Showing 165001 words to 168000 words out of 188421 words
daga kan system din ya maida kan haisam sanda ya dauki dabino bakwai cikin wanda ke zube a wani qawataccen gold plate dake ajiye a gurin.
"Sai ina?" Maleek ya tambaya kai tsaye,don yanason ya zauna suyi magana da haisam akan falaak. Abinda yakeji tattare da ita ya girmeshi,yana jin kamar kwanakin da motii ya dauka be dawo ba suna da nisan gaske.
"Zanje.....zaituna nason ganina" Haisam ya fadi yana cire qwallon dabinon daya dauka din. Sosai omar ya koma ya zauna yana duban haisam.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Kiranka kuma?,to ko nazo muje?" Sosai maganan ta bashi dariya,amma sai ya saki murmushi sanda yake jefa dabinon bakinsa yana taunashi a hankali. Ya yadda qwarai da gaske garin suna da albarkar dabino suma kamar qasarsu,a wasu abubuwan hana hangen kamanceceniya kadan kadan.
"Ka rakani?,saboda me?"
"Saboda tsaro mana haisam" Omar ya furta da dukkan gaskiyarsa. Murmushi ya kuma saki,sannan ya fara takawa a hankali da alama yana nufar hanyar fita ne.
"Shi zaki koda ba'a cikin gandun dajinsa ba ya tsinci kansa yana yin farautarss ne yadda yaga dama,duk wani kira.....duk wani kebewa,duk wani magana da zata nemi tayi dani yana zamantowa kaman qarin dama ce a tare dani,qarin daman da zan samu na buda mata hanyar da zata dilmiya kanta da kanta" Ya qarasa maganar a huce kuma hankali kwance.
"Amma ko connection ya kamata ka hada dani"
"Babu buqata.....saina dawo" Ya fadi yana saka qafafunsa waje.
Ajiyar zuciya maleek ya sauke,ya kuma maida dubansa ga omar da har yanzu yabar bakinsa a sake.
"Duk inda kake ajiye haisam ya wuce nan gurin.....ya wuce hasashena da naka,hakanan ya zarta tunaninmu,duk wani motsi da taku da zaiyi lissafinsa daban yake da namu.....yanayin jarumtarsa yana bani tsoro a wasu lokuta. Baisan tsoro ba....baissn fargaba ba,baya banbamce guri me hadari da akasin hakan a duk sanda ya sanya gabansa gaba a kan aikinsa.....yana da yaqini cikakke ga mahaliccinsa......zai dawo omar.....zai dawo lafiya ina da yaqini da hakan.....addu'a ta ratsashi fiye da zatonmu da kallon da muke masa,a kwanakin nan ni kaina nasan da haka,shi yasa baya shakkar kowa da komai,baya kuma shakkar tunkarar komai din" Sosai omar ke jinjina kansa,yana kuma sake gamsuwa dari bisa dari da maganganun maleek.
*MAMMINA*
Wannan karon kuma a wannan lokacin da kanta take takawa zuwa bakin iyakar gurin,cikin salo na kai kawo tare da tarin tsammanin jiran isowar haisam din.
Har wani zabalbala takeji jininta yana yi idan ta tuna cewa yau itace ke maimaita kiran wani d'ana adam dake rayuwa cikin masarautar agadez qarqashin alfarmarta?,bayan yayi watsi da kiran kuma har sai ya zabi lokacin zuwa?.
Ranta yana son ya cimma qololuwar baci,amma kuma tana danne hakan daga ranta,don a yanzu ba fusata ko tursasawa take buqata suyi mata aiki ba. Kwantar da kai,maida komai ba'a bakin komai ba da kuma nuna masa zallar karamci da tarin abun duniyar da zai iya rabauta dashi,su kadai ne makaman da tafi buqata a yanzu.
Tana juya baya tana komawa ciki a karo na barkatai taji sallamar tafisu. Saita waiwayo da wani irin yanayi tana dubanta. Dubanta itama tafisu takeyi,cikin girmamawa take dubanta.
"Ki dade kiyi qarko,Allah ya baki yawan rai.....mene yake faruwa haka ne?". Wani bacin rai ya tasowa mammina,ta kasa amsawa tafisu har sai data samu guri ta zauna.
"Nida wancan wulaqaccen malamin mara asali ballantana tushe.....mutumin da har yau jiya zuwa yau dana shirya zama dashi an kasa ganomin danginsa ko daya na kusa ko na nesa.....sai almajiransa mutum uku da yake tare dasu,don na ukunma baiyi cikakken sati biyu cikin masarautar nan ba" Mammina tayi furucin tsananin fushi yana nunawa kan fuskarta.
"Ki kwantar da hankalinki ranki ya dade.....iname tabbaci da yaqinin komai zai tafi yadda akeso,kinsan abu me qarko bai fiya zuwa da sauqi ba......yanzu haka tamim ne ya tasomin,ya kusa isa diffa amma ya juyo,yace yana buqatar ganinki da gaggawa". Kai ta jinjina a nutse,don hankalinta a yanzu ba'a kan tamim yake ba. Hankalinta yafi karkata ga yadda zata tsara auren haisam da akhnan,tayi imani shi daya ne zata juya yadda takeso cikin sauqi tayi amfani kuma da wannan damar ta bata tsakaninsa da sultane,ta nesanta tsakaninsa dashi har abada.
"Wannan mutumin tafisu.....har yanzu na kasa samun gamsuwa da aurensa da akhnan" Murmushi tafisu ta saki tana waiwaya kadan,sai itama idanunta ya sauka inda mammina ta kafe da kallo.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer π³πͺ*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITAπ*
*HUGUMANKU CE*βπ½
[2/11, 20:53] +234 903 555 3736: π *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*π
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 78*
Haisam ne yake takowa a nutse,shi daya da wani irin haiba kwarjini da kamala.
"Zaki ruftashi ne ramin rubutaccen alqawari da yarjejeniyar da bazai iya tsallake mata ba.....zaki daureshi da sasarin da bazai iya kunceshi ba dole saiya amince miki. Yasan girman alqawari,yana tattalin mutuncinsa da kimarsa,ko don gudun sarayar mutuncinsa da tsare tsaren da muka tanada zamu masa barazana dasu zai saketa salin alin". Kai mammina ke jinjinawa,maganganun tafisu kuma suna bata wani qwarin gwiwa na musamman.
Cikakkiyar sallama yayi yana takowa cikin nutsuwa,sai mammina din ta miqe cikin yanayi na girmamawa. Fuskarta dauke da wani kwantaccen murmushi take fadin
"Lale maraba da zuwan amintaccen sultane......ga gurin zama" Ta fadi tana nuna masa kujerar dake fuskantarta.
A nutse ya zube idanunsa ga kujerar,ya taka a hankali yana komawa bayan kujerar ya jawo wata can daban da bata cikin jerin jadawalin tsarin ya ajjiyeta a daidai inda yakejin ya gamsu dashi.
Wani boyayyen murmushi ta saki,a hankali ta maida idanunta kan fuskar tafisu. Cikin harshen afaan oromo,cikin yaren daya zame mata garkuwa,yaren da bata yarda ta yarashi sam a gabab mutane,saidai a kebantaccen guri irin wannan tace.
"Ko don na karya izzarsa....ko don na nuna masa shi din ba kowan kowa bane.....tabbas sai nayi amfani dashi......na rusa sultane na kuma rusa ragowar rayuwar AKHNAN,lokuta kadan ya rage,zai zamemin makami ba tare da shi kansa yasan da hakan ba" A wani irin jere maganganun suka shiga kunnen haisam wanda ya sanyo qafafunsa dab da gurin. Ya kamata ace yayi mamaki matuqa ko ya girgiza da jin futar furucin daga bakin ta,amma sai baiji komai ba. Mamakin daya mamayeshi kadai shine yadda yaren oromo daya dade da sanin tana jinsa a yau yake fita saman harshenta radau. Cikin rashin sani ta aza idanunta akan haisam tana me sakin fuska,sannan ta maida dubanta ga tafisu saboda tanaso ta sallameta kafin su zauna da haisam din.
"Tabani tamkar taba masarautar agadez ne tafisu,yayi ganganci daya aikata haka,don baisan yadda makomarsa zata kasance mafi muni ba.....baisan cewa ni zaituna bazan tabu ba.....ta kowacce fuska biyayya a gareni ne kawai zaman lafiyan kowa.......zan tilastashi ya karbi aurenta koda ya nuna wannan girman kan da kuma izzar da dagawar.....a shirye nake na sanya a batar da kafatanin ahalinsa muddin mazauna qasar nan ne da kewayenta"
"Kin dade da makara zaituna zeenatu" Haisam ya furta can qasan ranshi,saidai ko daya ba wata alama da zata baka cewa wai yana fahimtar yaren oromo gaba daya. A yau yaga amfanin adana yare da gasken gaske......a yau kuma da mammina ke sake fardewa cikinta wuqa zayaso ace NAMIJI ce ita. Zayaso wannan wasan......wannan yaqin......wannan farautar dan uwansa namiji ne a cikinta,saidai koma meye yayi imanin kawai BOYAYYUN MAZAJE cikin duk wani shirinta......wanda suma a kowanne mataki yake da lissafinsu da kuma alwashin birkitosu cikin da'irarsa.
Hakanan tafisu takejin maganar kamar tayi nauyi da yawa. Duk da cewa bayajin yaren amma wanda ake shirya komai a kansa?,kuma don saboda shi yana tsaye a gurin?.
"Maleeka......kibi a hankali kada ya fahimci wani abu" Murmushi ta saki me cike da izgili,sannan ta maida dubanta ga haisam dake takowa saman shimfidadden lallausan kilishin da aka qawata gurin dashi,ta saki masa murmushi cikin nuna alamun girmamawa.
"Qaraso sheikh,bismillah". Kai ya jinjina a hankali,yana sake riqe kansa da kyau gami da hanawa kansa nuna wani alama dazai bayyana shi din jinin OROMIA ne.
Maida kallonta tayi kan tafisu da wani salon kallon izza da isa.
"Ba wani alama tattare dashi dake nuna yasan yaren oromo.......oromia basa buya.....basa iya boye yarensu,yanayi da zubinsu da al'adunsu basa canzawa da wuri,ko ke kin manta yadda dukkanin ayarinku akasha wahala daku kafin ku saje ku koma ABZINAWA?" Murmushi tafisu tayi tana jinjina kai.
"Anyi haka maleeka". Sai itama mammina din ta jinjina nata kan
"Iya wannan ya isa amsa tafisu,kina iya tafiya,kafin mu kammala din naga tamim"
"A kammala lafiya" Ta fadi ta yunqura tana miqewa.
Saida tafisu ta kammala fita gaba daya sannan ta tattara hankalinta akan haisam,haisam din dake riqe da wayarsa yana sarrafata hankali kwance,saidai kunnuwansa da kwanyarsa suna bibiye da kowanne lafazi da zai fita a bakin mammina din.
"Ina neman afuwa sheikh......duk da tarin uzurori da nauyin masarauta dake kanka amma na matsanta game da batun neman haduwarmu dakai" Ta fada cikin kwantar dakai sosai,nuna karaya da tausasawa. Sai a sannan ya daga kanshi daga wayar,bai kuma kalleta kai tsaye ba saida ya yiwa wayarsa ma'ajiya sannan ya zube dukkanin idanunsa a kanta yana soke yatsun hannunsa cikin na juna. Wani irin magnet ya fusgeta da kyau,wasu kamanni suka gilma daga tsakiyar qwayar idanunsa cikin nata,sai tayi saurin janye qwayar idanunta a nashi can qasan ranta kuma tana tambayar kanta
"MENENE WANNAN?" Maganarsa ta kawar da tunaninta.
"Ba damuwa ranki ya dade". Har tsakiyar kanta taji kiranta da yayi ranki ya dade din bai zauna mata ba,don yau din a wannan lokacin kuma shine karo na farko data fara jin kalmar a bakinta.
"Aiki ne me muhimmanci a gabanki ZEENATU... Meye tattare da matashin malamin da zai firgitaki har haka?!!!" Wata zuciyar ta tsawatar mata,abinda ya sanya ta sake maida dubanta kansa a karo na biyu,saidai wannan karon ta kaucewa duban tsakiyar qwayar idanunsa kamar dazu,shima kuma ya karanci hakan.
"Na gode" Ta fada da murmushin nan.
"Bismillah.... Ga kayan sha da naci" Ta fadi tana nuna gaban shimfidarsa inda aka shirya komai. Sai daya dubi dukka tulin kayan da bai amince da koda cup daya dake gurin ba ballantana su kansu tarkacen cimar da aka cika gurin da ita,tamkar wanda aka gayyata wani party sannan ya maida dubansa a kanta.
"Godiya nake" Kawai ya furta a nutse. Ko a rayuwarsu ta yau da kullum,a tsarin aikinsu na security ba'a kowanne guri suke amincewa da kowa ba,kaman yadda ba'a hannun kowa suke amsar abu suci ba. Koda a office dinsu dake hukumar tsaro ta farin kaya masu girkinsu amintattu ne,musamman irinsa da suka zama manya. Uwa uba ma kuma shi din yana da bala'in tsantsami,ba kowacce mace ke masa girki yaci ba,wannan ya sanya Aanani ke yawan gulmarsa a bayan idanunsa.
"Captain din tsirfa......captain obbo inda macene nanay mun shiga uku" Bakinta baya gajiya da fadin hakan,musamman duk sanda zata tarara da nanay da shekarunta da komai.....duk da tarin hadimai dake gudanar da komai na gidan amma zaka sameta a kitchen a tsaye akan abincin Muhammad haisam din. Randa ta karkace tanaga gulmarsa,sam batasan yana qofan kitchen din ba,ya shigo gaida nanay dinsa ba,saida saamee ta tabata suman zaune tayi,baice mata qala ba ya qarasa shigowa kitchen din,ta samu ta sulale,sai data debi sati guda cur bata bari sun hadu ba,duk da sau tari shirunsa tasan wani punishment ne me zaman kansa,ta samu da qyar dai tasha zancan yabi ruwa,sai bayan wani lokaci ya tarfata. Bata da hanyar goge kanta,sai kawai ta fashe masa da kukan da tasan ya tsana,tattarata yayi yace ta bace masa da gani.
"Akwai muhimmiyar magana da nakeso muyi dakai.....wani muhimmin abu nake dauke dashi,wanda ba wanda ya cancanci samun wannan abun.... Wannan damar ta musamman face kai" Kai ya gyada a hankali yana ci gaba da dubanta don tabbatar mata yana tare da ita. Zamanta ta gyara sosai,tana kuma sauya yanayin fuskarta zuwa jimami da rashin sukuni.
"Ba shakka kai din wani babban mutum ne da ake girmamawa a nan,sunanka tsaftatacce ne......sannan mu'amalarka da jama'a me kyau ce kowa ya shaida hakan...." Saita dakata a hankali sannan ta dora.
"Magana ce akan shalelen sultane wato akhnan....." Wani yanayi ne a hankali ya ratsashi,ya kuma sake sanyawa ya tattara hankalinsa. Ba wani magana a bakin matar da zata zama me muhimmanci matuqa a tare dashi,amma kuma dole ta zama wani abu da za'a bawa nutsuwa....duk wani motsi nata.....duk wani fitar furuci daga bakinta ya sani tabbas YANA IYA KASANCEWA WATA SABUWAR RAYUWA.....WANI SABUWAR MASIFA GA RAYUWAR WANI,walau ta ambaci sunansa ko bata ambata ba.
"Duk da abubuwa da yawa sun faru,wadanda suka darsa fushin sultane a kanta,suka koma jawo raunin mu'amala a tsakaninsu,amma hakan ba abinda zai canza game da matsayinta a zuciyar sa......sannan kuma babu abinda zai hanashi yaji ciwo,kuma yaji zafi idan wani abu mara kyau yasameta". Still yana ci gaba da saurarenta ne ba tare daya furta komai ko ya motsa ba.
"Akhnan ta hadu da jarrabawar rayuwa ita sahihi kuma ingantaccen mijin data zaba....wanda a zahirin gaskiya ba qarya bane ya dace da ita. Suna yiwa junansu wani irin so dani kaina bansan dashi ba sai a yanzu bayan ya saketa kwanaki uku bayan daura aurensu,bisa makircin wasu da har yanzu ban gane su waye ba. Sun bugar dashi sun sanya ya fita hayyacinsa a ranar farko da zasu fara ganin juna,ya kuma yi mata mafi munin saki wato saki har uku" Saita dakata tana wani ajiye numfashi cikin nuna yanayin alhini na gasken gaske. Idanunsa ya lumshe a hankali ya sake budesu a kanta. Yana yabawa da jinjina yadda ta iya tsara wasan kwaikwayo me kyan gaske irin wannan. Yadda ta zama gagarumar me laifi da yadda ta maida qarya ha'inci da zamba cikin aminci ne kawai ke tafasa masa zuciya. Ba abinda yafi tsana kaf rayuwarsa irin qarya,ita kuma ya lura cewa tafi girmama QARYA sama da komai. A yadda take maganan nan banda dashi muhamamd haisam take magana.....mutumin dake kallonta tarrr a tafi hannunsa ba abinda zai hana tausayinta ya kama wanda take maganar dashi,ba abinda zai hana imani ya shiga zuciyar dan adam a kanta,wannan kadai ya sake tabbatar masa ME HADARI CE ita.
"Saki sheikh hasaim,wani abune dake barwa mace tabo koda bata da laifin komai yayin sakin......musamman saki irin wannan da aka yoshi a sanda ake ganiyar dokin haduwa da juna,ake kuma tsananin qaunar juna......"
"Ina ganin zaifi kyau ki wuce kai tsaye zuwa dalilin kiran" Ya samu kansa da katseta haka kawai yana jin bayanan nata sun fara cika masa kai. Cikin wata irin dabara ta qare masa kallo. Cikin izza yayi mata magana,tamkar dai tana magana da sultane. Ta sake duban yanayin zamansa dake nuna zallar QASAITA irin xaman da ba wani bawa ko hadimi daya taba zuwa gabanta yayi irinsa. Wani abu ta hadiye ta turashi can cikin maqoshinta,sannan ta qwaqulo murmushi ta aza saman fuskarta.
"Inaso na samar mata da nutsuwa,inaso na samar mata da daidaito cikin rayuwarta a matsayinta na amanar Allah a hannuna" Ta fadi tana dunqule hannunta. Sosai maganar ta wani irin ratsashi AMANAR ALLAH data kira ya sanya ya sake bude idanunsa sosai a kanta. Tabbas batasan girma da illar maganarta ba,tabbas batasan waye ALLAH ba......babu ko shakka batasan matsayin AMANA a musulunci ba,da bazatayi wannan furucin ba,sai ya sakejin matar gaba daya tana saare masa a rai....duk dama bai kamata ma ya tsammaci imani ko sanin Allah a tattare da ita ba.
"Naji cewa a musulunci ba laifi ko kuskure game da hada AUREN KISAN WUTA ko kuma AUREN YARJEJENIYA muddin bada sanin mace ba ko?....ko bada sanin miji da matar ba......muhammad,kaf duniya sultane bashi da wanda ya aminta dashi sama dakai......da kai kadai ne nima na aminta,na kumayi amannar cewa zaka iya taimakawa akhnan kamar yadda itama zata taimakeka" Sai ta dakata tana dubanshi kafin ta qarasa farke manufarta gaba daya,duk da tasan zuwa yanzu koda bai fahimceta gaba daya ba ya fahimci fiye da rabi na abinda take nufi.
Shima dubanta kawai yakeyi,hauka qarara kuma yake gani shimfide cikin maganganu da kalamanta. Jira yake ta qarasa fadin abinda take niyyar fada din a yanzu,abinda kawai ya rage masa kenan.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer π³πͺ*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITAπ*
*HUGUMANKU CE*βπ½
[2/11, 20:53] +234 903 555 3736: π *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*π
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 79*
"Nayi