Showing 51001 words to 54000 words out of 96103 words

Chapter 18 - RAGAYAR DUTSE BOOK 1 COMPLETE

25 Aug 2026

61

yake hannunta ta ce, "da wa da waye a Wakin lokacin da take tambayarta?."

"Duk an tafi wajan cin abinci, daga ita sai ita sai ni."

Ta da ki table ta ce, "Yarinyar nan tana ?o?arin wuce tunanin mu fa. Amma kin hana Zainab magana da ita ko?."

"E na hana, amma already ta riga ta faWa mata Hafsa bata nan. Wai Mama babu ta yadda za a hanata shigo gidan nan? Babu hanyar da za a bi a hanata zuwa gidan nan tunda ba a gidan take ba yanzu?."

Mama ta girgiza kai ta ce, "na san abinda zan yi mata Fadwa, na san maganinta. Abinda nake so dake, duk bala'i kar ku faWa mata komai, ku iya bakinku dan yarinyar nan shaiWaniya ce, kuma ?ar jarida ce, zata iya tarwatsa mana komai."

Fadwa ta ce, "To Mama."

Mama ta ce, "ki faWawa sauran, ko da yake in anjima ki turo min su ina da meeting dasu" ta faWa tana Waukar ruwa ta sha ita kuma Fadwa ta fita.

Ta girgiza kai ta ce, "sai na yi maganin yarinyar nan, na daina saurara mata, lokacin da zan Satar da ita ya yi ta faWa tana Waukar waya da niyar yin kira.

Islaha kuwa ko da ta fita napep ta tare kai tsaye ta koma hotel Win da suka baro. Ta rufe fuska da facemask ta shiga ta wuce har floor Win da ta ga Hafsa.

A nesa da Wakin ta tsaya, ta saka waya a kunne kamar tana amsa waya tana satar kallon Wakin, ta cigaba da kallon wajan tana Wan yin waya kamar mai yin wayar gaske.

Kamar a mafarki aka buWe ?ofar Wakin, da sauri ta sauke wayar daga kunnenta ta shiga camera ta cire flash light, ta mayar da wayar kunne kamar tana waya.

A lokacin Hafsa ita da wani suka fito, Hafsa ta Soye fuskarta da facemask, sai wanda suke tare shima ya rufe fuskarsa da facemask.

Islaha ta juya ta cigaba da yin video da hotuna har suka wuce, da sauri ta yi kamar zata koma ciki, har sai da suka sauka, ta tabbatar sun fita sannan ta fito ta fita daga hotel Win.

Napep ta sake tarewa ta shiga, ta tafi tana tunanin abinda ta gani wanda ya Waure mata kai ya kuma bata mamaki mai yawa.

Me Hafsa ta zo yi hotel ita da wani? Kuma gashi a gidan an san bata nan balle ta ce zuwan kai da kai ne, har ana cewa da Mama suka fita.

Ta girgiza kai a bayyane ta ce, "Allah ka kiyaye yaran nan daga abinda nake zargi, Allah ka tsare maraicinsu.

Ta shafa fuskar ta ta ce,  ko iya haka na samu hujja mai ?arfi."

Ta cigaba da kallon titi suna tafiya, tunanin ya ?i barin zuciyarta da idanunta, ko ya ta rufe ido Hafsa take gani ita da wanda bata san waye ba, gabaWaya ta takura ta rasa abinda zata yi.

Suna cikin tafiya wata dattijuwa ce ta zo tsallaka titin, ?iris ya rage mai napep Win ya buge ta, dan ya Wan taSa ta har ta faWi a ?asa.

Islaha cikin kiWima ta ce, "Subahanallahi! Malam tsaya."

Mai napep Win ya tsaya, ita kuma ta sauka ta nufi wajan matar da hanzaru, dan daga ganinta ka san ta girma sosai, tana bu?atar taimako.

Nana Haleema
'

*RAGAYAR DUTSE.*

?? *Nana Haleema.*

*Book 1*
*Page 014.*

SCENT BY SAPNAH BORNO.

Hajiya ta kina son gidan ki yayi Kamshi? Kina so kiyi wannan kamshin irin na matan borno? Kina so tun kafin isowarki waje k amshin kabbasar ki ta rigaki isowa? To indai wannan ne kizo scents by Sapnah Borno, zaki samu fiyeda yadda kike bukata da yardar Allah.
Sapnah takawo muku turaren kabbasa irin na manyan matan Borno Wanda ko turara Kaya kikayi indai kika zauna waje sai kin bar kamshin ki, tanada kabbasa spray mai musulmin dad i, sannan tanada turarukan wuta masu bada nutsuwa, bata tsaya iya wannan ba tana saida ready to use dilka, sannan tana zuwa duk garin da mutum yake tayi gyaran amarya, abubuwan datake saida su suna nan kamar haka.

Kabbasa spray
Dufr khumrah
Mahlab khumra
Body milk
Kuleccam
Matan Maiduguri
Ready to use dilka
Halawa
Shuwa Arab hair mist
Cotton incense
Dorut after period
Dukhaan stool
Gabgab
Sandal flex
Sandal sukkaria
Kajiji
Halud
Arabian oud
Oil perfume
Room fresh
Multi purpose sprays
Curtains incense
Kabbasa
Farce
Marshoosh
Senegalese Kajiji
Dilka soap
Dilka cream

Tana nation wide delivery ko wacce k asa. Sannan Tana promo a yanzu haka, karku sake a Baku lbr.

Zaku sameta ta wannan number Kai tsaye 08093772168
08164570032

____________________

Islaha ta ri?o matar ganinta zube a ?asa ta ce, "Mama Sannu, baki ji ciwo ba?."

Daada ta Wago kai ta kalli Islaha ta ce, "Ba ku yi min komai ba, gajiya ce kawai.

Islaha ta ce, "To Mama mi?e tsaye, magrib ta yi kina yawo ke kaWai."

Ta ri?e Daada suka mi?e tsaye ta ce, "Mama a ina ki ke?."

Ta kalli Islaha ta ce, "kaina ne ya juye, na rasa ina zan je."

Islaha ta ce, "mu shiga napep sai a sauke ki a gida." Islaha ta taimaka mata ta shiga sannan itama ta shiga.

Sai da suka fara tafiya sannan Islaha ta ce,  Mama ina za a kai ki?."

Daada ta yi shiru tana tuna sunan unguwar, sai daga baya ta ce,  Mafi a.

Islaha ta ce,  Malam kai mu Mafi as quarters.

Daada ta kalli Islaha tana murmushi ta ce, "na gode jikata, ba ko wanne yaran yanzu ake samu masu tausayin tsoho ba. Ya sunanki?."

Islaha ta yi murmushi ta ce, "Sunana Islaha."

Daada ta ce, "Ishlaya?."

Islaha ta Wan yi dariya jin yadda ta faWi sunan abin dariya, ta ce, "Is...la...ha" ta faWa a rarrabe yadda zata gane

Daada itama a rabe kamar yadda Islaha ta yi ta ce, "Ish...la....ya."

Islaha ta yi dariya ta ce, "ki ce min jikar ki kawai Mama."

Daada ta yi murmushi ta ce, "sunan na yara ne irin ku. Na gode jikata, yaran yanzu ba kowa ne mai tausayi ba. Na ji daWin taimakon ki sosai."

Islaha ta yi murmushi ta ce, "babu komai Mama, ai kamar kakata ki ke."

Daada ta yi dariyar jin daWi, tana kallon Islaha ta ce, "Gaki nan ba?ar bafulatana, kyakyakawa ma sha Allah. Ga kyau ga kirki, ga tarbiyya da sanin darajar tsoho. Islaha ta sake yin murmushi bata ce komai ba.

Daada ta ce,  Kina da aure?."

Ta girgiza kai tana murmushi ta ce, "bani dashi Mama."

"ai kuwa na samarwa jikana mata, daman yarinya mai hankali da tarbiyya nake nemar masa, kuma gaki na samu. Shikenan sai a yi bikin a huta.

Islaha ta kuma yin dariya sosai ta ce, "Hajiya Mama kenan."


"Da gaske nake jikata, daman ina so na samar masa yarinya jinin fulani mai tarbiyya, kuma ga ki na samu."

"Mama ni an kusa bikina."

"Sai a fasa auren da wancan, jikana Muhammad zaki aura ba wani ba."

Islaha ta sake yin dariya bata ce komai ba, dan bata Wauki maganar da gaske ba, ta san irin wasan tsofaffi ne da suka saba.

Mai napep ya ce, "mun shigo unguwar."

Islaha ta ce, "Mama mun shiga unguwar, a ina za a ajjiye ki?."

Ta kalle ta ta ce, "gidan Wana AbdulAziz."

"Ina kenan?."

"A nan unguwar ya ke, kawai gidan Wana."

Islaha ta girgiza kai ta kalli mai Napep ta ce, "ka san gidan?."

Ya girgiza kai ya ce, "wallahi ban sani ba."

Ta ce, "ka Wan tambaya, ba za a rasa sani ba."

Ya fita ya je wajan wani mai gadin wani gida ya tambaye sa yana nuna masa Hajiya, yana ganinta ya gane ta ya kuma yi masa kwantance estate Win.

Ya dawo ya shiga ya ce, "ai mun kusa, gashi layin gidan can."

Yana karya kwana zai shiga estate Win aka hanasu ?arasawa saboda security da yake wajan.

Islaha ta kalli Daada ta ce, "Maman hana mu wucewa, wai sai dai mu wuce da ?afa."

Sai a lokacin Daada ta kalli wajan ta ce, "in ji ubanwa? Matsa na fita ki gani."

Islaha ta ce, "A'a Mama ki zauna, bara na yi musu magana."

Daada ta ce, "ke dai bani hanya." Islaha ta fita itama ta fito.


Daada ta kalli Waya daga cikin masu tsaron ta ce, "waye ya ce bazan wuce ba? Na ce waye ya ce bazan wuce na shiga ba?."

Ya kalle ta ya ce, "Kaka ba a shiga da napep wajan nan, sai dai ku wuce da ?afa."

"In ji wa? Wallahi da babur Win zan shiga har gidan nan, sai naga wanda ya isa ya hana ni."

Islaha ta bita da kallon mamaki, ganin tsohuwa da ita faWa da neman rigima kamar bata girma ba.

Islaha ta ri?e ta ta ce, "Mama ki tsaya, ba a wasa da irin wajan nan, zasu iya harbin ki. Mu je sai in raka ki har cikin gidan."

Daada ta kalle ta ta ce, "nida gidan Wana a ace bazan shiga ba? Sun isa su hana ni wuce?."

Ta kalli mai Napep Win ta ce, "Mai babur mu je, sai na ga wanda ya isa ya hana ni shigewa ciki."

?aya daga cikinsu ya ?araso yana Waga bindinga sama ya ce, "Mama ki koma, ba a wucewa da keke, sai dai a ?asa."

Daada ta tsuguna ta buga ?asa ta ce, "wallahi sai na shiga da babur Win nan, in ban shiga dashi ba ku ce ban haifu ba..."

Ta kalli Waya daga cikinsu ta ce, "Kai shiga gidan nan, ka ce AbdulAziz ya zo in ji ni."

Shugaban masu gadin gidan ya ?araso da sauri ya du?a mata ya ce, "Daada barka da zuwa."

Ta kalle shi ta ce, "yauwa Sulaimanu, shiga gida ka kira min AbdulAziz, ka ce yazo ina nemansa."

Ya du?a da girmamawa ya ce, "Ba ya nan Daada."

Ta ?arasa kan wani tudu na dutse ta zauna ta ce, "zan jira sa a nan, babu inda zan je sai na nuna musu matsayin da nake dashi. Duk sai na saka an kore su, zasu san sun wula?anta ni, har suna nuna ni da bindiga."

Islaha ta dafe kai, tana mamakin wannan faWa na tsohuwa kamar ba babba ba. Ga rigima da Worawa kai, in banda rigima ina ita ina faWa da masu tsaron hanya.

Islaha ta duba agogo ta ga lokacin sallah har ya wuce bata yi sallah ba, ta kalli Daada ta ce, "Mama ni zan wuce, sauri nake yi."

Ta ta ri?o ta ta ce, "babu inda zaki je, sai kin shiga cikin gidan nan a wannan babur Win."

Mai gadin ne ya yi musu bayanin wacece a gidan, duk sai suka rikice, suka ruWe, gashi ta ce sai ta saka an kore su.

Cikin taushin murya guda Waya ya ce, "Ki yi ha?uri Hajiya, ba mu san ke bace, duk muna wannan abun ne saboda tsaoron lafiyar ku."

Ta hararesa sannan ta kalli mai gadi ta ce, "jinin indiyawa ya dawo ko?."

"eh ya dawo Hajiya."

"Ai na san sai shi, zuwansa ne kawai zai saka a tsayar daku a wajan nan kamar wani zuwan shugaban ?asa. Ku je gidan ku kira min Muhammadun, ya zo ya shiga cikin babur Win da kansa, mu shiga gidan a tare."

"Ki yi ha?uri Hajiya."

A fusace ta nuna su ta ce, "kuma duk sai na saka ya kore ku wallahi."

Suka haWa baki wajan faWin, "Ki yi ha?uri Hajiya, shiga babur Win sai ku wuce."

Ta harare su ta ce, "Sai da ku ka wula?anta ni? Nima sai na wula?anta ku sannan zan shiga."

Suka dinga bata ha?uri tana shan ?hamshi, da?yar aka samu Daada ta shiga Napep Win nan, Islaha ma ta shiga aka buWe musu suka wuce aka shiga da Napep Win har cikin gidan.

Islaha tunda suka shiga take kallon gidan saboda girma da kyau, duk da ta taSa shiga government house, ta shiga manyan gidaje sosai, amma wannan ya fi burge ta akan ko wanne gida. Ga motoci a zube kamar ba a so, ko ina mota ce babba da ?arama.

Lokaci kaWan jikokinta suka baibaye wajan, suna haWa baki suna cewa, "Daada ina ki ka tafi ke kaWai? Abba yana ta neman ki."

Islaha ta fito tana kallonsu, musamman Banisha da take ta dariya kanta babu Wankwali.

Sai ta ji yarinyar ta burge ta, kana kallon ta ka san ruwa biyu ce, iya gashinta ya gwada hakan, dan bai yi kama da na fulani ba. Islaha ta zuba mata ido tana kallonta, gata yar duma-duma, irin yaran masu kuWin nan.

Bashisha ta kalle ta ganin tana kallon ta, sai ta ce, "Sannu."

Islaha ta yi murmushi ta ce, "yauwa."

Sai kuma ta kalli Islaha ta ce, "kamar na san ki, Islaha ko?."

Islaha ta yi murmsuhi ta ce, "haka ne.

Ta Wan buWe ido ta ce, "Wow, na ji daWin ganinki. Ina ganin programs Winki a tiktok" ta faWa tana bata hannu alamun su gaisa.

Islaha ta saka hannunts a cikin na Banisha tana murmushi.

_Kai, ka ji hannun yarinya da shegen laushi._

Islaha ta furta tana sake kallon Banisha tana ayyana Allah ya yi mana arzu?i a ranta.

Banisha ta ce, "Sunana Banisha" kafin ta bata amsa ta tafi a guje ta yi cikin gidan tana kwalla ihu kamar ?aramar yarinya.

Ta bita da kallo tana murmushi, tana sake maimaita sunan Banisha, tana aiyana su fa ?a?a masu kuWin nan gudu ba komai ne a wajansu ba, duk shekarun mace dan ta yi gudu abu ne mai sau?i a wajansu.

Islaha ganin Daada ta yi gaba ita da jikokinta, sai ta koma cikin Napep Win ta ce, "Yi ha?uri Malam, juya mu koma kawai bana son Sata lokaci."

Ya ce, "Hajiya ai da kin shiga, baki san alkhairi da zata yi miki ba."

"In rabona ne zai kira ni, mu je kawai." Bai musa ba ya ja napep Win ya juya suka fita daga gidan.

Daada tana shiga Sangarenta Abba ya shigo, sai da ta samu waje ta zauna sannan ya ce, "Daada ina ki ka je ke kaWai? Hankalina ya tashi, tun Wazu na fita ina neman ki, na rasa inda ki ka nufa."

Ta yi shiru bata ce komai ba, sai ta kalli ?ofa ta ce, "ina yarinyar da ta dawo dani ta ke?."

Ya kalli ?ofa shima ya ce, "babu kowa a nan."

"Akwai yarinya da mu ka dawo tare, tana ina?."

Kafin ya yi magana aka shigo da sallaama, ta amsa ta ce, "Ke ina yarinyar da muka shigo da ita a babur?."

Ta ce, "Daada ai sun tafi, tun kafin ki ?araso suka hau babur Win suka tafi."

Daada ta ce, "Sun tafi fa ki ka ce, ta tafi ba tare da mun yi sallama ba? A yi maza a bi bayanta a nemo min ita yanzun nan."

Janan ta ce, "Daada a ina za a ganta? Ai kawai ki ?yaleta."

"Bazan ?yale ta ba, aje a nemo min ita,
ko ni na tashi naje na nemo ta" ta faWa tana mi?ewa.

Abba ya ce, "A'a, baza a yi haka ba. Janan je ki ki faWawa drivern Daada, ya bi bayansu ko zai gansu."

Janan ta juya ta fita tana ?un?uni, banda rigima irin ta Daada ko a ina za a gansu oho.

Abba ya ce, "Sannu Daada." Ta Waga masa kai tana shan ruwa.

Abba ya ce, "Don girman Allah ki daina fita ke kaWai, ban san kin fita ba, sai da na tambaya masu gadi suke ce min wai kin fita a keke. Don Allah ki daina fita ke kaWai, tunda an girma."

Daada ta ce, "na tashi ina son na yi ziyara, na tashi ina son na je dubiya matanka duk sun aiki direbobin. Ita waccan ishahshiyar da yake tafi kowa mutum biyu ta aika, Waya ma ta aiki wani. To ya ka ke so nayi? Ina da mai kai ni ne?."

Abba ya ce, "sai a buga min waya Daada, ko a tura cikin gida, in da wani yaron sai ya kai ki. Amma fitar ki ke kaWai bai kamata ba."

"Ni fa dan na fita ni kaWai babu abinda zai ci ni, kawai wannan juyewar kan da nake fama dashi ne matsalata. ?azun ma juyewa kaina ya yi da zan dawo, sai wannan yarinya ce, meye ma sunanta...." Ta faWa tana tafiya tunani.

Sai kuma ta ce, "Ishlaya. Yarinya ?ar albarka, itace ta sako ni a babur har gidan nan. Amma da yake wancan yaron ya dawo, muna zuwa wai aka hanani shigowa gidan nan."

Abba ya Wan sauke numfashi ya ce, "ki yi ha?uri, duk akan tsaron lafiyarku ne ya saka aka ajjiye jami'an."

"Tsaron lafiyarsa dai, dan sai ya dawo ake wannan dafifin a ?ofar gidan nan."

"Ki yi ha?uri, zan samar miki da driver da zai dinga kai ki duk inda ki ke so. Na ki ne ke kaWai, duk wacce ta aike sa bazai je ba."

Daada ta taSe baki ta ce, "ban yi sallah ba, zan shiga in yi sallah. Kafin na fito a nemo Ishlaya, sannan in an idar da sallar i'sha ka kira min ba?on da ya dawo yau, ka tattaro min kan kowa ina da magana.."

Abba ya mi?e kamar yadda ta mi?e ya ce, "in sha Allah." Shi ya ri?e ta har Wakinta, ta shiga ta yi alwala ta fito ta tayar da sallah sannan ya fita.

Yana komawa part Winsa Rehaan ya shiga part da sallama. Abba ya amsa yana kallonsa ganin fuskarsa ta yi ja, kana ganinsa ka san bashi da lafiya. Abba ya girgiza kai, dan ya san daman sai anyi haka, da wahala Rehaan ya dawo bai yi ciwo ba.

Ya taka a hankali ya zauna a kan carpet ya ce, "Abba barka da dare" ya faWa cikin yaren fulani, dan Abba ya fi so ya yi masa magana da yaren.

Abba ya amsa yana kallonsa ya ce, "Rehaan an dawo lafiya?."

Ya Wan dafe kansa sananan ya Waga kai ya ce, "Lafiya lau Abba."

"Ya dai, Lafiya ka ke?."

"Kaina yana ciwo Abba" ya faWa yana dafe kansa da hannu Waya yana sauke numfashi a hankali.

Abba ya bi sa da kallo tausayi ya ce, "sannu, ka je ka sha magani sai ka kwanta. Sannan ka tabbatar da ka yi addu'a."

A sanyaye ya ce, "To."

Abba ya bishi da kallo, a sanyaye ya ce, "Rehaan kasan za a yi faWa da Daada akan gashin nan naka ko? Meyasa baka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login