Showing 105001 words to 108000 words out of 172989 words
masa sannan ya kasa mata biyayya ta matsawa rayuwarsa dayawa akan maryam ,shi kanshi baya jin dadin abubuwan dake faruwa ,jin kukanta yake aransa yana jin kamar ya
yi kuka .“
ahankali yayi amfani da karfin zuciya irin tashi ya fara bata hakuri da rarrashinta “sweetheart Kiyi hakuri nasan bana miki yadda kike so Kiyi min addua wallahi a shirye nake da na canza in zama mai faranta miki ,kuma wallahi ina son yan’uwana
sweetheart wani dadi ne ya ziyarci zuciyar mami dan abinda tafi bukata kenan ta dade tana adduar ya canja .”
ya qara gyara kanshi akan cinyar sweetheart dinsa “sweetheart ki yafe min ko zan samu sausaucin abinda nake ji araina kada zuciyata ta buga sw
eetheart ,damuwa tayi min yawa wallahi ni kadai nasan halin da zuciyata take ciki a haka kamar lafiyayyen mutun ne amman sam ba haka bane mutun ne mai dauke da mummunar ciwo a qirjinsa da zaki barni haka babu nauyin kowa akaina zanfi ji dadin rayuwata sai
dai zuciyata taji da damuwa daya amman yanzu damuwa tayi min yawa na rasa ya zanyi da rayuwata wallahi zan gwamaci mutuwa sweetheart akan
rayuwar da nake .”mami tayi saurin saka hannu ta rufe masa bakinsa bata son taji batun zai mutu idan ya mutu tayi yaya
ai ita babban burinta ta mutu ta barshi a duniya, tana shafa kanshi tana jin sonshi har acikin bargon zuciyarta “ki yafe min sweetheart “adamcy baka min laifin komai ba ban ta’ba rikeka araina ba kullum addau nake maka d’ana sai dai abu daya nake só kamo
. ina son ka sausautawa maryam ka zauan da mace mafi cancanta ,maryam ta cancanta kowani nmj idan ya sameta zaka ji dadin rayuwa daita mace ta gari ya dago kanshi yana kallonta ya saka hannu shi ya rike kunnuwansa bazan iya ba sweetheart “but I promise y
ou in sha allahu zan kawo miki matar da zan aura in sha allahu zan faranta miki zakiyi farinciki da zabina amman batun wannan yarinyar fa gsky sweetheart sai dai kiyi hakuri .he ending the talk with a smile .”
mami tayi shiru tana dubansa sam adamcy
baya ganin girmanta baya tausaya mata duk son da yake ikirarin yana mata abaki ne bai kai har zuciyarsa ba .”shiru kawai tayi tana jin babu dadi ko kadan acikin ranta tana son zubar da hawaye amman data tuna irin matsifar da hakan zai jefa rayuwarsa da
alamuransa sai ta fasa sai dai yadda zuciyarta take tukuki ta tabbatarwa kanta tana cikin tsannain damuwa akanshi, idan batayi gaugauwan kawar da hakan aranta ba shima wani bala’i ne ga rayuwarsa runtse ido tayi zuciyarta na shirya mata yadda zata kawo qa
rshen komai “Sweetheart me kike tunani haka ?”muryar ATA ne ta katse mata tunani , harara ta maka masa tana cewa “ina ruwanka da abinda nake tunani ?wayarsa ya ciro ya kira daya daga cikin yaransa ya bashi umarnin a shigo da komai na kayan abinci enough .”
Cikin kankanin lokaci aka dinga shigo da kayan abinci sai daaka cika store tab da kayan abinci babu abinda babu na amafani haka ma fridge tun a ranar komai ya sauyawa maryam sunci mai kyau ita da mami su sha mai kyua, sai abinda suka ga dama suka gi
rka kuma basuyi wa ATA tayi ba shima bai damu ba tsabgogin gabansa kawai yake yi sai da yamma ne ya dan saci kallon mami yace “sweetheart ko zan samu irin coffee da kike min ?zaka samu mana amman a wajen matarka ba “tun da yaji ta fadi haka bai sake cewa
um ba bare um um, ya cigaba da danna wayarsa maryam najin haka ta matso kusa da mami tace “mami dan allah Kiyi masa mana “wani kallo mami tayi mata na rashin zuciya irin nata ,mutun bai damu da kai ba amman kai kabi ka damu kanka akanshi “please mami ai
kema kin iya kije kiyi masa ta rage murya sosai tace “idan nayi bazai sha ba amman muje muyi masa tare zai sha mami ta tsura mata ido kawai tana kallonta cike da tausayawa tare suka shiga kitchen din sukayi sai dai koda ta fito parlour bata gansa ba a d
’akinsa ta sameshi zaune akan kujera yana amsa kira taja qaramin table din glass din dake tsakar dakin ta dora tray din akai ta tsiyaya masa acikin a cup tace “gashi !”ba
tare daya kalleta ba ya dauka ya fara sha dan a bukace yake .”
ta juya ta bar d
akin tana rufo masa kofa kwanan mami uku a gidan wanda hakan ya haifar da sukuni da kwanciyar hankali ga maryam har mamakin kanta tayi yadda yanayin jikinta ya canza, domin mami nayi mata duk wani abinda zai kwantar mata da hankali tare da kawar mata da
damuwarta da zarar taganta cikin damuwa sai tayi duk abinda zata kawar da damuwar sannan hankalinta zai kwanta sosai take kula da cin abincinta mussaman ta dinga had’a mata fruit masu gyara skin da qara ni’ima ajiki most especially yankakkiyar ayaba da
soyayyiyar gyada da kankana da madarar ruwa a had’a waje daya wannan kam kullum sai mami ta had’a mata ta bata ,wannan had’in mai dadi yana aiki abu biyu ne ajikin nmj ko mace yana gyara skin sannan yana qara ni’ima ajikin mutun. zaman mami a gidan ya d
an kawo sauyi domin duk abinda ATA zai yi na rashin mutunci tana taka masa burki da fushinta domin dai idan ba fushinta ya gani ba baya kin abinda yayi niyya kuma yanzu babu laifi yana cin abincin gidan .”
Da misalin karfe shida na yammacin ranar
da mami ta cike kwana biyar a gidan ATA ya tashi da rashin lafiya na ciwon kai mai tsanani wanda har sai da doctor dinsa yazo ya dubasa inda yayi wa doctor bayanin yadda yake jin ciwon Kan kuma koya sha magani baya masa sauki yadda yake buqata, doctor ya
yi gwaje gwaje ,a inda yace akwai kwayoyoyin da yake sha wanda sune suke haddasa masa wannan ciwon, dan shiru yayi yana tunani dan shi a sanin da yayi wa kanshi baya shan wata kwaya dama sigari yace itama yanzu ba koda yaushe yake shanta ba amman kwaya kam
baya sha “doctor bana shan kowani irin kwaya amman ko zaa iya duba wace irin kwaya ce ?”eh zaa iya dubawa kuma zaa gano kowani iri ne amman dole sai kaajiye ayyukanka na gobe kazo hospital .” ATA ya gyda kai alamun zai zo .”
tun zuwan doctor maryam
ta fahimci bashi da lafiya ne dan duk sanda kagansa to rashin lafiya ne bayan doctor ya gama duba ATA maryam ta shigo dakinsa hannunta dauke da tray ta sameshi zaune akan doguwar kujera yana sanye da singlet da gajeran wando kallo d’aya tayi masa ta dauke
idanunta sakamakon yanayin data tsinci kanta d’an kwantaccen sumar jikinsa kawai ya isa tadawa mutun shaawarsa ,taja dan karamin table din glass din dake tsakar dakin ta dora cooler din abinci a kai ta zuba mishi a cikin plet tasa spoon tace “ga abinci sh
iru bai ce uffan ba ta sauke numfashi ta sake bud’e bakinta akawo maka coffe ?ya girgiza mata kai kawai alamun baya bukata wani sanyayyen numfashi ta sauke a boye a raina tace “alhamdulillah yau dai da alamun mutane kirki ne a kusa babu rashin mutunci
,kamar baka jin dadi ?sannu allah ya baka lafiya meke damunka “?ba tare da ya kalleta yace “ki kama kanki dan naga kina wani jin dadi dan kinga sweetheart atare
damu kisani ba tabbata zatayi a gidan nan ba zata wuce idan ta wuce kuma kema Kinsan me zai far
u ?tace babu abinda zai faru sai alkhairi allah dai ya baka lafiya baby nah tana rufe bakinta daya daga cikin wayoyinsa ta soma ringin zuciyarsa cike da mamakinta karo na biyu kenan da ta kirasa da wannan banzar sunan kamar ya tashi ya gaugaura mata mari
amman jikinsa babu kwari shine ma yasa ya qasa tashi kuma yana jin yadda zai ce tabashi wayar maryam ta fahimci haka, dan haka cike da sanyi jiki ta qarasa inda wayar take akan katifarshi ta dauko ta duba fuskar wayar nan take gabana yayi wani mummu
nan faduwa sakamakon ganin hoton wata kyakkwar yarinya a fuskar wayar mijinta .”
yarinyar kyakkyawa ce duk da fuskarta kamar zane ce aranta tace”ko dai wannna ce yarinyar mafarkin sa?kwakwaluwarta bata kai ga bata amsa ba “tajiyo sautin muryarsa c
an qasan makoshi yace “bani wayata “jiki a matuqar sanyaye ta kai mishi sañan tace bari na wanke maka toilet shi dai bai ce mata uffan ba har ta shiga ta wanke ta fito yana cin abinci yace “bani abinsha a fridge da sauri ta bude demsino na gwangwani ta d
auko masa ta hado masa da ruwa nestle ta ajiye tana jin zuciyarta babu dadi duk da yarinyar mafarki ce amman abun ya damu zuciyarta zata cigaba tsayuwa ad’akin yace “please leave! simi simi ta fito daga d’akinsa yaja tsaki tare da cewa nonsense mace sam b
abu class ,to wani aji zatayi wannan ?allah na tuba ai isasun mata né masu aji shi yaji ajikinsa muddin zai had’u da princesa dinsa tabbas zata fita dabam acikin mata ranar da wuri ya kwanta bacci sakamakon maganin bacci da alluran da doctor yayi masa .”w
aahegari kuwa karfe biyu a office din doctor tayi masa duk wani gwaje gwaje anyi masa, inda doctor yace zai zo gida ya kawo masa abinda suka gani daga nan kai tsaye gidan mb yace a wuce dashi sun jima tare,bashi ya dawo gidan ba sai bayan ishai.”
Da misalin karfe goma sha daya na dare maryam ta fito daga dakinta sanye da kayan bacci iya cinyarta sai dai ta daura zani a saman kayan baccin kai tsaye d’akinsa ta shiga bata gansa ba dan haka ta sauko qasa cikin tsananin tashin hankali har zanin jiki
nta ya fita bata sani ba “yaya Adam kazo mami bata iya numfashi sosai ,ai da wani irin mugun sauri ya zabura ya mike yayi wulli da remut din hannunsa bai san yaakayi ba sai ganinsa a dakin maryam yayi har tsakiyar gadonta ya daga kan mami ya daura bisa k
afafunsa yana qoqarin tallabota ya sauko daita ta girgiza masa kai “dan girman allah sweetheart wallahi baki san yadda naji a zuciyata ba “ke tsayuwar me kikayi kije ki dauko min wayata” yayi mgnr a tsawa ce yayinda maryam ta juya da sauri ta fita “haba ad
amcy ka dinga sausautawa maryam mana .tayi maganar da kyar”
furzar da iska yayi yana kamo hannun mami cikin nashi “adamcy nah! mami ta kira sunansa”na’am sweetheart sannu gobe gobe nan zan bar kasar nan dake “duk inda zaka kai ni bazai hanani mutuw
a ba ,dan haka ma gara ka barni kawai a kasata idan mutuwar ce allah ya bamu ikon cikawa da imani ta qarasa maganar da kyar tana sauke numfashi “kinji abinda naji kuwa sweetheart da kikayi zance mutuwa nan dan girman allah ki daina fad’a min haka “to ada
mcy mutuwa ai dole ce maryam ta shigo ta mika masa waya ta hawo har saman gadon ta riko hannun mami cikin nata suka sakata a tsakiyarsu mrym tana mata sannu yayinda ATA Ke qoqarin kiran layin Aunty shahida “karka kira shida ka daga mata hankali sannan k
iranta bazai hanani mutuwa ba idan mutuwar ce.” saurin runtse idanunshi yayi .”
Bai kula maganar mami ba ya cigaba da kiran layin shahida sai dai kiran na shiga bata d’auka daga adamcy har maryam duk suka zubawa mami ido hankalinsu a matukar tashe
“maryam adamcy ku yafe min had’aku aure da nayi “haba mami dan allah kiyi shiru numfashi ki har yanzu bai daidaita ba kuma aurenmu da kika hada baki mana laifin komai ba inji cewar mrym “idan Ke ban miki laifi ba ai nayiwa adamcy “ki kwantar da hankalinki
mami shima baki masa laifi ba muddin muna raye zai faranta miki har ma bayan ranki “shi kam ATA gabad’aya ya nemi natsuwar ya rasa dan har layukan mijin aunty shahida ya kira bai zuwa haka ma layin likitan dake dubasa yana qoqarin durowa daga kan gadon
mami ta riko hannunsa ya dawo ya zauna cikin tsananin tashin hankali “dan allah sweetheart karki bari sanadiyar careless dinki na rasaki,wallahi bazan iya daukar zafin jarabawar nan ba “yayi mgnr kamar zai yi kuka “ haka rayuwa ta gada adamcy kuma ita ray
uwa cike take da qaddarori da jarabawa iri iri sai dai idan baka cikin duniyar nan, yau dadi ne gobe kuka dukkanin rayuwa rubutattacen lamari ne daga rabbi da d’an adam yana gane wannan da bazai tsaya batawa kansa lokaci ba kamar yadda ka kasa ganewa “tan
a gama fadar haka idanunta suka juye numfashinta ya soma qoqarin tsayawa .”
“sweetheart sweetheart!! Kawa yake iya kira yayinda maryam ma ta dinga kuka tana kiran sunanta atare suka nemi durowa daga kan gadon suka jiyo sautin muryarta can kasa “ma
ryam bani ruwa kishi nake ji .” ya dawo da sauri yana cewa “shikenan sweetheart mutuwa zakiyi ki barni ,dan allah karki min haka sweetheart, dan girman allah karki min haka ya allah ka d’auki rayuwata ka bar ta mahaifiya ta” ya fad’a yana damke hannunta ci
kin nashi gam wasu hawaye masu zabi suka gangaro masa “adamcy Nah kuka kake yi ?ya sauke numfashi yana kai hannunta bakinsa inda hawayensa ke diga “kayi hakuri haka rayuwa ta gada ,kana cikin jin dadi sai allah ya jeho jarabawa cikin rayuwarka “ka rik
e yanuwanka adamcy saboda kai ne kamar babba agaresu ,ka kyautata masu ,ka tsaya masu a
dukkanin lamarinsa “dan allah sweetheart ki daina fad’ar haka “dole fa zan mutu adamcy fatana allah yasa mu cika da kyau da imani .”
Tayi shiru can ta motsa bakin
ta “ka min wani alfarma adamcy ya d’ago ya tsura mata ido yana sake damke hannunta cikin nashi “me kike so sweetheart just tell me matsawar zakiyi farinciki ki dawo daidai “ka ta’ba kusantar maryam ne amatsayinta na matarka ?shiru yayi yana duban mami zuc
iyarsa na bugawa da karfi ganin haka yasa mami ta soma tari wanda da kyar tarin yake fita “sweetheart sannu ya furta yana kwallawa maryam kira” ki kawo ruwan mana ko dan ba uwarki bace kike westing time “cikin yanayi na ciwo mami ta cigaba da magana “na
tambayeka baka bani amsa ba “a’a sweetheart babu abinda ya ta’ba shiga tsakaninmu “yanzu ka kyauta kenan adamcy ?wata shida kenan da aurenku amman ka kasa sauke wannan nauyin kana ganin allah zai barka haka né ?shiru yayi yana daura hannunsa a goshin mami
“me maryam ta tsare maka adamcy ?ta fad’a tana wani irin numfashi mai zafi idan laifi ko haushi ne nawa zaka ji domin nice silar komai .”
“Kiyi hakuri sweetheart ya fad’a adaidai lokacin da maryam ta shigo hannunta rike da roban ruwa ya fixge da kar
fi “idan mutuwa ne tuni ta mutu kawai kije ki kawo ruwa kinje kinyi zamanki saboda ba mahaifiyarki bace cike da rawar jiki ya bude murfin roban yana mai tallabo kan mami ya kai goran ruwan bakinta ta sha sosai sannan ta kawar da bakinta tana cewa maryam ko
ma d’akin adamcy zai zo ya sameki kinji allah yayi miki albarka, jiki a sanyaye ta juya ta bar dakin sai dai ta qasa shiga dakinsa ta tsaya corriedor ta jingina bayanta da bango tana zubar da hawaye.”yanzu idan mami ta mutu ya zan yi da rayuwarta “?tayiw
a kanta tmbyr tana fashewa da kuka .”
“Kayi min wannan alfarmar adamcy baka sani ba ko iya alfarmar da zan nema kenan daga gareka ya matso da kunnensa daidai bakinta dan yaji alfamar da take so “sweetheart ki fad’a min abinda kike bukata in promis
e you zanyi “ina son ka fad’a min gsky kana da cikakkiyar lafiya kuwa kamar yadda sauran maza suke ?numfashi ya fesar yana mai dagowa ya tsura mata ido “yau ba ranar wasa bace bare ya kawo rainin hankalin da ya saba ,dan hk da sauri yace “lafiyata kalau s
weetheart ,amman wannan tamvayar ba yau bane karo na farko da kika min ,idan bani da lafiya kece mutun ta farko da zan fadawa “to na yarda tunda kai ma ka tabbatar da lafiyarka kalau ina son kaje ka sauke nauyin da allah ya rataya akanka na aure da maryam
“lumshe idanunshi yayi kana ya bud’e ahankali yana dubanta ko kifta idanu bayayi ko bata fito fili ba ya fahimceta sosai “idan kayi min haka ko na mutu ruhina zai samu salama adamcy ,lalla a illalla muhammadu rasulillahi sallahu alaihi salam,dan allah adam
cy ka cika min wannan
burin , kayi min wannan alfarma kuma a yanzu ta damke hannunsa gam cikin nashi jikinta na rawa kamar yadda jikinsa yake rawa yana furta inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ita kuma mami tana salati tana furta ya cika mata burinta .”
Gabad’aya ATA ya gigice ya fita haiyacinsa ganin halin da mahaifiyarsa take ciki ya juya da sauri ya fita daga cikin dakin a corriedoor yaga maryam tsaye ta daura hannuwanta duka a saman kanta tana rusa kuka ya tsura mata ido cikin tsnanin tashin
hankali bashi da wani lokacin ‘batawa gara yayi abinda zai yi ya faranta ran mahaifiyarsa ko bayan ta mutu