mutum da yake a kwance a wajen, ta girgiza kai tana cewa, "Maybe gwamna ne a kwance" ta faWa tana wuce wajan.

? ?? Rehaan yana zaune kusa da Mamy, ya kwantar da kansa a kafaWarta ita kuma tana shafa kansa a hankali. Mamy ta shagwaSa Rehaan, musamman in bashi da lafiya komai yi masa take yi, hatta wanka da zai tsaya Mamy zata iya yi masa saboda kar ya wahala.

In bashi da lafiya a apartment Winsa take kwana, ita take bashi abinci, ta kwantar dashi a jikinta, ta ri?e shi ya tashi. Ta saba masa da hakan sosai, shiyasa in yana Uk kuma rashin lafiya yake shan wahala, dan shi ya saba har tea a baki ake bashi.

Mummy mahaifiyar Jafar ce ta shigo da ?annensa maza biyu da mace Waya. Mamy ta yi murmushi da jin daWin ganin Mummy ta ce, "Mummy sannu da zuwa."

Mummy ta ajjiye basket Win da ta shigo dashi, ta ce, "Sannu Mamy. Ya jikin Rehaan Win?" Ta faWa tana shafa kansa kamar yadda hakan ya zamar musu sabo.

Rehaan ya Wago a hankali ya ce, "Mummy sannu da zuwa."

"Yauwa Rehaan, ya jikin?."

"Na ji sau?i."

"Allah ya ?ara lafiya."

Ikram ta ?arasa tana kallonsa ta ce,  Sannu my dear, ya jikin na ka?. Ya Waga mata kai alamun da sau?i, ta ce,  Ka tabbatar da sau?i?.

 Na ji sau?i Ikram.

 Allah ya ?ara maka lafiya.

Aka amsa da amin, kafin Mummy ta zauna su gaisa da Mamy tana tambayar ta jikin Rehaan Win.

Mummy ta ce, "jikin nasa ya yi kyau sosai."

Mamy ta ce, "an taki sa'a sosai."

"Haka Jafar ya faWa min, wai an bashi guba."

"Wallahi Mummy, abun babu daWin ji."

Mummy ta girgiza kai ta ce, "Allah ya basa lafiya." Suka amsa da amin.

A lokacin Riyya ta shigo da sallama, suka amsa suna kallon ta gabaWayansu. Suna haWa ido da Mummy tayi murmushi, ta ?araso kusa da ita ta ce, "Mummy sannu da zuwa."

Mummy ta dafa kafaWarta tana murmushi ta ce, "Riyya ya school?."

"Alhamdu lillah Mummy."

"Allah ya taimaka."

"Amin Mummy."

Riyya ta kalli Ikram da ta zubawa Rehaan ido tana kallonsa cikin tausayi, Riyya ta ce,  Ikram. Ikram ta kalle ta ta ce,  Sis yaushe ki ka shigo?.

 Yanzu na dawo ta kalli Mamy ta ce, "Mamy ya jikinsa, Hamma ya jikin?" Ta faWa tana ri?e hannunsa tana kallonsa.

Ya kalle ta ya ce, "I'm fine."

"Amma baka ci abinci ba."

"Bana son cin komai."

Mummy ta ce, "ai nazo maka da light food, tunda Jafar ya faWa min an bashi guba a abinda Riyya ta haWa masa, na shiga kitchen da kaina na girka maka. Tashi zaune ka ci." Mummy ta zuba masa abincin tana mi?a masa

Mamy ta karSa tana kallonsa cikin rarrashi kamar yaro ?arami ta ce, "Tashi ka ci." Ya mi?e zaune dan abincin Mummy ne bazai ?i ci ba, dan ya san wacece Mummy a gare su gabaWaya.

Mamy da kanta take feeding Winsa kamar yadda ra saba yi, ya ci kaWan ya ce ya ishe shi, ba a matsa masa ba aka ?yalesa ya jingina da gadon ya lumshe ido.

A lokacin Jafar ya shigo yana amsa waya, bayan ya gama wayar ya ?arasa inda yake ya ce, "Mamy Dr ya ce jikinsa ya yi sau?i sosai, zuwa gobe zai iya komawa gida."

Rehaan ya buWe ido ya ce, "ni a nan zan zauna, in kuma aka ce na koma gida zan tafi wajan Mummy na zauna."

Mamy ta ce, "sai ka ji sau?i sosai zan bari ka bar nan, bazai yu daga samun sau?i ace ka koma ba. Sai su bari a gama gwaji mana, a tabbatar da babu sauran gubar." Jafar jin abinda Hajiya Mamy ta ce sai ya murmusa bai ce komai ba ya juya ya fita.

? ? Har aka yi sallar magrib su Islaha basu san matakin da Baffa yake kai ba, tunda suka ga Dr Isma'il sau Waya basu kuma ganinsa ba.

Zuwa lokacin sun wahala sosai, ga gajiya ga yunwa, ga zaman waje Waya. Duk da akwai Waki na musamman da aka tanada dan zama irin wannan, ya sha kujeru da ac da komai akwai amma a gajiye suke sosai.

Islaha ta mi?e tsaye ta kalli Mama ta ce, "Mama zan je in duba likitan ko zan ganshi, ya kamata ace mun san halin da Baffa yake ciki.

Mama ta ce,  Gaskiya ne, jeki to. Islaha ta fita zuwa floor Win da suka ga Dr Isma il Wazu.

Ta je daidai inda ta ga security guard Win nan Wazu, ta sake kallon wajen ta ga suna wajen a tsaye, ta Wauke kai tana niyar waucewa ta ji wata irin ?asa dammm kamar fashewar gas cylinder.

Lokaci Waya wutar asibitin ta Wauke, inda take tsaye haya?i ya yi yawa a wajan. Tun tana korewa da hannunta har ya yi mata yawan da ta gaza yin komai. Haya?in ya yi yawa a wajen, ya girmi lafiyar ta gabbaWaya. A guje ta bar wajan tana hakki da tari, numfashinta ya fara yin sama da ?asa, tana neman inda zata ji iska mai sau?i amma ta rada

?akin da idanunta ya ganar mata kawai ta murWa handle Win ta shiga tana fitar da nunfashi sama-sama, cikin fitar hankali da ciwon da yake son sar?e ta lokaci Waya.

Nana Haleema
'

*RAGAYAR DUTSE.*

? ? ? ? ??? *Nana Haleema.*

*Book 1*
*Page 021.*


Ko da aka buWe ?ofar bai buWe ido ba dan ya yi tunanin Jafar ne, idanunsa suna a lumshe bai fahimci wutar asibitin ta Wauke ba dan idanunsa a rufe suke.

Jin shiru Jazy bai ce masa komai ba sai ya fara buWe ido a hankali, kafin ya kai idanunsa wajan ?ofa da ya gawaye, sai ya fara jin sautin fitar numfashi da?yar, alamun ko numfashin waye yana barazarar ?wacewa. Ya kalli wajan da yake jin sautin, ya hango ta a zaune a jikin ?ofar sai jan numfashi take yi, ta gigice ta fita daga hankalinta.

Ya mi?e zaune a hankali dan har lokacin yana jin ciwo a cikinsa sosai, ya bita da kallo ganin wannan dai ba Janan bace, kuma ba Riyya ba ce.

Da mamaki yake kallon Wakin ganin babu haske sai kaWan, duk da ba ya hango ta yadda ya kamata, amma ya tabbatar mace ce dan yana ganin hijjab Win jikinta.

A hankali ya tashi tsaye ya ?arasa ya buWe window yana kallon compound Win asibitin, sai ya ga gabaWaya asibitin babu wuta ta Wauke. Ya dawo da kallon sa gare ta, har lokacin jan numfashi take yi tana neman Wauki.

Ya Wan matsa tana kallon ta, a yadda take fitar da numfashin ya tabbatar masa da asthmatic patient ce, tana bu?atar inhaler, tana bu?atar iska, tana bu?atar kwantar da hankali. Asibitin babu iska tunda babu wuta, sannan bai sani ba ko tana da inhaler, gashi babu wuta balle ya saka a kira wani a taimaka mata.

A hankali yake takawa kamar ba ya so, ya dawo inda gadon yake, ya sake juyawa ya kalli Islaha yana tunanin taimakon da ya kamata ya bata, tunda numfashin nata bai Wauke ba. Ya buWe drawer ya Wauko hand oxgyen yana juyata a hannunsa, yana tunanin zata iya taimaka mata na Wan lokaci kafin wutar ta dawo.

Ya juyo ya kalli Islaha, kamar kar ya ?arasa sai kuma ya tuna shi Dr ne, taimakon mara lafiya aikinsa ne, hakan ya tako a hankali ya tsaya a inda take.

Ya zuba mata ido na wani lokaci ganin yadda yake jan numfashi da alamun ta samu attack ne, sannan ga facemask a fuskarta.

A hankali ya tsunguna a gabanta, kamar mai jin tsoron wani abun ya kai hannunsa ya zare facemask Win fuskarta, hawaye suka sakko daga idanunta da suke a kulle.

Ya saka mata oxgyen Win a hancinta ya matsa, yana taimakawa numfashinta dan ya Wan daidaita kafin hasken ya dawo. Ya zubawa fuskarta ido yana kallo, kuma ba ya ganin fuskarta yadda ya kamata, dan babu hasken da zai wadacesa har ya ga fuskarta sosai.

Idanunta yana kulle bata san waye a kusa da ita ba, neman Wauki take yi, numfashinta gab yake da tsayawa. A daidai lokacin hasken asibitin ya dawo, har lokacin yana tsugune a gabanta, duk da yadda yake jin ya takura kansa saboda ciwon cikin da yake yi, amma hakan bai saka ya mi?e ba.

Ya Waga ido ya kalli fuskar ta, duk da idanunta a rufe suke amma tsaf ya gane fuskarta, dan itace fuskar mace ta farko a duniya da ta taSa tsaya masa a rai har yake so ya sake ganinta.

Y janye ido daga kanta, a lokacin ta zame a hankali ta kwanta a wajan tana mayar da numfashi, har lokacin bata dawo normal ba, kawai ta Wan samu nutsuwa kaWan.

Ya mi?e da?yar, yana ja baya ba tare da ya juya ya kalli gabansa ba, yana tafiya yana kallon ta, ya girgiza kai yana mamakin abinda ya kawo ta asibitin har ta samu ta shigo Wakin da yake kwance.

A lokacin aka turo ?ofar aka shigo, suka haWa ido da Dr Abdul, wanda ya kasance manager na asibitin gabaWaya. Dr Abdul cikin girmamawa ya ce, "Sir, i'm sorry."

Rehaan ya koma ya zauna, ya mayar da abinda ya Wauko sannan ya ce, "me ya faru?."

"An samu fashe gas ne, sai wuta ta Wauke."

Ya girgiza kai kamar bazai yi magana ba, kafin kalle sa ya ce, "call a meeating, now."

Dr Abdul ya kalle sa, gabansa ya faWi sosai, dan ya san babu kyau tunda ya ce a haWa meeting a lokacin, da?yar bai kori wanda ya yi sakaci har aka samu wannan kuskuren ba.

Dr Abdul da girmamawa ya ce, "Okay Sir."

Har ya juya zai fita Rehaan ya ce, "wait."

Ya juyo yana kallonsa, ya nuna masa Islaha ya ce, "she had attack."

Dr ya juya kalle ta, tana kwance tana jan numfashi a hankali. Dr ya fita ya kira nurses aka Wauki Islaha suka fita da ita, ya bisu da kallo har suka Sace.

Amon muryar Jazy yake jiyowa yana zazzagawa securities masifa a waje, ya yi murmushi tare da lumshe ido, ya girgiza kai ya ce, "an taSa sarkin faWa da masifa."

Ya shafa kansa yana murmushi har lokacin, im aka cire iyayensa babu mai ?aunarsa kamar Jafar, ko su Riyya sai dai su biyo bayan Jafar. Ko yaushe yana tare dashi, ba dan neman wani abu ba, sai dan ?auna da sha?uwa mai tsanani. Duk da suna faWa, har su daina yiwa juna magana, amma haka zasu shirya su dawo a cigaba daga inda aka tsaya.

A lokacin Jazy ya shigo Wakin fuskarsa a Waure ya ce, "ta ya za a samu fashewa gas a nan? Ta ya zasu yi sakaci wuta ta Wauke?. Su kuma waWanan security guards Win na baki ?ofa, sun tafi sun bar wajan babu kowa, in plan aka haWa fa? In da gangan aka aikata fa?."

Ray buWe ido ya kalle sa bai ce komai ba, dan bai san me zai ce masa ba.? Jazy ya ja tsaki ya ce, "shirme!" Ya faWa yana zama.

Sai kuma ya kalli Ray ya ce, "kai kuma ka zuba min ido, i hope lafiya ka ke?."

Sai ya bawa Rehaan dariya, ya yi murmushi mai sauti yana kallonsa, dan yadda ya yi maganar da fusata ya ba shi dariya sosai. Sai hakan ya tuna masa wani lokaci da suke yara, in ya Sata masa rai haka yake fusata ya yi ta masifa kamar zai ci babu. Shi Rehaan bai cika faWa kamar Jafar ba, amma shine mai takalarsa har ya yi faWan. In ka ga ran Rehaan ya Saci to babban abu ne, ?aramin abu baya Sata masa rai kamae Jafar.

Ray ya Wan shafa kansa yana Wan girgiza kai kafin ya ce, "i've called for a meeting, let's go" ya faWa yana mi?ewa tsaye da?yar.

Jazy ya bi shi da harara ya ce, "baka da lafiyar zaka iya wani meeting, Kai wai baka da hankali ne?."

Ray ya sake yin murmushi yana kallon sa ya ce, "bani dashi Jazy. Let's go."

"Wait! An ce wata yarinya ta shigo nan, ka ganta?." Ray ya kalli Inda ta kwanta, yana hango yadda hawaye yake sakkowa daga idanunta saboda attack Win da ta samu.

Jazy ya ja tsaki ya ce, "ban ga amfanin mutanen nan ba, har su bar wata mace, wacce bamu san wacece ba ta shigo nan. Wai sun tafi bada taimako inda gas Win ya fashe, ko waye ya aike su oho."

Shi dai bai ce komai ba, ya yi shiru yana kallon inda Islaha ta tashi, yana sake tuna fuskarta a hotel da fuskarta ta yau.

Jazy ya taSa shi ganin ya zubawa waje Waya ido ya ce, "Mr man ina magana ka yi min shiru, baka jina ne?."

Ray ya kalle shi ya ce, "sai masifa ka ke yi, me ka ke so in ce?."

"Sai ka ?yale ni cigaba da yi, da yake mahaukaci ko?."

Ya sake bashi dariya, ya sake murmusawa sannan ya ce, "Mu je."

Har zasu fita Ray ya dawo, ya Wauki jacket Winsa ya Wora akan kayan jikinsa, hular da take baya ya saka ta a kansa sannan suka fita.

Islaha kuwa ana fita daga ita daga Wakin, aka kai ta aka bata taimakon da ya kamata har ta dawo nutsuwar ta.

Islaha ta mi?e zaune ta kalli Nurse Win ta ce, "Don Allah ina Dr Isma'il yake?."

Nurse Win ya ce, "Sun shiga meeting, amma baza su jima ba. Ki kwanta ki huta."

Ta mi?e tsaye, ta Wauki hijjab Winta da aka cire mata ta saka, ta saka takalmanta da ta gansu a wajan a ajjiye ta ce, "i'm okay, thank you." Tana faWa tana fitowa ta koma inda su Mama suke ta gansu a zaune harda Sadik.

Suna hango ta Sadik ya mi?e ya ce, "Ina kika shiga?."

Ta Wan sauke numfashi a sanyaye ta ce, "haya?in nan na Wazu ne ya saka na Wan samu attack, ni kaina bazan ce ga yanayin da na kasance ba. Ina Baffa? Ka haWu da Dr?."

"An ce sun shiga meeting" ya faWa yana mi?a mata wata leda ya ce, "da yake asibitin na masu kuWi, akwai lafiyayyen entry da ake siyar da abinci, kuma na ji ance ga wanda zai zauna jinyar mara lafiya, da mara lafiyar abinci kyauta ne. KarSi ki ci, ke ce baki ci komai ba duk mun ci."

Ta mi?a hannu ta karSa tana jin jiri yana Waukar ta ta ce, "wallahi bana jin yunwar, so nake mu san yanayin da Baffa yake ciki."

Labiba ta ce, "gwara dai, dan wallahi na gaji gida nake so naje na kwanta na huta. Ita waccen sagalalliyar har yanzu bata zo ba."

Islaha zata yi magana Adda Sa'ida ta ?araso wajan, ta ce, "Islaha tunda nazo ban ganki ba."

Islaha da fara'a ta ce, "Yaushe ki ka zo Adda?."

"Ban wani jima sosai ba, na je nayi sallar i'sha ne."

"Lah nima ban yi sallah ba, bara na je na yi na dawo" ta faWa tana juyawa a sanyaye tana jan numfashi a hankali. Sai da ta shiga restroom Win asibitin ta ga yanayin fuskarta, hijjab Winta duk ya ji?e da gumi. Ta Wan gyara fuskarta, ta mayar da facemask Winta sannan ta fito.

Tana shiga masallacin lafiyayyen ?hamshi ya yi mata sallama, bata tsaya ?are masa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login