Showing 156001 words to 159000 words out of 188421 words
dake can qofa tana jiran umarninta. Da gaggawa ta iso gabanta tana zubewa.
"Zan shiga naga akhnan,bana buqatar iso,bana kuma buqatar a gaya mata zuwa na".
" Hakan za'ayi Allah ya baki yawan rai" Ta fadi kanta a qasa sannan ta miqe itama ta fita.
Kwana da kwanaki tayi bata sanya akhnan din a idanunta ba,ba kuma wai don ta shirya faruwar hakan ba,sai don abubuwan da suka sha mata kai take qoqarin ganin komai ya tafi a tsari. Shirye shirye taketa yi,shiri kota kwana,maganan motsuwar daya daga cikin tarakuna Ethiopia ya tsaye mata a rai,shine kuma abu na farko da take kwana take kuma tashi dashi,sannan da kanta take bibiyar samun tabbacin abun,ta zare wakilci tana ganin kaman bazai mata ba.
Abinda yafi sanya mata wata fargaba shine......ganin yadda aka kasa samun cikakken bayani kai tsaye cikin sauqi kan da gaske akwai wanda yayi tafiya zuwa agadez?. Abinda yake sake luguiguita mata zuciya kenan.....yake sanya mata shakka da wasi wasin ANYA ba wani gagarumin abu bane yake shirin tunkarota?.
*AKHNAN*
Ba zata sake bari wani abu ya taba IKONTA ba.....ba zata sake bari wani abu ya girgiza duniyarta ba......ba kuma zata sake bawa kowa dama ya bude qofar rayuwarta ba.....koda wayeshi.....komai kusancin dake tsakaninsu.
Tun a dararen da suka shude ta yiwa kanta wadannan alqawuran,zata maida rayuwarta yadda take a baya a cikin satin. Zata maida kanta PRINCESS KHADEEJA MUHAMMAD HAMMUD dinta kamar yadda take a baya,zata rayu yadda takeso,ba shawarar kowa....ba sanya hannun kowa.....ba gudanarwa ko yankewar hukuncin kowa. Wannan ya sanya ba tare data shaidawa mammina ko tayi shawara da ita ba ta fara shirye shiryen komawa Niamey. Tun a daren jiya ta gayawa hannatu a gyaran gidan a maidashi kaman yadda yake a baya,a fadawa babban driver dinta na garin Niamey wato HARISU ya duba motocinta gaba daya da take fita office dasu a fita dasu a siyo wasu. Koda ta koma Niamey tana jin zatayi hutun sati daya cikin gidan kafin ta fara fita office. Zata zauna na sati daya ta maida wannan tunanin na CEO a kanta,ta sake kintsa nutsuwarta da yadda zata karbi ayyukanta.
A yanzun da take zaune cikin daya daga cikin falukanta da takan huta. Baida kujera ko daya,sai wasu irin lausasan Turkish carpet da tuntum manya masu dauke da tambari na sarauta da sunanta a jikin kowanne. ABIDA me mata gyaran gashinta ce,wadda ta iya nau'ikan manyan kitso na qasashe da qabilu daban daban,da kuma kalba manya da takan yiwa akhnan din a sanda duk zata koma Niamey idan ta gama hutun qarshen mako da takeyi a baya.
Tana mata kalbar data zama manya kuma tana hade jelarsu guri daya yadda ba zasu damu uwar gijiyartata ba,yayin da akhnan din ta maida hankalinta sosai ga ameesha tana sauraren bayanai akan kamfanin na watannin da tayi bata tare dasu.
Kowanne bayani na ameesha sake bata mamaki kawai yakeyi,amma bata dakatar da ita ba,taci gaba da sauraronta duk da ba ganewa takeyi ba,amma ta aza hakan akan cakudewar bayanan ameesha dinne guri daya ya kawo haka,don bada wannan salon da kuma wannan yanayin suka gabatar mata da bayani ba.
Kanta taji abida ta saki,abinda ya sanyata dauke kai daha system din da suke video call da ameesha ta maida ga abida,sai idanun nata suka sauka akan mammina dake takowa cikin izza,da alama kuma ita ta saka hadimanta su bawa dukkan hadiman dake dakin umarnin fita.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer ๐ณ๐ช*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA๐*
*HUGUMANKU CE*โ๐ฝ
[2/10, 19:48] +234 903 555 3736: ๐ *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*๐
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 74*
Bata motsa ba,bata kuma ce da ita komai ba,sai kawai ta maida idanunta ga Ameesha sukaci gaba da tattaunawarsu cikin salon miskilancin nan nata da ya motsa.
Idanun mammina akan ameesha bayan ta daukeshi daga kan akhnan da rabi akayi masa kalbar ta kuma sauka lambas a gadon bayanta,sai rabin gashin da yabi gefan kuncinta ya kwanta.
A jikinta taji abubuwa biyu,bata kuma buqatar qarin bayani. Hankalinta ya kwanta da har take shirye shiryen komawa Niamey kenan?,sannan ya akayi ta samu access da ameesha?....me take gaya mata?.
Tana buqatar fahimtar komai kafin tayi magana daukan mataki na gaba ko kuma yin wani motsin,don haka ta samu tuntum daya ta zauna akai tana harde qafarta.
Still akhnan bata waiwayo ba,saidai yanayin ameesha da taga kaman yana sauyawa,kamar bayanin tana yinsa ne kawai ba tare da ita kanta tasan gundarin abinda take magana akai ba. A nutse ta lumshe idanunta sannan ta budesu a kanta.
"Ameesha" Ta kirata da muryarnan tata dake cike da aji gayu da sarauta.
"Ranki ya dade"
"Ki tattara komai ta yadda idan na iso zanji dadin dubawa,bazan wuce gata ba in sha Allah"
"To Allah ya kawoki lafiya,godiya nake" Ameesha ta fadi wani sanyi yana tsargawa qasan ranta. Tana fatan ta iso da wuri,ta kuma jima tana addu'ar dawowarta a lokaci irin wannan kafin komai ya qarasa kwabewa.
"Gata?" Mammina ta furta a nutse da salon tambayar da ba iya fili kadai ba.....hatta da zuciyarta ta aikewa tambayar. A nutse ta waiwayo ta dubi mammina tana kuma dakatawa da kashe system din.
"Eh gata" Ta amsa mata kai tsaye da wani irin yanayi da tasan sauran mutane kadai akhnan me magana dasu a haka ba ita giwa ba.
"Gata in sha Allah......ko akwai sauran abinda ya rage da zan zauna nayi?.....kowa burinsa ya cika,an daurawa akhnan aure,ta taba aure a tarihin rayuwarta dai ko?" Ta fada da dukkanin alamun dake nuna abun yana mata ciwo.....da dukkanin alamun dake nuna cewa abun yana mata radadi tare da jefata a danasanin amincewa da wannan yarjejeniyar tunda farko.
"Akhnan d'iyata" Mammina ta kirata bayan ya sake matsowa dab da ita,idanunta da jikinta dukka sunayin wani irin laushi.
"Ban taba zato ko tunanin wani lokaci yana zuwa da zaki zargeni koki tuhumeni da cutar dake ba" Ta furta hawaye yana saukowa daga idanunta. Har tsakiyar zuciyarta akhnan taji hakan,a karon farko taga abinda bata taba ganina idanun mammina ba tsahon rayuwarta,kuka ko hawaye
"Na rantse miki harda girman Allah......almaz shine kalar mijin da yafi dacewa dake.....kinsan a yanzu haka halin daya shiga saboda abinda ya aikata din?". Tayi mata tambayar tana tsareta da idanu tanason karantar yanayinta.
Kai tsaye akhnan din take duban mammina. Haka kawai tayi loosing interest aka komai daya shafeta......tana jin tana rasa dukkan wani confidence da qwarin gwiwa akan mammina din. Batasan me yasa ba,tana jin kawai komai ma ya fita a ranta,amma wani sashe na zuciyarta yana gaya mata,bai kamata KUSKURE D'AYA TAK da aka samu daga bangaren mammina din ya zama wani abu ba.....ya zama wani dalili da zai sanya ta juya bayanta daga dukkan wani alkhairan mammina din a tare da ita ba.
Wata irin mutum ce ita da bata manta alkhairi komai qanqantarsa.
"Wallahi akhnan ya fiki shiga baqinciki bacin rai da kuma damuwa.......a yanzun ina me baki tabbacin baisan inda kanshi da hankalinsa yake ba,kuma dukka a kanki,dukka ta sanadinki" Mammina din ta fadi yanayinta yana nuna narkewar zuciyarta.
"Ta yaya zanyi saken da wani mummunan abu zai rabi diyata?.....ta yaya zanyi saken da halitta mafi soyuwa a zuciyata da rayuwata zata fuskanci wata barazana?,bayan bani da kamar wannan halittar duk duniya?. Ina jin wani irin mamaki kaman zai kasheni a duk sanda na kalli fuskarki,naga kuma ba abinda ya cikata sai tuhuma da ganin baqina" Mammina ta furta tana share qwallarta data sake gangaro mata.
"Amma duk da haka ni zaituna.....nayi alqawarin saita lamuranki,koda kuwa hakan shine abu na qarshe da zan aiwatar a rayuwata.......abu daya zan gaya miki.....ko mene zai biyo baya kada ki tuhumeni.....idanunki da hankalinki kawai nake buqata......amma karki manta da wannan ko sau daya a zuciyarki......ni mammina UWA nake a gareki.....bazan kuma taba canzawa daga wannan sunan ba har abada.....kamar yadda babu wani abu da zai sauya qaunar da nake miki har gaban abada". Daga haka ta miqe da wani irin yanayi dake nuna mutuwar jiki da damuwa me yawa.
Samun kanta tayi dabin mammina din da kallo,tana jin jikinta itama gaba daya yanayin wani irin sanyi. Tana jin kamar ya kamata tabi bayanta.....amma wani sashe na zuciyarta dake daqare da wannan izzar dake gauraye da jinin sarauta na gaya mata ta qyaleta.
Wani irin kewa takeji a yau......wani irin kadaici takeji duk da cewa tana zagaye ne da mutane. Samun kanta tayi da miqewa tsam,ta taka a hankali tana isa bakin qofar dakin,ya maidata ta murza mata key ta kulleta. Dawowa tayi a nutse zuwa bedside drawer dinta da ba wanda yake da alhakin taba gurin,ta murzata ta budeta,ta kuma fiddo wani dan zagayayyen akwaiti me matsakaicin girma ruwan gold. Budeshi tayi a nutse,ta saka hannu tana fiddo wasu hotuna qananu guda biyu.
Idanu sosai ta xubawa fuskar dake jikin hoton,fuskar dake dauke da wani lallausan murmushi. SAFEENA ce,idanunta a cikin hoton suna kallon camera ne kai tsaye,wasu irin kyawawan idanu da suke kama sosai da nata,banbamcinsa da natan ita fari da blue ne......yayin da na safeena ya kasance fari da baqi sidik......
Hannu ta sanya a hankali ta shafi hoton,a ranta tana raya abubuwa masu yawa.......a ranta tana raya inda tana raye yaya zasu fuskanci wadannan kwanakin masu tsanani da taurari a tattare da ita?,saita lumshe idanunta tana damqe hoton sosai a tafin hannunta.
Haka kawai takejin akwai wani abu da ba daidai ba......haka kawai takejin akwai wani KUSKURE da yake tare da ayyukanta da zartarwata......ko kuma yake tattare da tunani da hukuncin mammina?. Amsar da bata da ita batasan kuma yadda zata fassara abun ba.
*SULTANE*
Cikin kamala da nutsuwa irin tasa,wadda bata taba sauyawa ba ko a wanne bigire kuma ko awanne yanayi ya samu kansa ba ya qarasa qofar dakin bobbo muhammad dawud,wanda ya kasance daura dashi cikin daya daga cikin manyan hotels dake kusa da haramin madeena.
Sau daya ya nema izinin shiga,bobbo da kansa ya taso ya budewa sultane din bayan ya ajiye dan qaramin alqur'anin dake hannunsa.
"Ina fata kaima qira'arka irin ta yaronka ce ko?" Sultane ya fadi yana duban bobbo muhammad wanda ya ajiye masa ruwan daya ciro masa mara sanyi sosai a fridge. Bawai don daga wani guri sultane ya taso ba,ba kuma wai don yana jin ishirwa ba.....aah,kawai don tarin girmamawa ga tsohuwar abota.
Murmushi sosai bobbo muhammad dawud yayi. Zuwa yanzu har ya saba da yanda duk fitowar rana da kuma faduwarta sai sultane din ya ambaci hasaim. A irin ambaton da ko motii aba jifar baya tunanin yana ambatonsa haka.
"Duk wanda ya zauna da muhammad saiya dosani wani haske na alqur'ani daga gareshi" Obbo ya fadi yana zama gefan gadonsa yana fuskantar sultane. Kai sultane ya gyada a hankali,yana sake jin nutsuwa gami da gamsuwa me yawan gaske a tare dashi game da haisam din.
"Zanso nasan wadanne iyaye ne haka Allah ya yiwa baiwa da samun yaro irin muhammad.....tabbas ni na sani,suna cikin iyaye masu sa'a a duniya". Murmushi kadan bobbo yayi,ya sani ba abu bane me yiwuwa ya gayawa sultane cewa tsohon abokinsa motii aba jifar shine mahaifi ga haisam din. Yin hakan kamar ya tona asirin aikinsu ne.....komai kuma zai iya bayyana a lokaci da kuma muhallin da ba'a shiryawa faruwar hakan ba.
"Abokina ne......wanda ya damqa amanar muhammad a hannuna......ya damqa min da amana da gaskiya.....wanna ya sanya sau tari ni kaina nakejin muhammad din kamar nina haifeshi"
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Wannan shine dalilin daya sanya nayi tattaki zuwa gurinka.....don ka yimin alfarma.......don kuma ka nema min alfarma". A nutse bobbo ya daga kai yana duban sultane,maganganunsu suna zuwa masa a hagunce.
"Kamar yaya?" Bobbo ya tambaya kai tsaye da alamun kullewar kai a tare dashi.
Sosai sultane ya gyara zamansa,yana kuma tattarawa bobbo dukkanin nutsuwarsa,abinda yake gayawa bobbo cewa maganar tana da tarin muhimmanci mara misaltuwa.
"Inaji a jikina akwai qaddarar data sake hadamu a nan gurin dawud,bayan tsahon shekaru da mukayi bama tare,ba kuma tare da mun sake haduwa ba. Yanayinka da yanayin girman da muhamamad ke baka....labarin qarfi da girman amincinku ya tabbatar zaka iya tsaiwa a bigiren da mahaifine kawai yake tsayawa,Nazo ne na nemawa d'iyata khadeeja auren muhammad haisam a hannunka......kai kuma ka nema mata aurensa a hannun amininka mahaifinsa". Maganar ta zowa bobbo a bazata.....kamar yadda asalin salsalar maganar da sigar maganar ta canza daga anihin ma'anarta.
Duk da yadda maganan ta saukarwa bobbo a bazata,amma hakan bai hanashi sakin dan qaramin murmushi ba.
"Sultane......yaushe aka fara nemawa mace kuma auren namiji......har abada namiji ne yake neman auren mace". Kai sultane ya jinjina a nutse.
"Na sani......na sauya ma'anar ne.....na sauya yadda asalin yake,cike da fatan wannan sauyin ya zama tabbatacce har a qarshen rayuwar khadeeja". Cikin nazari qwarewa da sabo da aikinsu da security intelligence bobbo ya zubawa sultane idanu. Koda sultane bai zurfafa magana ba,koda bai zurfafa bayani ba ya fahimci kai tsaye daga zuciyarsa maganar take fitowa.....kai tsaye yake maganan daga ma'ajiyar dukkan lafuzzansa na gaskiya......hakanan ya karanci wani abu lullube a bayan furucinsa dake taba zuciyarsa.
"Sakin aurenta a kwanaki uku ne zai sanya sultane ka sake nema mata wani mijin?" Murmushi sultane ya saki a nutse yana girgiza kansa.
"Na maimaita istikhara a kwanakinnan har bansan adadi ba Akwai abubuwa masu tarin yawa da bansan yadda zan bayyanawa kowa yadda nakejin sukarsu a qirji da zuciyata ba......amma nasan abu daya da yayiwa tunani na da fatana karan tsaye shine......MAGANGANUN SAFIYYA WANI HASKE NE.....wani mabudi ne da sai a yanzu nake zurfafa tunanin zasu zama wani SANADI a rayuwar akhnan. Ba kalar wannan qaddarar na shirya gani a rayuwar biftu ba muhammad..... Wannan ya sanya na RUNGUMI kalaman safiyya a yanzun da dukkan nazari da dacewa a bisa ma'auni.......namiji me addini shine zai zama silar bango garkuwa da kuma me jangorar rayuwar akhnan bisa hanya me kyau.......ban shirya bawa diyata kowa ba sai HAISAM.....bari kaji dawud.....na jima ina kawaici.....na jima ina bege da fatan zukatansu su hadu guri guda.....to amma abun tsoron sai na fuskanci akwai wata irin tazarar nisa a tsakaninsu. Tun daga sannan na duqufa da addu'ar haduwar zuciyarsu da kawunansu,don ko tahowa nan da nayi jigon silar zuwana itace wannan addu'ar,cike da fata da kuma sanya rai....ban kuma cire tsammani ba har sai ranar da aka gayamin shi da kansa ya bada aurenta ga wani......ashe duka duka cikin kwanaki uku jarrabawar da kokwanton amsuwar addu'o'ina dukka zasu qare......"
"Dawud...." Sultane ya kira bobbo kai tsaye,bai amsa masa ba,amma kuma yaci gaba da dubansa.
"Nayi bacci har sau uku cikin raudha bayan na gama addu'o'ina da istikhara ta.......haisam nake gani a mafarkina da zarar bacci ya daukeni.......yana farautar duk wani abun farauta daga namun daji da suka kawowa akhnan hari......mafarkina na qarshe kuma tana boye a bayansa ya zame mata GARKUWA......kayimin alfarma.....kayimin kuma jangora haisam ya zama GARKUWA na gaske ga marainiyar d'iyata......" Yayi maganar zuciyarsa tana motsuwa saboda tuna safeena da yayi.
Wani abu ya ratsa bobbo,mamakin wani nannauyan abu me girma da yake hangowa cikin idanun sultane yana kamashi. Saidai sultane bai barshi haka ba,a nutse ya warware masa labarin SAFEENA da ya gangaro zuwa ga rayuwar akhnan.
A cikin labarin ya dasa ayar tambayoyi masu yawa......a ciki ya dinga hasashen al'mura masu yawan gaske.......saidai yayi imanin muddin haisam ya wanxu cikinsu ya rayu dasu na wata guda.....yana da tabbacin zai wahala baida labarin komai.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer ๐ณ๐ช*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA