Showing 54001 words to 57000 words out of 172989 words

Chapter 19 - MAR’ADAM’S COMPLETE

30 Aug 2026

71

bangarenta abun bai mata dadi ba dan bata son maryama ta riga ya'yanta aure  amman zata yi iya yinta taga ya'yanta sun rigata aure ita da take da suruki kamar yusuf

me zai dameta da wani  sadam gashi  ga dukkanin alamun dole akayi wa sadam din zai aureta."

aunty fati tace" sadam d'ana ina maka fatan alkhairi suna gama fadar haka suka bar wajen zuwa bangaren aunty hassana suna shiga aunty hassana tace "yanzu ke k

in yarda da wannan tsarin"?nasan karya ne dole akayi masa amman tunda ta zabi haka ki zuba ido Kiyi kallon abinda zai biyo baya da wannan maganar suka kawo karshen zance suka shiga wata ."maryama na  zaune cikin  halin tashin hankali umma ta shigo parlour'

n tana ganin ummah ta mike ta  rungumeta tana kuka "ummah me nayiwa su aunty fati ?"me  zanyi  su soni  ?wallahi banason muktar ki taimakeni ummah kar a d'aura auren nan   laifin me nayi masu ummah ?ina ta  bawa zuciyata hakurin  rayuwa dasu, amman kullum

burinsu suga bayana ."ta karashe mgnr tana kuka."

"ki qara  hakuri da kowa da komai  akan wanda kikeyi maryama rayuwarki  qaddara ce zuwa yanzu ya kamata ace kin saba da qaddararki karta dinga baki tsoro "wallahi ummah  jarabawa bata bani tsoro saboda

na maida alamarina zuwa ga allah "yauwa abinda nake son ji kenan kowa ce  rayuwata cike take da  lullubali  da qaddara kuma sai allah yana sonka yake jarabaka domin yaga karfin imaninka idan kuma akace haka dole sai ka shirya, jarabawa ko ta class ce yaya

kike jinta bare jarabawa daga allah? fatana allah ya bamu ikon cinye jarabawa ."ta fad'a tana shafa bayanta tana jin fad'uwar gaba ."tana Tunanin yadda zata shigo mata da zance sadam  taji sautin muryar maryama tana cewa "ni dai ummah kisa abar maganar mu

ktar ke kad'ai ce nake da yakinin zata min wannan gatan ."

ummah  ta zareta ajikinta ta kamo fuskar maryama da hannuwanta duka tana  kallon fuskarta  tace "babu wani muktar da zaki aura na yanke shawarar zaki auri yayanki sadam, maryama ta zaro idanu

  tana duban umma cike da matsanamcin mamaki "yaya sadam kuma  ummah ?"a matukar rikice  ummah tace "Eh ko baki sonshi."ahankali ta shiga girgiza mata kai domin dai tasan  ko giya ta sha bazata iya furta hakan gareta ba ,bare kuma tasan

tayi hakan ne dan

yantota daga hannunsu aunty fati ."ai ko bata son yaya sadam ta karba kuma ta amince sai dai fargaban yadda yaya sadam din zai karbeta muryarta a raunane tace "ummah kina tunanin yaya sadam din zai  amince   ?

"ya ma amince  maryama "kuka ta fashe da

shi  mai karfi "shikenan mafarkinta ya tabbata"ya allah kabani kwarin gwiwar cinye jarabawar da duk zaka min "alhamdulillah alhamdulillah shine kawai abinda umma taji yana fitowa daga bakinta "allah ne abun godiya maryama babu abinda zai biyo bayan wannan

auren sai alkhari, karshen wahalarki yazo ta fad'a tana sake  rungumeta ajikinta " aunty ta qaraso ta zauna kasa kusa da kafafuwan ummah "ban san da wace irin kalmar godiya zanyi amfani dashi wajen gode miki ba amman zan zabi wannan kalmar allah yay miki s

akamakon da gidan aljana "na gode na gode !!sai kuka ya kufce mata daga maryama har Aunty  suka saka ummah tsakiya suna mata kuka ."

koda habib ya dawo yaji hukuncin ummah abun yayi masa dadi sosai  dan gara sadam sau million akan wani muktar fatan al

khairi yayi yana tmbyr aunty maryama .""Tana d'aki  !" ta fad'a atakaice tana sauke numfashi a daki ya iske maryama kwance  akan katifa tayi kuka har idanunta sun kunbura tana tunanin  yadda qaddarori suka yita zuwa mata daki daki akan aurenta a she tana t

are da mijinta bata sani ba "ya zauna kusa daita  yana kiran sunanta "heartbeat ".ta sauke numfashi tana dubansa da kunburarrun idanunta "bakiji dadin hukuncinsu umma ba ko ?ta langwabar da kanta kawai  batare da tace komai ba "heartbeat idan da wani aka b

aki zance Aa amman yaya sadam dabam ne karki ce aa bazaki samu kamarsa ba "

"kai ma ka amince dashi  ?sosai kuwa dan mutumin kirki ne kuma yana duk wasu quality's da zaa so shi ta sakar masa murmushi  wanda ya bayyana wushiriyarta sama da kasa tana gy

ara kwanciyarta

ta jingina bayanta da abun gado ta janyo pillow ta rungume tana jin wani nauyi a qirjinta"bana jin son yaya sadam  ko kad'an acikin raina amman bani option zan rayu dashi muddin rai "yayi shiru kawai yana kallonta cike da tausayawa dan ba

i san me zai sake cewa ba ,domin farincikinta farincikinsa ne haka zalika damuwarta damuwarsa ne zai sake magana ta katsesa ta hanyar cewa "karka ce komai after dad tunda har ka

amince  daman kai kawai nake jira naji raayinka tana gama fadar haka ta sauko

"muje parlour'n muci abinci ta riko hannunsa binta kawai yake jikinsa a sanyaye ."

*******

Tun bayan da ummah ta furta   maganar aureta da yaya sadam habib  bai zauna ba ya shiga buga bugan neman aiki karfi daga wannan kamfani zuwa wannan duk kuma

saboda ita da mahaifiyarsu ne daman da karatu da kwallon kafa ya dogara dan yana d'an  samu a buga kwallon kafa amman ba wani samu sosai ba dan kudin ba wani kudin azo agani bane amman babu laifi yana toshe  masu wata kafar dan  hatta mashin din da yake da

shi yanzu  da dan kudin da yake samu ya siya ."matslar dai   ba koda yaushe ake samu  ba sai a dauki alokaci baa daukesa ba shiyasa yaga gara ya had'a da aikin kamfani ranar da'akayi dashi za'a d'aukesa  a ranar ya samu damar  buga kwallon kafa  zuwa ogun

state kenan  ya samu promotion daga  jahar lagos zuwa wata jahar  ."

Adaidai wannan lokacin maryama ta kammala bautar kasa tare da kawarta subai'a babu inda take zuwa tana zaune a gida abinda tafi tsana kenan zaman gida sam a yanzu bata son zaman gid

ansu  gashi dai tana samun kulawa gata sangarta só qauna soyayya tarairaya daga  mahaifiyarta  haka ma habib sai ummah wacce sanadiyyar sadam yasa yanzu motsin kad'an tana bibiyar me take ciki komai ta samu ita zata  bawa amman zaman gidan baya mata dadi s

aboda zuciyarta ta rasa abu d'aya wato mai d'ebewa zuciyarta kewa dan gabad'aya tunda akayi maganar aurensu da yaya sadam ta rasa gane kanta dashi karon kashi sadam din sai ma taga ya rage bata kulawar daya saba bata ada can baya ."

****

A hankali ATA

ya shiga office dinsa babban ma'akacinsa  mai tantance ma'aikata na  kamfaninsa Z&A na biye dashi  abaya ,ya zauna a mazauninsa yana kallonsa  batare da yace komai ba "good morning sir ? ya gaishesa cike da girmamawa "uhm ! yayi gyara murya kawai alamun ya

na jinsa  yana maida hankalinsa Kan system "uhm amm  sir ko zan iya magana yanzu "uhm ! ya fad'a a takaice "adadin mutane kimanin dubu dari uku ne suke bukatar aiki a karkahainmu ,sir wannan shekara ko zaa hada da  masu degree ? Ko kuma daga master zuwa sa

ma ne zaa dauka ."?" ka ma da kake maganar daga wani mataki ka  fara aiki ?"sorry sir ya fad'a a tsorace "duk mutumin da aka tabbatar takurdunsa sunyi kyau ayi  masa interview idan ya cancata a d'aukesa ."

"sai  abu na gaba kada a Kuskure akarba'  kwabo d

uk wani mutun domin samar masa aiki a duba cancanta yana gama magana ya dauke idanunshi akan system zuwa wani bangare dabam  yana cewa fatan" ka fahimta "yes sir sai kuma game da compaing dake kasar  togo sun kira suna bukatar almustapha "me zance

masu?" k

ai komai bazakayi da tunanin kanka ba sai ka tmby ? "am sorry sir"ya juya da sauri ya bar office din ."

Ranar  monday   tun asuba da maryama ta tashi tayi sallah bata koma ta kwanta ba ta soma shirin zuwa wajen interview duk abinda tasan zaa buqata ta

had'asu waje d'aya  acikin jakarta hatta kayan da zata saka ta fito dashi sannan ta shiga wanka karfe bakwa  daidai ta gama shirinta ta fito parlour'n ta hango aunty tsaye a kitchen ta qarasa ta rungumeta ta baya "good morning mumy "ta kai hannunta ta sha

fa gefen fuskarta morning my princess har kin fito ?yes !ta fad'a tana duba agogon dake daure da tsintsiyar hannunta "muje ki karya kafin ki fita "aunty da kin bar breakfast din nan Kiyi min addua kawai" bakince akwai wanda zai tsaya maku  ba ?aunty ta fad

'a tana fitowa daga kitchen maryama ta biyo bayanta tana cewa "akwai but bashi zai mana interview ba amman dai ina ji ajikina zamu samu nida subai'a "to Allah yasa a dace "Ameen !ta fad'a a lokacin da wayarta ta d'auki qara ta ciro ta duba tana cewa "aunty

subai'a ce ."

Tayi sauri ta d'auka tana "cewa hello suby okay gani nan fitowa mgnr second biyu sukai  ta katse kiran tana cewa "aunty ni zan wuce subai'a har ta fito "kema yanzu zaki wuce ta kai cup din tea bakinta ta kurbi kad'an ta kai bread bakint

a a haka ta shanye cup din tea tace "na gode sosai Allah bar min Ke mamana ina sonki ta kai mata kiss a kumatunta ta nufi kofar fita da sauri tana cewa aunty "bye ye sai na dawo "bye ta d'aga mata hannu tana kallon bayanta kai tsaye bangaren ummah ta shiga

da sallamarta yaya sadam ta gani zaune  Jiki a sanyaye ta gaishesa "yaya sadam ina kwana?"ya dago idanunshi ya kalleta sannan ya amsa da" lafiya !"

ta nufi hanyar dakin ummah  sai ga umma ta fito"maryama har kin fito ?na fito umma to Allah yasa a dace

  tace Ameen " ina zata ?ya tambaya batare daya kallesu ba "interview ! ummah ta bashi amsa da haka "aiki zatayi kenan ?" to meye amfanin karatunta idan batayi aiki ba ya dan yi shiru can yace "nifa gsky bana da wannan raayin yana gama fad'ar haka ya mike

yana cewa " ni na wuce tsaya ka sauke  min ita "bai ce komai ba ya fita maryama tabishi da kallon mamaki dan bata ta'ba tunanin zata samu matsala dashi akan aiki ba ganin shima dan boko ne ita kam akan aikinta zata iya hakura da auren dan

sam aure baya r

anta a yanzu mutuntakan umma ne ta duba  da tausayin mahaifiyarta bawai son aure take ba ,ganin yadda yanayinta  ya canza  yasa ummah tace "karki wani damu zakiyi aikinki "amman  ummah alamunsa ya nuna baya so "gsky ne sadam bai  son  amman zai yarda kinji

  wahalar karatunki bazai tafi a banza ba ,yana ma daga cikin abinda yasa ban bari an daura maku aure ba nafi son  ki  shiga da aikinki". kanta kawai ta gyada mata "maza bishi ya saukeki ."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗

MAR'ADAMS



💖💖💖💖

💗💗💗

💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH

AREWABOOKS USERNAME

AYSHAABAGUDO

bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi ac

cess idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

Page 11

Jiki a sanyaye maryama take taku gabad’aya kuzarin jikinta yayi kasa ,”a

iki zatayi kenan nifa bana ra’ayi ? maganarsa ta shiga yawo acikin kwakwaluwa da zuciyarta , tana tafiya tana tunanin maganarsa , a qalla yaya sadam ya kusan minti shabiyar zaune acikin motarsa yana jiranta , ya dubi agogo a karo kusan na shabiyar yaja qar

amin tsaki a lokacin da wayarsa ta soma ringing ya kai hannu ya d’auka ya duba yaga sunan ummanshi ke yawo akan screen din wayar. numfashi ya sauke sannan ya d’auka cike da girmamawa “sadam !”ta kira sunansa ya amsa da “na’am “ina son kaso maryama tun daga

qasan zuciyarka ,sannan zaka iya zama madadi ko ka cike gurbin abubuwan da maryama ta rasa a rayuwarta na shekaru baya.”

“ina jin ciwon da qunci abubuwan da sukai ta faruwa daita amman ina fatan kai ne zaka wanke min wannan quncin ya dawo farinciki n

a har abada “naji ummah in sha Allahu zan yi iyakar qoqarin na kawo miki wannan farinciki “dan allah sadam ka son maryama “ yayi murmushi kawai yana sosai keyarsa yayinda idanunshi ke kallon hanyar da maryama zata bullo .”ahankali yaga tahowarta a natse ta

ke yin komai nata kamar bata son taka kasa koma yace tausayin kasar take “nayi magana ba kace komai ba ? “duk abinda ummanah take so ya zama dole naso “ya fad’a yana sake tsaida idanunshi akanta “

“na gode maka allah yayiwa rayuwarka albarka yadda k

ayi min biyayya kai ma allah ya baka ya’yan da zasu maka biyayya “Ameen ya hayyu ya qayyum “

qirjin maryama na tsananin fad’uwa ta qaraso bakin titin unguwarsu har ta tsaya jikin motarsa bai iya d’auke kwayar idanunshi akanta ba ,jikinta a matukar sanyaye

ta bud’e gaban motar yaya sadam ta shiga yayinda zuciyarta Ke bugawa da karfin gaske ta zauna tare da rafka tagumi cikin rashin sanin madafa madadin taji yaja motar sun wuce sai taji yayi sallama ya ajiye wayar hannunsa ya kunna music yana bin wakar ahank

ali .”

Kanta taji ya sara mata ganin bashi da niyyar tafiya ga lokaci na wucewa ya sata kallonsa kamar mai shirin yin kuka tace “yaya sadam !”tamkar ba magana take yi masa ba haka ya cigaba da bin wakarsa babu alamun damuwa ko nadama a fuskarsa hann

u ta mika hakan yasa sukayi daf da juna wanda da zata qara matsar da hannunta zata iya yin masauki a jikinsa, a natse ta kashe wakar ta sake kallonsa tace “i am talking to you yaya sadam “.“me kike son na yi ?ya fad’a a sanyaye “kayi hakuri dan allah idan

wani laifi nayi maka lokacin na tafiya gashi naga baka da niyyar tafiya wannan aikin shine rayuwata bana son rasashi .”

ya d’an matsota yana cewa “ni dana zauna jiranki tsawon mintuna shabiyar bani da aikin yi ne ?”ko bani da wajen zuwa ne?” ko kuma a

ikina bashi da mahimanci ne ?”yayi mata tambayar ajere yana sake kunna wakarsa .”sake kashe wakar tayi ta kallesa a marairaice sannan tace “am sorry duk maganarka ce ta rikitani har yasa kuzarina yayi kasa wallahi da kyar na kawo kaina bakin titin nan shir

u yayi yana kallonta fuskarsa a d’aure tmkr wanda bai ta’ba dariya ba “ka d’an saki fuska nan dan fushi baya maka kyau “ ta furta cikin wani irin salo da sautin murya mai sanyi huci bakinta da numfashinta duka na dukan wuyansa wanda sanadiyyar hakan ya had

dasawa tsigar jikinsa mikewa ya kuma qara bugawar da zuciyarsa take .”

ajiyar zuciya ya sauke yana jin wani iri a ilahirin jikinsa “saboda nace bana ra’ayin aiki ?”wallahi duk shi ya sanyayyar min da jiki da dai zaka amince zanyi farinciki da hakan

“bai sake cewa uffan ba ya kunna motar ya soma tafiya kamar wasu kurame haka suka cigaba da tafiya .”qarfe tara saura wasu mintuna suka isa bakin tafkeken get din Z&A yaja ya tsaya batare daya kashe motar ba cikin siririyar muryarta tace “yaya sadam na god

e sosai allah ya kai lafiya “ ta fad’a tana qoqarin fitowa daga cikin motar adaidai lokacin da hancin motar ammar ta sanyo kai “Ameen ki kula da kanki “I will !ta

fad’a tana sakar masa murmushi duk da bawani sonshi take ji ba amman taji dadi sosai kuma zat

a iya rayuwa dashi muddin rai .ammar yana kallo sukayi bankwana “

da sanyi jiki ta shige cikin sadam ya cigaba da tsayuwa yana kallon bayanta har ta ,bace masa sannan ya lumshe idanunshi lokaci d’aya kuma ya bud’e “oh my goodness god “ya furta a can q

asan zuciyarsa ta yadda idan ba bakinsa ka kalla da kyau ba bazaka fahimci abinda yace ba .”murmushi ya kwace masa a saman fuska wa zai same kamar maryam yace bai so ?”sai dai wani dalili na dabam ya haifar da hakan ,sam ya manta a inda yake sai da yaji mu

tane ana masa hon a she fa motoci ya tare duk suna tsaye suna jiransa murmushi yayi sannan ya kama gabansa yayinda maryama tuni ta shige cikin ma’aikata bata ma san lokacin da yaya sadam ya wuce ba .”

tana shiga sauran abokan aikinta suka qaraso suna

mata magana suna shirin shiga inda zaa wa masu neman aiki interview amman ita maryama hankalinta bai garesu yana kan neman inda subia ta shige ,tunda tasan a tun lokacin da sukai waya daita ya cancanci ace tana wajen koma anyi mata interview an gama .”taja

ta tsaya tana cewa” kuje zanzo na sameku daga baya “.ta bud’e jakarta ta ciro qaramar wayarta ta shiga neman layin subai’a ,ganin an bud’ewa ammar mota ya fito yana nufota yasa ta sauke wayar daga kunnenta tare da kashewa gabad’aya “ya iso har inda take t

saye yana gama qarasowa wayar hannunta ya amsa ya rike ta kallesa tana murmushi sannan tace “barka da safiya ?

“Barka !

“me ya tsayar dake da sai yanzu kika qaraso ?ya tmbyeta yana duba screen din wayarta sunan wacce ya gani ne yasa ya mika mata waya

r “wallahi wanda zan aura ne ya ‘bata min lokaci “ tayi maganar cikin salon jan hankalin duk wanda yake tare daita, ammar kasa magana yayi kafin daga baya da kyar cikin fad’a yace “wato har zaki iya fad’a min wanda zaki aura ne ya ‘bata miki lokaci ? tayi

shiru tana wasa da yatsun hannunta dan batayi tsamanin zai ji haushi maganarta ba ganin babu komai a tsakaninsu sai mutunci da girmamawa “amman ki sani wannan ba mutuncinki bane ko nace zaki zubda mutuncin family d’inku ne .”

“Ai shima family dinmu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login