Showing 144001 words to 147000 words out of 188421 words

Chapter 49 - LU'ULU'U COMPLETE

Unknown   

27 Aug 2026

92

ya zare dubansa daga kansa yana maidawa qofar shigar bargar,ya fara takawa a hankali yana nufar gurin,abinda ya alamtawa maleek shiga zaiyi,miskilancinnan nasu na cikin jini ne kawai bazai barshi ya furta da baki ba.



*AKHNAN*

Zuwa yanzu idan tace ba komai cikin 'ya'yan hanjinta ta tabbatar batayi qarya ba. Ta manta a daidai wanne lokaci......ta kuma manta wanne abinci ne na qarshe daya shiga cikinta cikin salama.

A wannan yammacinne kawai data gama tabbatarwa gami da amannar ba zata rayu ba tare da abinci ba ta amince ta karbi zazzafan ruwan tea din da birra keta mata nacin ta karba tasha din.

Sanye yake da wata cotton gown ta wani irin tattausan material fari qal wanda aka yiwa adon gold d'aid'aiku a jiki. Hade yake da hularsa da kuma yalwataccen cotton din mayafin da tunda birra ta ware mata kayan batabi ta kansa ba. A yau ko hula bata sanyawa sassalkan gashin kanta ba,ta sakeshi ne kawai yana kwance a bayanta wanda tsahonsa yayi kusa da mazaunanta. Abune me wahalan gaske ka samu gashinta a cukurkude ko a yamutse,ko a yanzun ma da take cikin wani irin mode da batasan sunan da zata bashi ba,gashin a kwance yake a gadon bayanta da wani irin glowing da darkness dake nuna kulawar da yake samu,saidai daga gaban kanta yadan tashi kadan,tashin da bai hana kwantacciyar sumar data kwanta daga goshinta har gefunan kunnuwanta bayyana ba.

Fuskarta tayi wani irin haske,tayi fresh sosai,blue eyes dinta haskensa ya sake fitowa qwarai. Kana iya ganin yadda labbanta suka sake sirancewa,labban da basa rabo da kyakkyawan lip gloss ko lip balm.

Wani irin zurfi tayi a tunani,har yanzu tana jin emptiness dinnan a zuciyarta dama rayuwarta gaba daya,har yanzu zuciyarta ta kasa miqa wuya dari bisa dari akan cewa bada taimakon mammina ta tsinci kanta a hali mafi muni da tozarci a tarihin masarautar agadez dana family dinta ba.

Bata zargin mammina da cutar da ita......amma tana zarginta da gaza maida hankali ta zaba mata CANCANTACCE da zata rayu kalar rayuwar da mamminan tasan ta jima tana mafarki,kalar rayuwar da tasan ta jima tana mararinta,RAYUWAR 'YANCI BA QARQASHIN DOKA KO UMARNIN KOWANNE D'A NAMIJI BA.

"Ranki ya dade......akwai matsala....." Taji muryar bushira daga bayanta,abinda ya sanyata waigowa da sauri tana dubanta,zuciyarta kuma na cike da fata da kuma neman tsarin sake jin wani abu da zai kassara farincikin da taketa tattalin dawowa dashi.

Da idanu ta tambayi bushiran,wani yare da sun jima da saba magana dashi da ita da kuma haddaceshi,don haka ba tare da jinkiri ba ta amsa mata.

"Thunder ne ya tsinke.....yace ko zaki iya wani abu akai?,dukka dabarunsu ya qare". Bata tsaya sauraren sauran maganar bushira ba ta dire cup din dake saman d'an plate din da take zuqar coffee din a gaggauce,ta soma baro harabar dake liqe da dakin hutawar tata tana shigowa ciki da wannan zazzaqar siririyar muryartata take bawa bushiran umarni.

"Bani mayafi". Da hanzari bushiran ta dauko mata tana yafa mata,gami da saita mata lausasan takalmanta.

Bata wani damu da boyon kanta da takeyi na kwana da kwanaki ba,kamar yadda bata damu da gaisuwa da kuma kallon da hadimai keta binta dashi ba. Wasunsu kallo ne na gulma da munafunci,ta fito a yau din bayan kwanakin data shafe ba wanda yaga koda qyallin idanunta.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Hankalinta sosai yana kan dokin,doki ne matuqar tsada da sultane ya sanya zunzurutun kudade na qasar dubai ya siyo mata shi,ya siyo mata shine kawai a matsayin kyautar kammala degree dinta,ta kuma fita da kalar sakamakon da sultane din yake buri,harma sama da yadda yake hasashe. Takanas tasa aka dawo dashi agadez tun a wancan abun daya faru a hippodrome,tasa ake bashi kyakkyawar kulawa,sai ta qara saurin tafiyarta wanda duka duka baifi takun tafiyar wata macen tafiya ta al'ada ba......bata soma jin nutsuwa ba sai data kawo bakin gurin ta kuma sanya kai kai tsaye ba tare data tsaya sauraren jawabin hadimin data samu a tsaye bakin gurin ba.

Tun daga nesa idanunta suka sauka a kansu,yana zaune saman bayan thunder din,saidai yayi kaman rub da ciki ya riqeshi da kyau. Sukuwa yake faman yi tare da qoqarin kayar dashi,amma cikin wata irin qwarewa yaqi bashi wannan damar. Magana yake masa da dan qarfin da zaka iya jiyowa tamkar yana magana da dan adam. Da dukka jarumtarsa ya sake rungume gadon bayan thunder din da yayi wata irin haniniya yana daga qafafunsa na gaba,abinda sukasan tabbas idan ba gwanin sarrafa doki ba ba abinda zai hana mutum faduwa qasa war was a gurin.

Idanunta ta lumshe,tana jin wata irin matsananciyar faduwar gaba,tana hango yadda thunder zai watsar dashi ya kuma tattakashi yabi ta kanshi ne kawai. Faduwa a doki wani mummunan abune da bata qaunar kalla,saidai kuma yadda taji gurin ya fara nutsuwa ya sanyata bude idanunta a hankali. Ga mamakinta thunder ya fara nutsuwa,still bai sauka a kansa ba yana ci gaba da shafashi a hankali gami da yin magana qasa qasa dashi,har zuwa sanda ya tsaya cak ya daina bige bigen da yakeyi,sai yayi wani tsallae tana direwa a qasa daga bayan thunder din.

Sosai ya qarewa dokin kallo bayan ya samu nasarar maidashi nutsuwarsa. Ya aza hannunsa gadon bayansa yana sake shafashi a hankali,abinda ya sake bawa dokin nutsuwa sosai,sannan yaja akalarsa zuwa gefe,ya kuma tsugunnar dshi,cikin ladabi yayi biyayya ya tsugunna saman qafafun nasa,sai shima ya tsugunna daga daya side din yana ci gaba da magana dashi,maganan da ba wanda yasan me yake fadi.

Idanunta ta ware sosai,tana jin wani irin kishi yana saukar mata. Don me zai sarrafa mata doki bayan bata da tabbacin iya komai a tare dashi?,meye hadinsa ma da doki?,tunda ba magana ake ta takarda ko bada karatu ba?. Batason yayi mata komai da yayi kama da taimako tallafawa ko dafawa,da wannan tunanin nata ta fara takawa zuwa inda ya tsugunnar da dokin.

Bai lura da ita ba sam,cikin sassanyan sautinnan nasa maras amo yake ci gaba da karantawa thunder wasu ayiyo na qur'ani. Yayi relaxing sosai tamkar me fahimtar ma'anonin ayoyin.

Ta daya bangaren thunder din ta tsugunna,tana qanqance idanunta. Zataso ko sau daya ya kalleta don ta karanta masa a karance cewa din bashi da hurumi akan komai nata,saidai baiyi hakan ba,don baikai qarshen ayar da yake karantawa ba,wadda sautin ya fara shiga zuciyarta a hankali yana saukar da wani yanayi,saita janye dubanta daga kallon mutumin da ko sau daya bai daga idanunshi a kanta ba,ta soma shafa fuskar dokin.

Shafar fuskar tasa ya sanyashi yin wani qaqqarfan yunquri kamar zai tashi,abinda.ya sanyasu dukkaninsu miqewa da hanzari da niyyar riqe akalarsa,lokaci guda.....cikin sakanni guda,abinda yayi sanadiyyar haduwarsu gaban fuskar dokin.

Haduwa hannuwansu sukayi guri guda,kowanne ya janye da wani irin sauri. Lokaci guda dukkaninsu suka daga kai. Idanunsu ne suka gauraya dana juna,wani irin zuzzurfan kallo suka sakarwa junansu,iskar dake kai kawo a gurin tana kada sassanyan qamshin da ya kama jikin kowannensu. Musamman nasa scent din,wannan unique turaren da shi daya ya mallaki irin qamshin a duniya.

Hasken ranar da yayi saura a sassanyan yammacin dake sake hada wani irin nau'in hadari ya haske fuskar nan tata,fuskar data mallaki wata irin kwantacciyar fata kaman da madara take wanka.

A nutse ya janye idanunsa daga kanta yana mamakin samun blue eyes a yankain africa a tattare da wata mace har haka. Launin idanun da suka jima suna bashi mamaki kafin a hankali su juye su soma burgeshi tun daga sanda ya fara mallakar hankalin kansa. Nata idanun sunyi wani irin dacewa da zara zara eye lashes dinta,da kuma gewayayyar fuskarta dake dauke da kwantaccen gashin gaban yalwataccen goshinta.

Wani abu ya taba zuciyarsa,sai ya samu kansa da tuhumar kansa da kansa da ganin baikensa na qare ma fuskarta kallo.ya sunkuya a hankali yana daukar akalar thunder dake zube a qasa,abinda ya sanya akhnan din ja da baya a hankali.

Idanunta ta sake lumshewa tana sake budesu lokaci daya sanda ya sake zaunar da thunder sosai. Ta budesu fes a kansa,ta tsani duk wani mutum da zataji yayi mata kwarjini......ta tsani wani mutum ya fits kwarjini,ba'a taba samu ba tsahon rayuwarta tsakanin mutanen da duk suke kewaye da ita,sai yanxu?,bama kuma akan kowa ba akan wani malami can?.

Iska ta zuqa sosai don daidaita nutsuwarta da hankalinta da takejin kamar tana shirin daburcewa daga sanda kallon cikin idanunsa ya zame mata wani abu na kusa kusa da tayi a yau din. Idanun da cikin mafarkinta kadai take ganin irinsu,......idanun da take tsammanin su ta gani a hippodrome,yau gasu kusa da ita ainun,kusancin da baifi banbamcin d'ani biyar ba. Kwarjinin da take hanga a nesa a kusa ya ninka wannan.......idanun sun zame mata alaqaqai din rayuwa da a yanzun cikin qasa da second ashirin na gaurayar idanunsu waje daya ta soma tunanin anya ba sihiri gareshi ba?.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*

*Safiya musa abdullahi*

*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261

KO

08187255862

*Al'ummar qasar nijer ๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ช*

*2349166221261*

*Safiya musa abdullahi*

*NITA*

*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*

09166221261

*SHAIDAR BIYA*

09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA๐Ÿ‘‘*

*HUGUMANKU CE*โœ๐Ÿฝ

[2/6, 19:28] +234 903 555 3736: ๐Ÿ’Ž *L U'U L U'U*

*_(The diamond)_*๐Ÿ’Ž

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 69*

Ba wani ido daya taba hanata furta bacin ranta koda kuwa idanun mammina ne.....mamminan dake da girma da kima a rayuwarta,amma a yau da kallo daya da yayi mata ya shafe duk wani tunaninta na abinda ya kamata ta fada masa,na sanya masa iyakoki da tsaidashi daga shiga hurumin da ya shafeta. Da kallo guda daya tak taji ya saka mata wani irin fargaba da rudewar da batasan dalilinta ba.......da wannan kallon guda daya ta daina shaqar kowacce iska saita wannan mayataccen qamshin da har yau bata gaji da neman wanne nau'in turare bane haka?.

A nutse ya miqe,miqewar data sanya idanunta sauka kan qafafunsa duk da yadda take qoqarin yiwa qwayoyin idanunta control. Kai tsaye suka fada kan takalmin dake sanye cikin doguwar qafarsa. Fes take fara sol kamar bai taba taka qasa a duniya ba,yayin da baqin takalmin da aka saqashi da magi daukakar darajar fata ta dace matuqa da gaske da qafar tasa.

Karon farko wani abu ya fusgi hankalinta,ta zubawa takalman idanu sosai sanda yake matsawa baya da baya a hankali yana barin jikin dokin.

Crown half shoe ne na kamfanin Dolce and Gabbana.......irin takalmin sultane sak,takalmin da aka taba bawa sultane din kyautarsa don nuna girmamawa daga sarkin tahoua. A lokacin suna tare da sultane din,tana zaune a farfajiyarsa yana duba kayan,kurkusa lokacin da take a matsayin aminiyar sultane din,ba yanzu da komai ya sauya ba.

Takalmin ya burgeta sosai a sannan,don har sultane yana cewa.

"Inda namiji ce ke da na bar miki shi kadeejatou" Tayi murmushi sosai a sannan,ta kuma dauki wayarta tayi qiyasin adadin kudinsa. Kanta ya kwance sosai da zallar kudin da aka buga mata lissafi da CFA din qasarsu.

Idanunta take ta qoqarin zarewa,ko kuma qaryata asalin takalmin shine a qafarsa. Sam takalmin bai dace da malami ba......takalmine dake bayyana zallar kuma tsantsar mulki da iko ga duk wanda ya mallakeshi,anya ba takalmin sultane dinne ba?,idan har haka ya kasance kenan baya ga shigar sauri da yakewa sultane da dukka al'amuransa har ya fara shiga taskokinsa?. Idan hakane gaba me zai faru?,anya bazai shiga sahun mutanen da suke zuwa a madadin baqi ba amma daga baya su qwace sarauta daga anihin wanda sarautar ke hannunsu ba.

"Da ambaton Allah kadai zukata suke samun nutsuwa" Yayi maganar hankali kwance yana sakin akalar dokin. Blue eyes dinta ta dauke daga saman takalmin tana maidawa kansa,daidai lokacin da ya juya baya,bata iya hangen fuskarsa sai kwanctacciyar baqar sumar da take kwance a qeyarsa zuwa dokin wuyansa kadan,shigen yadda asalin matasan samarin BUZAYE 'yan qabilarta suke.

Wani irin taku da take iya hangen zallar izza a tattare dashi,izzar da har yanzu take qalubalantarsa akan yinta,izzar da takejin bai cancanceta ba.....izzar da take alaqantata da tsananin girman kai ne kawai irin nashi,tare dakai kanshi inda bai baije ba.

Wani abu ya mata tsaye a wuya sanda take jinsa yana magana da hadiman gurin.

"Koda dabba ne sai Allah ya tambayeku yadda kukayi kiwonta kuka kula da damuwarta,kada kuyi tunanin idan akwai zalunci gurin kula dashi Allah bazai muku hisabi akai ba,don haka ku kula" Yadda dukkaninsu suka rusunar dakai cikin girmamawa ya sake tunzurata qwarai. Me yasa yana bare zai shigo masarautarsu ne har ya dinga iko mulki da kuma izza?.....don me sultane zai bar masa riqon babbar masarauta kaman masarautar agadez?,bayan shi din baqone akan komai ma. Hasalima baisan me ake kira da sarauta ba,meye hadinsa da ita?,sunyi hannun riga ta kowacce fuska. A yanzun tsakanin ita dashi batasan waye magajin SULTANE OF AGADEZ ba. Tana hangen wani girmamawa da dukka hadimai ke.masa,har tayi kunnen doki da irin girmamawar da suke mata.

Wannan bacin ran shi ya sanyata yin abinda bata taba yi ba wato kiran bawa da kanta. Yana dab da fita daga gurin yaji sautin kiran,karon farko da shima yaji bayyanar muryarta a fili irin haka,sai yaja numfashi sosai ya fesar dashi yana lumshe idanunsa gami da budesa duka lokaci guda.

Kadan kadan yakejin magananta cikin fada,kalma daya tak ya iya jiyowa.

"Akwai wani dama dana bayar na kowa ma zai iya shigarmin barga da duba dawakaina bayan ku?". Idanunsa ya lumshe a hankali yana maida hankalinsa ga maleek dake tattauna matsalolin daya hanga tattare da dokin,can qasan zuciyarsa kuma tana sake cika da mamakin tsananin girman kan dake damunta. Bai cewa maleek komai ba,har zuwa sanda shi da kansa ya sauya topic din.

Ita kanta batasan dalili guda daya da ya sanya taketa zabga fadan ba. Saita dinga jin kamar ba ita ba,kamar an canzata sanda ta baro bargar tana takowa gami da komawa sassanta. Yanayin girman kansa da izzarsa ke sake bata mata rai. Yana da wani dabi'a data lura da ita,basarwa tare da attitude na I don't care. Komai ma yana nuna bai gabansa bai dameshi ba,abinda take gani a matsayin zallar wulaqanci da kuma girman kai.

wadannan idanun suka sake gilmawa ta tsananin hijabin tunaninta,taja siririn tsaki yana qoqarin kauda tunanin gefe. Abu daya ta sani tabbas koda ba shine mutumin hippodrome ba.....komai nasu yazo da tarin tsananin kamanni,mutumin da har yanzu yaqi barin cikin baccinta,a wannan karon tana jin zata saka kudo ko nawa ne don binkito gaskiyar WAYE SHI?.

"Ranki ya dade.....mammina ta aiko tana son ganinki......"

"Bana sha'awar ganawa da kowa......" Ta amsawa birra a taqaice wadda ta karbo saqon daga hannun yalwa. Ko d'ar bataji ba soma takawa zuwa balcony dinta. Har qasan ranta tana jin wani zafi zafi na mammina.....tana kuma son nuna mata taji radadin da bata taba ji ba a tsahon rayuwarta don ta fahimci cewa ta bata mata da gasken gaske. Ta bata mata martabarta tarihinta da GIRMANTA da taketa fama riritawa,sai takai hannunta a hankali da zummar jawo mayafin kanta dake shirin sauka,nan take hancinta ya shaqi wannan daddan qamshin da duk sanda zata shaqeshi yake haifar mata da faduwar gaba.

Sake kai hannun nata tayi hancinta da sauri,sosai qamshin ya shige mata qofofin hancinta yana ratsawa a hankali yana isa ga kwanyarta dama zuciyarta gaba daya.

Dakatawa tayi da tafiyar a hankali,sunan barratu ta kira,ta qaraso a hanzarce,saita miqa mata hannunta kawai. Ta fahimci me take nufi,ta matso a hankali cikin d'ar d'ar takai hancinta ta shanshana.

"Inaso ki nemo contact na kamfanin YASMEEN.....shine kawai company

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login