Showing 129001 words to 132000 words out of 188421 words
555 3736: π *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*π
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 61*
Ba wannan ba gaba daya....,can wani sashe na zuciyarta ke tuna mata WAYESHI?. Da kalar wannan izzar da kusancin da yakeji ya samu zaya yarda da sharuddanta?. Tambayar data jefawa tafisu kenan.
"Yana da wata irin izza da girman kai na banza tunda ba kowan kowa bane.....ina hangen wani irin taurin kai a tattare dashi tafisu.....ina ganin koda zai amince bazai yarda ya karba sharuddana da auren ta cikin sauqi ba". Wani murmushi dake gayawa mammina tafisu tana da kowacce mafita ta matsala da zata tunkarosu ta saki.
"Ba wanda yafi qarfin barazana da takan iya juyewa ta zama gaske.....indai ba daga sama ya fado ba ai yana da ahali.....idan baida mahaifiya yana da mahaifi,idan duka babu akwai makusanta......ki tabbatar masa da daukan rayuwarsu daya bayan daya har sai sanda ya aminta da sharudanki,ruwansa ya karbi ladansa ruwansa kada ya karba". Ta fada hankali kwance.
Kai mammina ta girgiza
"Banajin barazana zata juya wannan.....amma a maganganunki na tanadi hanyoyi biyu da zan sashi karbar buqatata ta ruwan sanyi" Ta furta tana sakin qaramin murmushi.
"Ki samomin qaramin malami,ina buqatar wasu ayoyi da hadisai da zan riqe koda qananu ne"
"An gama" Tafisu ta amsa tana rusunar da kanta.
*MORSA SAFIYYA*
Ta jima tana maimaita innalillahi din,har zuwa sanda taji wata nutsuwa ta soma saukar mata a zuciyarta a hankali.
"Rakani armelle......inaso na ganta" Ta fadi tana miqewa daga kan kujerar,tana kuma jin jiri kamar zai kayar da ita.
Tafiya kawai takeyi amma tana jin kamar tana taka qasa ba daidai ba. Takawa take da wani irin yanayin da takeji kamar iskar daminar dake kadawa zata kayar da ita
Qirjinta da zuciyarta a quntace,idanunta suna dauko mata shekarun baya. Sanda safeena ta amsa sunan BAZAWARA a qasa da shekara daya tal da aure.....bata fata hakan ta kasance akan akhnan,bata fata itama wannan sunan ya bita,duk da cewa ta sani basu riga da sunkaita gidanta ba,amma bata da tabbacin dukkan abinda ya faru a bayan idanunta.
Da idanunta take hangen tsaiwar jama'a biyu uku daga taku xuwa wani takun nata. Mafi yawancinsu mata ne,kuma a take jikinta ya fara gaya mata suna tattaunawa ne kan al'amarin,tabbacin magana ya fara yaduwa kenan,abinda ya sake quntata qirjinta.
*AKHNAN*
Duhun da dakin yake dashi a yanayin yafi mata komai dadi,tanajin kamar ta tserewa duk wani kallo na tuhuma ko tozartarci da zata iya fuskanta.
A wani irin soye takejin zuciyarta da wani irin yanayi da ba zata tantance wanne iri bane. Abu daya da takejin yana zagayawa a jikinta da zuciyarta gaba daya shine TOZARCI da QASQANCIN da almaz ga ajiye mata cikin tarihin rayuwarta,wani irin mummunan tarihi data tabbatar har a gama sarauta a agadez ba za'a manta da ita ba.
Wannan shine ABINDA TAKE GUDU shine abinda ya sanya taketa gudun wuce sa'a tsakaninta da kalmar AURE. Ta sani cewa,ba komai a cikinsa sai tarin bin umarni da barin dukkan wani da zuciya keso ko muradi ko kuma buri,dukka don kawai ka cika muradin NAMIJI. Mammina da sultane tana iya kiransu da cewa SUNE SILA......duk da ta fannin sultane tana masa uzuri da cewa ZIGA ce da qoqarin shiga tsakaninsu da akeyi tun can can.
Amma ta fuskar mammina fa?......makancewa tayi?,tunaninta ya gushe ne data dauko makakke mashayi ta damqa ragamar igiyar aurenta a hannunsa?.
Me yasa mammina bata qure duba cancanta ba?,me yasa bata zagaye kusan rabin duniya ba saboda ita?....me yasa?.....me yahau kanta ta zabo mata mutumin daya munana kyakkyawan tarihinta?.
A hankali morsa safiyya ta murda qofar dakin tana shigowa idanunta zube akan akhnan din. Kallon kusan sakanni talatin tayi mata sannan ta saki qofar tana takowa a hankali zuwa inda akhnan din ke zaune.
Fuskarta tayi wani fayau a iya awannin kawai.....wannan blue eyes din sun rune da surkin jaja jaja a cikinsu. Kusa da window take zaune,saidai ba dukkanin fuskarta bane ke kallon window din. Sosai morsa safiyya ke hangen wani irin yanayi tattare da akhnan din,yanayin data tabbatar UWA ce kawai zata iya hangensa akan d'iyarta. A firgice take gaba dayanta,saidau rashin sanin makomar rayuwarta da abinda ke mata ciwo da zafi........abubuwan da suka cancanta da rayuwarta gaba daya ya sanya bata fahimci komai ba,ta yanke kebe kanta a matsayin wani hukunci daya dace da ita. Tana iya hangen yanayin cikin idanun akhnan din,kamar an qara mata shekaru tsakanin kwanaki ukun da aka daura mata aure. Ta sake zama wata mutual data tabbatar girman igiyar data yanke cikin kwanaki uku ne ya haifar da hakan.
Har cikin jikinta taji shigowar morsa safiyyan,saidai zuciyarta na gaya mata ne.....ta shigo taga fitar hawaye ne daga idanunta?....kota shigo ta nuna farincikinta na mummunan abinda ya sameta?.....ko ta shigo ta bayyana mata cewa ta samu nasara a dukka shirinta.
Yanayin akhnan bai hana morsa safiyya kusanta kanta da ita ba,daga can qasan zuciyarta takejin wani irin rauni,yanayin yana daukota mata hoton safeena sak a irin wadancan shekarun tun kafin samuwar akhnan din.
Bata dakata ba har sai data isa dab da akhnan din,a nutse ta zauna saman kujerar dake fuskarta ta,kujeru qwara biyun da aka ajiyesu kawai a gurin me dauke da qaramin table a tsakiya.
"Ba buqatar ki tambayeni komai......labari nasan ya riskeki,ba sai kin taso ganin hawaye a idanuna ba kafin ki samu tabbaci.....da gaske ya sakeni,ya sakeni saki uku.....shikenan dukkan wani fata da buri sun gama cika?" Akhnan ta fada da wata murya me nauyi,wanda duk daga harshen da zatayi wani irin d'aci takeji yana sauka saman harshen nata.
Mamaki sosai ya saukarwa morsa safiyya,saidai har yanzu tana jin cewa ita din UWA ce......a yanzu ne kuma takejin lokaci yayi da zata kusantar da kanta da rayuwar akhnan din,wannan zargin da wannan zaton da take mata tana jin ya kamata ta maidashi reality.....abu d'aya daya rage tayi,koda zata zargeta......koda zata tuhumeta nan gaba ko bayan babu ranta zatasan bata da wata UWA a duniya bayan ita.
"Ba wata uwa dake burin ganin ibtila'i cikin rayuwar d'iyarta........sau da dama fuskokin dake murmushi a garemu ba sune asalin fuskokin masoyanmu ba......hannuwan dake miqo kansu garemu,ba sune hannayen daya cancanci mu kama mu riqe don samun kubuta da tsira ba,wani lokaci suke fincikarmu zuwa ga shiga kowacce matsala da muke tsintar kanmu a ciki.......na samu amsar tambayar farko daga gareki" Morsa ta fadi da wani irin yanayi da akhnan din bata taba jin morsa safiyya din tayi magana dashi ba.
Bata sake cewa komai ba,taci gaba da kallon akhnan din tana karantar wasu halaye da akayi mata horo dasu. Tana daukan nesanta kai a matsayin AMINCI,shi yasa koda wanne lokaci take zabar nesanta kanta da kowa da komai idan tashin hankali ya sameta.....saidai ba haka siddan aka koya mata hakan ba,an koya mata hakanne saboda ta zama me karbar kowacce shawara idan aka kusanceta da shawarar.......ta zama me ragaggun hanyoyin samawa kanta da zabawa kanta abubuwan da suka dace.
"Zanyi nesa dake,don na samu tabbacin bai taba lafiyarki ba.....to alhamdulillah.....amma hakan ba yana nufin zanyi nesa da rayuwarki ba,zan zama maras abun cewa akan abinda ya shafi rayuwarki......sam sam.....tun kina qaramarki akwai wani SHAMAKI da aka sanya tsakanina dake......akwai wanda yake kururuta samuwar TSORO cikin kunnuwanki.......akwai wanda ya koya miki ganin ABOKAN GABA DA ADAWA a inda sam sam babu su........a wannan lokacin zan kasance tare dake koda ban zauna kusa dake ba......zan kasance me ruwa da tsaki gurin yanke hukunci akan RAYUWARKI ta gaba.....koda hakan yaha nufin ba zaki sake kallona a matsayin QANWAR SAFEENA ba har abada......ban damu ba muddin zan bawa jinin safeena qwaya daya tal daya rage kariya.....banzo don na zauna nayita tambayarki ba......don iya abinda nakeji game da sakinki na tabbatar KARIYA ce ubangiji ya baki,duk da ke a wajenki zai miki kama da MASIFA da TASHIN HANKALI.....tambayata guda daya ce......kun hada jiki dashi ko baku hada ba?" Morsa ta yiwa akhnan tambayar kai tsaye tana tsareta da wani irin zazzafan kallo.
Da sauri ta daga kanta zuwa ga morsa safiyya,zuciyarta na tafasa tana amsar duk wata magana data fita a bakinta tana farfasata,ba abinda zuciyarta ke gaya mata illa mammina take toxartawa da kalamanta. A qasan ranta karon farko tunda ta zauna a gurin tana jin wani zafin mammina ne a ranta akan zaben data mata,tana jin a wannan karon tana da tarin tambayoyin da zata yiwa mammina akan mijin data zaba mata......amma batasan me yasa takejin zafi da baqar magana ko baqar kalma guda daya da aka gaya mata ba.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Ta daga kai ne da niyyar tsare morsa safiyya da kallon da zai sanya ta fahimci ita din ba kowa bace da zata tasata a gaba da wannan tambayar,ba huruminta bane wannan bata da wannan ikon,amma kuma a yau a karon farko kallon dake cikin idanun morsa safiyya din wasu iri ne......wani kallo ne na daban daya sanyata dole ta juyar da fuskarta gefe tana jin wani abu me kama da tsananin nauyi yana sauka a idanunta da zuciyarta,tana kuma jin girman tambayar da nauyinta.
Siririn numfashi kawai morsa safiyya ta sauke,koda akwai rashin kunya da izza a idanun akhnan,amma ta gama samun amsar ba abinda ya hadata da almaz.
"Alhamdulillah" Ta furta a hankali tana miqewa. Hamdalar ta sake jawo hankalin akhnan din,me take nufi matar?,tana murna kenan da abinda ya sameta?. Me yasa wai ba zata canza ba?,me yasa ma take kiran kanta a matsayin qanwar mahaifiyarta?,bayan tana maraba da duk wani bala'i da zai sameta?.
Har cikin zuciyarta takejin wata nutsuwa tana saukar mata,duk wani tashin hankalinta akan auren yana sake gushewa,tana sake gasgata girman ubangiji da buwayarsa,komai zaiyi akwai hikimarsa a ciki amma ga ma'abota hankali.
*MAMMINA*
Sai data koma sassanta ta sauya shigar jikinta sannan ta nufi sassan akhnan. Sassan da tana sanya qafarta zata shiga morsa safiyya na fitowa da tata,saita samu kanta da wani irin faduwar gaba.
Bin juna sukayi da kallon kallo,zuciyar mammina cike da fargaba da shakku gami da tarin tambayoyin me yakai.morsa safiyya din sashen akhnan haka da wurwuri daga faruwar abun? Kada Allah ya bawa akhnan damar furta komai ga morsa safiyya din,duk da tana da yaqini,tasan abune me wahalar gaske wata magana ta shaquwa ko fahimtar juna ta shiga tsakaninsu. Ta dade da kashe wannan feeling din a tsakaninsu,ta dade da cusawa akhnan ra'ayi da hali na tsananin qyamar morsa safiyya da kuma sanyata a sahun farko na maqiyanta. To amma a yanzu bata da tabbas akan kowa da komai,har saita saita komai yadda takeso yaci gaba da kasancewa.
Sassanyan murmushi morsa safiyya ta saukewa mammina sannan a hankali ta dauke kanta tana fita a gurin cikin cikakkiyar nutsuwar nan tata data jima tana huda zuciyar mammina din..
Raga raga murmushin yayi da zuciyar mammina......ya sake ajiye wata qatuwar fargaba da kuma rashin tabbas a cikin zuciyarta,wannan ya qara mata qaimin sanya kai zuwa sassan akhnan da sassarfa.
Fitar morsa safiyya ta barta da wani irin tunani me zurfin gaske a kanta,tunanin da baiyi zurfi ba taji muryar mammina tana qwala mata kira da wannan muryar da kowanne lokaci take nuna zallar tashin hankali akan dukkan wani mummunan abu da zai sameta.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer π³πͺ*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITAπ*
*HUGUMANKU CE*βπ½
[2/4, 19:51] +234 903 555 3736: π *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*π
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 62*
Idanunta ta lumshe kawai ba tare data waiwaya ba,idanunta ta lumshe kawai tana ci gaba da sauraron muryar mammina din maimakon ta tashi ta fada jikinta kamar yadda ta saba a dukkan wani abu da zai sameta.
Haka kawai yau bata jin saukar muryar saman zuciyarta,a yau din bata jin sautin da yanayin yana ratsa zuciyarta yadda ta saba jinsa.
Sak mammina tayi tana duban akhnan dake zaune kawai,ba wani alamun motsawa ko xuwa gareta kamar yadda ta saba a duk yanayi ko lokaci makamancin wannan.
Gabanta ya fadi,shakkarta da kokwantonta suka dadu,amma sai tayi saurin canza yanayinta da sake takowa gaban akhnan din da sassarfa tana fadin.
"Na shiga uku ni zaituna.......biftu,ya taba lafiyarki ne?" Ta qarasa maganan tana zubewa gaban akhnan,gami da sanya hannunta tana dudduba jikinta kamar me neman wani abu.
"Kiyimin magana mana biftu......na rantse da ubangiji dake busa mana numfashi bazan barshi ba".
" Zaki masa mene?,zaki iya goge abinda ya faru ne?,ko don bai bar tabo a jikina ba hakan yana nufin tabon dake zuciyata ma zai goge ne ko zai warke?,har abada" Akhnan ta amsa mata da wata irin dakakkiyar murya. Sosai mamaki ya tsarga a zuciyar mammina.......wanne irin magana akhnan din takeyi haka?,me takeson fadi?,anya safiyya batayi amfani da wata hanyar ba ta soma gotarwa da akhnan tunani?.
"Kuskurenki ne tun farko.....kuskurenki ne mammina.....kinyimin alqawarin zaki fiddani......amma kuma sai kika sake dilmiya ni cikin wata sabuwar matsalar.....mafi munin matsalar ma da gwara bijirewa maganan sultane da umarninsa akan wannan KARYAMIN DARAJAR da kikayi" Tayi maganar karon farko hawaye na taruwa cikin idanunta,duk da batajin zata bari hawaye ko daya ya zuba daga idanunta wai don aurenta ya mutu,koda zatayi kuka ma,zatayi kuka ne kawai saboda tabuwar DARAJARTA da kuma MARTABARTA.
"Me kikasha akhnan?.....baki da hankali ne?.....ni kikr tuhuma da jefa rayuwarki a wani yanayi bayan dukkan sadaukarwar da nayi?" Ta fadi da wani mugun hargagi da bata taba mata irinsa ba.
Da wani irin kallo kawai takebin mammina,tsawarta tana sauka saman zuciyarta da wani irin yanayi,saboda wani abune baqo kuma sabo da bai taba faruwa tsakaninsu ba.
"Ba komai biftu,na gode na gode" Mammina ta furta tana qoqarin dauke hawayen daya soma zarto mata daga ramin idanunta.
Har Tsakiyar kanta takejin fitar hawayen,a tsahon shekarun rayuwarta ashirin da hudu bata taba ganin duk girman tsanani mammina ta fidda hawaye ko sau daya ba,sai yau?,kuma a kanta?.
BAKI KYAUTA BA taji sautin yana sauka saman zuciyarta. A hankali ta dauke kanta gefe,muryarta dauke da izzarnan dake sake tsananta tsanarta a zuciyar mammina tayi magana.
"Bazanyi magana dake ba MAMMINA.....ina roqonki ki tafi daga nan". Idanu ta zuba mata sosai,tana jin wani abu yana taso mata. Ita kadai tasan me takeji akan yarinyar.......ita kadai tasan adadin kaiwa bango da tayi.
Ba shekara daya ko biyu ba,ta jima tana sanyata hidimta mata bawai kai tsaye ba.......ta jima tana bata umarni masu tarin yawa,kafin ita ta samu daman maidata qasa ta koma karbar umarninta.
"Zan tafi......amma hakan bai yana nufin xan kasa yin abinda ya dace ba a matsayina na uwa.....ko yau she xanbar miki qofata a bude,duk sanda kika buqaceni ina nan ina jiranki" Maganar mammina ta qarshe kenan ta juya tana fita da wani irin yanayi dake nuna sanyin jikinta.
*MORSA SAFIYYA*
Wani irin shuru ne ya ratsa dakin,ba a abinda ke motsi banda bugun zukatansu dake cike da wani irin nauyi. A zaune suke suna fuskantar juna ita da hairaan,gwiwoyinsu suna gugar juna,hannuwan morsa safiyya din dukka cikin na hairaan data kama ta riqe sosai tana matsasu a hankali don samarwa da morsa safiyya nutsuwa,wadda bugun zuciyarta da numfashinta suke fita wani iri.
"Ki shaqi iska sosai momma......ki fitar ta bakinki don Allah" Hairaan ta fadi cikin tashin hankali. Yanayin da take ganin morsa safiyya din a ciki yafi daga mata hankali fiye da labarin mutuwar