Showing 51001 words to 54000 words out of 172989 words
an tura domin
sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa
bakwai ) a YouTube.
Page 10
Ahankali ta yunkura ta mike tsaye kamar wata mahaukaciya ta soma zariya acikin d'akin tana sambatu "yanzu me zan masa na kawowa kaina kwanciya hankalin acikin gidan nan ?tayiwa kanta tambayar tana mai
qara shiga tashin hankali "babu abinda zaki iyawa wannan mai shegen taurin kan da zaki burgesa ,komai zaki masa a banza ne a wajensa "tayi shiru na minti biyar tana tunani kafin ahankali ta qarasa inda wayarta take ajiye, ta kai hannu ta d'auka tana tuna
nin kiran d'aya daga cikin yan'uwansa wani tunani tayi sai kuma ta fasa kiran domin dai tasan kowa a cikinsu abu d'aya yake fad'a mata shine hakuri hakuri !! kuma yanzu da zata kirasu hakurin dai zasu bata ."
"bana son wannan hakurin gashi ku
ma hakurin dole zanyi tausayin kanta ya kamata tana mai jin kamar duk ita ta jefa rayuwarta cikin matsala a dalilin zunzuruntun qaunar da take masa da taki auren tun farko data zauna da rayuwarta lafiya ."yanzu me zanyi ?ta sake tambayar kanta tana cure h
annuwanta waje d'aya "idan da hali ki sake zuwa wajensa ki kwantar da kai tunda kece a kasansa "da sauri ta girgiza kai alamun shawarar bata yi mata ba "wallahi da zan cire kulafucinsa nayi hakuri na bar rayuwarshi da komai zai zo min da sauki "ta sake
bawa kanta wannan shawara "amman ina bazata iya ba dan tana da kulafucinsa tana mutuwar son shi kamar yadda yake mugun kinta murmushin takaici maryam tayi tana cewa "Allah kasani ina wa adam wani irin so mai girma, allah ka nuna min ranar da zai soni k
amar yadda nake sonshi dan zan só faruwar haka."
"burina a koda yaushe mu kasance a matsayin miji da mata kamar sauran ma'aurata dan haka maryam karki gaji da halin mijinki kije ga mijinki baki san abinda allah zai yi ba wata rana sai labari ga kuma
alqawarin da kika d'aukarwa mahaifiyarsa kuma mami ta yarda dake shiyasa ma ta baki amanarsa
da wannan shawar ta fito daga cikin d'akin cike da sanyi jiki ."bayansa ta hango yana taka step ahankali yayinda hannuwansa duka ke cikin aljihun wandonsa kunnen
sa manne iPod ."kai tsaye bayansa tabi yo tana kallon yadda yake taka step yana wani rangaji." alamun taku yaji abayansa ya waiwaya ya kalleta sannan ya juya ya cigaba da taku ,yana gama sauka ya samu waje ya zauna akan d'aya daga cikin kujerun parlour'
n ya d'aura kafarsa d'aya akan d'aya yana cigaba da wayarsa "karka qara min damuwa ammar akan wanda nake ciki,
ina ruwa da wata yarinya ta gama bautar qasanta mana ina ruwana ."
"idan zanyi aure dole sai ita zan aura ?" kaga dan allah malam mu bar mag
anar nan ta isheni haka
yes of course ni na furta zan qara aure amman ba lallai sai wannan yarinyar ba .""Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun maryam ta furta a kasan zuciyarta qirjinta na dukan uku uku sakamakon jin maganarsa ,ta tsaya nesa kad'an dashi
tana kallon yadda yake motsa bakinsa tare da sauraron maganarsa .shiru ATA yayi can yace "ammar ba lallai tayi min ba ka dai san halina ba duk abinda yayiwa mutane yake min ba ina da test "maryam ta runtse idanunta qirjinta ya cigaba da beating very fast
amman kuma ta d'an ji sausauci jin abinda ya fad'a dan haka ta taka ta shige kitchen tana mamakin yaya ammar ."
"In da wani ne ya fad'a mata zai kasance cikin masu bawa mijinta goyon bayan ya qara aure zata musa sai gashi taji da kunnenta sosai taji
ciwon abun aranta ta had'o masa shayi irin wanda tasan yana so ta qaraso inda yake zaune jikinta a sanyaye ta mika "ga shayi !".ya d'ago tsumammun idanunshi ya zuba mata batare daya kar'ba ba ya cigaba da wayarsa "kasan Allah da nayi niyyar naga yarinya
r nan ko sau d'aya ne amman jin yadda kake wani zuzutata naji bazan iya ganinta ba ." wani naunayen ajiyar zuciya maryam ta sauke najin dadin abinda ya fad'a dadinta dashi akwai ra'ayi kuma ra'ayinsa nayi mata dan ba duk abinda mutane ke so yake masa ba
"ga shayi ka sha " ta sake furtawa a raunane kwayar idanunsa ya sake d'agowa ya zuba mata wanda yasa ta sake shiga tashin hankali "nasan kana da d'abiar shan shayi a duk lokacin da ka dawo daga aiki ".
wani dogon tsaki yaja yana d'auke kwayar idan
unshi akanta "abinda ya kamata tayi tun a farko shine dan shirme irin nata ya dawo karshe" ya sake jan tsaki ."
Daga can bangaren ammar kuwa cewa yayi "haba ATA kaji da madam mana ,dan allah kayi qoqarin kabi mahaifiyarka shine kawai zai samar maka kwan
ciyar hankali da natsuwa "na sani ammar ina iyakacin qoqarina the girl always doing nonsense wai abinda ya kamata ayi da farko dan hauka irin nata shine ya dawo karshe "haka zaka d'aure kayi hakuri kuma da zaka d'aure ka .."enough ammar ! ya fad'a tare da
amsar qaramin cup din hanunta ya ajiye akan table ya mike ya nufi kofar fita ya barta a wajen tsaye bayanshi tabi da kallo tana furta "oh ni maryam naga takaina."
Haka taja kafafunta ta koma d'aki duk yadda taso kin kiran kowa acikin yan'wansa am
man zuciyarta ta gaza hakurin haka sai data kira nana hauwa'u "tana dauka ta fashe mata da kuka
tana cewa "sister me na tsarewa yaya ammar da yake son yaya Adam ya qara aure?" "aure kuma ?wallahi da kunnena naji suna hirar inda allah ya taimakeni yayanki
yana da raayi yaki yarda da maganarsa "to ki godewa allah da bai yi raayin qarawa ba dan koni bazan so akawo miki wata matar gidanki a halin da'ake ciki ba ciwo zaa qara miki akan ciwo "."Sister wai taya zaayi na shawo Kan yayanki ne ?ina ji ajikina haku
rina ya kusan qarewa acikin gidan nan "na sani sister kina hakuri sosai da yaya Adam amman ki qara akan wanda kike yi sannan karki gaji dashi ki cigaba da bashi duk wata kulawa da mata ke bawa mijinta idan babu mutuwa akwai rabuwa wata rana zai ga amfani
niki sai abu na gaba " ki dage da addua abinda na fahimci kina sakaci dashi kenan sister wallahi idan kika rike allah zai isar miki ,dogaro da allah shi ke yaye wa mutun damuwa sosai nana hauwa'u ta ajiye damuwarta ta dinga kwantar mata da hankali ."
******
Maryama na zaune a d'akinta tana nike kayanta yayinda kunneta Ke makale da hearpis tana waya da ammar "tayi murmushi ai kam da zamu samu zamu ji dadi sosai dan ance samun aiki a Z&A akwai matukar wahala amman tunda kana nan nasan bani da wata
damuwa ,Allah kuwa zuwa lokacin ma mun qare nysc dinmu allah dai yasa muna da rabo , daga can bangaren ammar yace "wai waye wanda yayi muku hanyar samun nysc dinku a Z&A ?"ta sake fad'ad'a fuskarta da murmushi sannan tace "wani tsohon saurayina "kai da
n allah?wallahi kuwa malamin islamiyyarmu ne mutumin kirki ai ina ganin da allah ya qaddaro aure a tsakaninmu da yanzu ana daf da bikinmu amman yanzu babu wannan maganar ".me ya faru da babu maganar "long story ne sir "tana rufe bakinta tajiyo muryar au
nty fati tana cewa "ina maryama !"
mikewa aunty tayi da sauri tare da kallonta ganin ta shigo mata babu ko sallama kamar wata zararriya " ina maryama take ?" jiki a sanyaye maryama ta kai dubanta ga kofar d'akin ,sannan a tsanake cigaba da waya da
oga ammar har ta qarasa ninke riga kwaya d'ayan dake hannunta ta had'a da sauran kayayyakin da take nikewa muryarta a sanyaye tayi masa sallama ta mike ta ajiye kayan a ma'ajiyarsu sannan ta fito parlour'n tana jin mummunar fad'uwar gaba wanda adai
dai wannan lokacin sautin muryar aunty ya shiga kunnenta "maryama ta .."tana d'akinta "yauwa hakan ma yayi kyau dana sameta a gida ,ta sheida miki yadda mukayi daita ?".
numfashi Aunty ta sauke tace "akan me kenan?Karya kike mara mutunci kice baki san k
omai ba dan nayi imani babu abinda take boye miki idan kuma baki sani ba bari ni na fad'a miki da kaina akan aurenta da muktar ne nasan kina sane da zamansa karki ce min a'a kiga tashin hankali yanzu ."
nan da nan zuciyar maryama ta jagule taji kam
ar ta d'ora hannu aka tasa ihu ko taji saukin zafin da zuciyarta take mata ."aunty tayi shiru tana kallon Aunty fati a tsanake kafin ahankali tace " idan wannnan maganr ne ta fad'a min "amman .."ya isa !tunda ta fad'a miki ya kuke ciki ?akan me kenan aunt
y fati ? wani kallon raini aunty fati tayiwa Aunty sannan tace "kan batun saka ranar aurensu mana dan na matsu na matsu naga maryama a gidan muktar".aunty muktar yaron kirki ne ,sannan bashi da wata makusa amamn maryama ta nuna min bata da ra'ayinsa m
afi alkhairi abar maganar allah ya had'a kowa da rabonsa na alkhairin ".Karya kike mara mutunci ga dukkanin alamun na fahimci
daga gareki zaa samu matsala " ta fad'a tana zare mata ido "ai wannan matar bata da kai bata san mai sonta ba yaro ya had'u
yana da aikinsa mai kyau ,ita yartaki ba yar kowan kowa ba dilalin kashi zaki ce bata da ra'ayinshi "inji cewar aunty hasana data shigo ."
aunty ta kalleta wani iri ,cikin jin haushi tace "idan dai haka ne me yasa ke bazaki bashi d'aya daga ciki
n ya'yanki ba ?"ki bashi Islam ko kaulat mana ."
"Oh haka ma zaki ce ?kwarai kuwa na fad'a tunda auren zumunci kuke só had'awa kunga zumunci zai fi maku dad'i ,ina dalili zaku saka min yarinya gaba dame zata ji duk mutanen kirki kun kuresu zaku wani had'a
ta da muktar ".amman yanzu kika gama cewa muktar yaron kirki ne ?ai bazan ta'ba aibanta d'an wani ba tunda inda nawa " oh kice dai kina gudun yarki ta auri dan shashaye?aunty hassana tayi mata tmbyr tana murmushin mugunta "aunty tayi shiru kawai tana kall
onta zuciyarta na tafarfasa."
"ke yanzu har kin guji mai hali irin nashi ?"kinga ni bana son kananan magana aure ne dai maryama bazata auri muktar ba tun da bata son shi "wallahi baki isa ba karewa ubanta ma menene ."?inji cewar aunty fati hankali
n maryama yayi matukar tashi jikinta rawa tace "aunty fati please mana dan allah duk abun bai kai haka ba bana son ana tashin mahaifina ta wannan han.."bata qarasa ba ta qara bud'e murya "wai dan giya ne da shaye shaye bakya son ana fad'a kome ?"maryama
ta sunkuyar da kanta kasa tarasa meke mata dadi "wannan wani irin dangi ne gareta?" hakika aunty bata masu adalci ba data zabar masu uba acikin wannan zuri'ar ."
Cikin wani zare ido da maseefa aunty fati tace "kaf dangin ubansa babu mai shaye shaye ba
re giya sai acikin dagina kinga kuwa ubanki ya gada, aunty ta runtse idanunta tana jin wani irin zafi acikin ranta "wallahi aunty fati wannan yarinyar muguwar yar bakinciki ce kuma ba kowa take wa bakinciki ba
sai wannan tsinanniyar uwaratata takewa domin
ubanki kwalbar giya biyu aka bashi ta ishesa ya miqa ki ga duk uban dayazo neman aurenki ." aunty ta sake runtse idanunta tana datasani maganarta data tasan magangun da zasu gasa mata kenan da babu abinda zai kaita yin magna ."aunty fati ta kalli maryama
a wulaqance tace "idan kika kuskura kika kawo matsalar akan auren nan ni da kaina zan kawo wanda zai tura miki ciki kuyi auren dole dashi".
Maryama tayi raurau da idanu "aunty hassana tace "ni kuma wallahi kinji na rantse muddin kika ki auren muktar
sai dai ku tattara ku bar gidan nan amman aurensa babu fashi sai anyisa kuma acikin satin nan . "to ni yanzu idan ma auren ma za'ayi me muka ajiye da zaayi acikin satin nan ?uwarki zaki yiwa wannan tmbyr bani ba aure ne dai sai kin auresa kuma ni bab
u gudumuwar da zan bayar mara kunyar banza zan fad'awa dangin ubansa suzo a saka rana aiki banza kawai suna gama fad'ar haka suka juya suka fice daga parlour'n."shiru maryama tayi cikin tsnanin zullumi da juyayin maganr yayar mahaifinta " wallahi duk au
nty ce tajawo masu wannan wulakanci da tozarcin "ta tsani dangin mahaifinta ta tsanin akidarsu "why aunty me yasa kika cutar damu haka ?me yasa kika auri mahaifinmu tayi maganr a fili ."
"shiru aunty tayi ta kasa cewa komai yayinda hawaye suka
cika kwarnin idanunta aunty kuka maryama kuka "abinda mahaifiyarsu tafi karfi yau shi yafi karfinta adalilin biyewa son zuciyarta "
yayar mahaifinta zata aurar daita ga lalataccen d'anta.",ina ma aunty zata koma zuwa ga dinginta ina ma zatai hakan ko sa
u daya né, tasan yan'
uwanta zasu yafe mata su karbeta kuma bazasu ta'ba barin taji kunya ba zasu tsaya mata suyi mata komai hawayen da take kokarin boye né suka samu nasarar zubawa tayi saurin saka hannunta ta goge tana kokarin maida sauran dake kokarin
zubowa ."
A tsakar gidan su Aunty fati sukai cikibis da ummah aunty fati tace "yauwa ga aunty nan ma daman wajenki zan shiga yanzu "ina jinki me zaki shigo yi? tmbyr ya dan bawa aunty mamaki amman dai ta danne tace "muje daga ciki mu zauna muyi mgn
r ai kamar zaifi ?A'a muyi anan "nan aunty fati ta zayyane mata komai tana dasa aya umma tace "a'a fati babu mai kamar maryama yayi shaawar bawa muktar aure "meye illarsa aunty ?tayi mgnr tana zaro mata ido itama ummah cikin zaro ido tace "illoli dayawa
, na rasa meke damunku ?ta qarasa mgnr da karfi tare da yarfar da hannu ."
"Aikuwa tunda har muktar yace yana sonta ko sama da kasa zasu hade sai anyi auren sai duk abinda zai faru ya faru "sama da kasa bazasu hade ba haka zalika babu abinda zai far
u aure ne dai bazaa yi shi muddin kika ga anyi wannan auren to maryama ce da kanta taji tana so amman wallahi babu wanda ya isa yayi mata auren dole hayaniyarsu ce ta fito da aunty salma da aunty wani irin asirtaccen murmushi aunty salma tayi tare da karka
cewa tana kallonsu .""Bata fada miki akwai wanda suke maganar aure dashi ba ?"ta fad'a amman wannan maganar karya ce babu kowa saboda duk abinda ke faruwa acikin gidan ina sane dashi, dan haka karya ne babu wanda yake sonta idan kuma har akwai ya fito mu
gansa "
tana gama fad'ar haka umma ta juya zuwa bangaren ta, duk suka bi bayanta da kallo".
Bayn kamar minti biyu ummah ta fito hannuta rike dana sadam a d'an rikice aunty salma ta maida kallonta sosai garesu "ba kowa bane illa sadam shine wanda
suke soyayya da maryama."aunty ta tsura ma ummah ido idanunta na kawo ruwan hawaye."aunty salma zaro idanu tayi tana girgiza kanta bata so saka bakinta cikin maganarsu ba amman ya zama dole tace wani abu dan haka tace "umma yaushe suka fara so.."bata ba
ri ta qarasa ba tace " bakiyi tsammanin faruwar hakan ba ko ? to haka rayuwa take salma sadam shine wanda zai auri maryama da izinin allah "ba aunty da Aunty salma da sauran mutanen dake tsaye ba shi kanshi sadam ya shiga rudani da tashin hankalin jin abi
nda mahaifiyarsa ta fad'a "taya ummansa zata masa haka ?" yaushe suka yi haka daita ."?yayi wa kanshi tambayar ajere yana had'a zufa .
"Gsky wannan had'in yanzu ne ,wallahi a yanzu aka shiryasa ta kalli sadam "da gaske kuna soyayya da maryama ?kas
a amsawa yayi dan gbdy ya gama daburcewa kwakwaluwarsa ta toshe kansa ya cunkusheya rasa me zai fad'a mata yayi dan duk abinda aunty salma ta fad'a haka ne a yanzu aka shirya komai kai shi sai da suka fito yasan dalilin da yasa mahaifiyarsa ta fito dashi
"kun gani ba ai bazai iya cewa komai ba dan wannan had'in shirin yanzu ne sam sam babu maganar a kasa "Ke salma bana son makirci da shashanci banza d'anki ko d'ana ?"
"d'anki ne amman wannan had'in yan.." babu ruwanki had'in yanzu ko akwai maganar a k
asa naki ido ne idan kuma kikace zaki bi dare kibi dubu akan maganar nan zaki mutu ."
"Kai sadam kalleni nan ya d'ago kwayar idanunshi da kyar ya kalli Aunty fati "karka boye min komai sadam kasan matsayinka a wajena ina sonka fiyye da ya'yan ciki
na nan kuma jikin ummah ya fara yin sanyi ,"nan ji duk abinda mahaifiyarka ta fad'a amman ina son naji gskyar magana daga bakinka ,da gaske ne sadam kana son auren maryama"? ya runtse idanunshi gam yana jin wani sabon tashin hankali na
ta'ba zuciyarsa
da kwalkwaluwarsa sai data sake tmbyrsa sannan ya bude idanunshi ya kalli mahaifiyarsa dake tsaye cikin tashin hankali tana dubansa ,a yanayin yadda take kallonsa bazai iya kunyatata a bayyanan nasi ba".
"kai nake sauraro sadam wallahi da gaske zan
iya bar maka maryama na nema muktar wata matukar kana sonta " jikin ummah ya sake yin dan tasan akwai soyayya a tsakaninsu ,"kace wani abu "da gaske ne aunty ?ya fad'a cikin wata irin murya mai cike da tsananin tashin hankali "aunty salma ta zaro ido tana
cewa "kai wallahi aunty fati karya ne , babu wata soyayya a tsananinsu "kinga salma magana ta qare sadam nawa ne koda karya ne tunda ya amsa da bakinsa bani da ja domin soyayyar sa dabam ce acikin zuciyata "shiru aunty salma tayi dan ta dade dasanin son d
a take wa mahaifinsa ne ya juye kanshi .dariyar mugunta aunty salma tayi ta juya ta koma