Showing 90001 words to 93000 words out of 132482 words

Chapter 31 - ZAZZAFAN SO COMPLETE

01 Sep 2026

24

ke bata mamaki shine sau biyu Haala tazo gidansu, duk maganganun da suke yi a waya ne gashi gobe wa,adin abba zai cika.!!



📝



*HAJEEYAH KHAREEMERH*

[17/03, 2:37 p.m.]

UMAIMA BASHEER: ♥















*ZAZZAFAN SO*

(Masoyin k'warai)

*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*

💔💔

*By*

*Karima Tijjani Mansur*

*(Hajeeyah Khareemerh)*

*Dedicated to unique in your love heart*

📄

*53*

*Yau* jin ta take gaba

-d`aya kamar ba ita ba, komai tana yinshi ne cikin sanyi. Ba wai damuwa ce ta mata yawa ba, sai dai kawai fargabar bak'on da zatayi. Ta nemi dalilin damuwar itama ta rasa.

Ita ba bakin maza ne batayi ba, bare ace rashin sabo ne, takanyi bak'i idan ta ka

ma saboda yanayin aikinta.

Sannan gefe guda tana son sanarwa mama batun zuwan bak'on shima taji ta kasa hakan. Hatta Basheer, ko Zainab ji tayi tana jin nauyin sanar musu bare kuma abba. Sai ta fara tuhumar kanta. _"Zuwan nashi zuwa ne fa na ziyara kawa

i, ba alak'ar soyayya ce tsakaninsu ba, idan ma zata bashi matsayi zata iya kiranshi da abokinta kawai.._

_To mene ya kawo jin nauyin da fargabar."?_

Wani b'angaren na zuciyarta yace, _"Saboda baki sanshi ba baki taba ganin shi ba.!!"_

Sai kawai ta ya

rdarwa kanta wannan dalilin ne yasa.

Har kusan k'arfe uku da rabi tana d'aki a kwance. Mufida na ta kai kawo cikin d'akin, sai da ta tambaye ta ma, _"Aunty ko baki da lafiya ne."?_

Ta girgiza kai kawai.

Jin ana kiran sallar La,asar ne yasa dole ta ta

shi. Tuna cewa, _yace mata da yamma zai zo fah."?_

Sai da tayi wanka sannan tayi sallah lokacin zainab itama ta lek'o d'akin. Ta kirata.

"Zainab zo kiji."

Zainab ta shigo d'akin gaba-d`aya ta zauna kusa da ita, "gani meke faruwa."?

Ta girgiza kai, _"

babu komai,_ sannan ta waro ido, don tambayar tasa ta tsargu. _"Me kika gani.?_ Ta tambaya.

Zainab ta girgiza kai.

"Babu komai gani nayi kin kirani."

"Okey Abba yana nan."?

Hafsah ta tambaya.

"Ya fita tun dazu."

"Basheer fa."?

Zainab tayi mata

kallon mamaki sannan tace. "Ya sa kayan kwallo ya fita."

"Okey.."

"Bak'o zanyi neh!!

Ta fad'a a hankali tana kawar da kai.

Zainab ta saki murmushi, dama ta lura da yawan wayar da yayar tata keyi kwanakin nan.

Ta waro mata ido, "Really aunty."?

"A

a to mene kike mamaki don nace zanyi bak'o"?

Zainab ta kuma yin murmushi, "Babu komai, da yamman nan zaizo."?

"Eh, ni duk na kasa komai ma.!!

Ta fada tana k'arasa shafa mai a hannunta.

Zainab ta boye dariyarta. Sannan tace, "Meya sa toh aunty."?

Tan

a sane tayi mata tambayar.

"I don't really know, kawai bana son ya raina ni, so kuma na kasa komai."

"Kin tanadi kayan da zaki sa."? Inji zainab.

Duba Ki zab'o min.

Zainab ta mik'e ta shiga dubawa, har kayan cikin akwatu, itama tana son ta fito da

yayar tata.

Daga k'arshe dai ta nemi mata, wata pink d`in atampha riga da skirt dinki stone work yayi kyau sai shek'i suke, ta ciro mayafi, da sark'a d'an-kunne zobe, agogo duka ta ajye mata.

"Kisa wannan aunty zaki yi kyau."

Ta kalli kayan ta tab'

e baki, kawai ni yazo zai tashe ni tsaye wallahi.!!

Zainab tayi murmushi ta gimtse. Hafsah ta mik'e don saka kayan. Zainab Tayi saurin dakatar da ita da tambaya, "Aa yaya ba zaki shafa ko powder bane."?

"Ke kyale ni fa, ba wai kwalliya zanyi ba yana zu

wa kuma zai tafi."

Zainab ta zaunar da ita bisa gado. "Please aunty Ki bari na shafa miki powder."

Bata mata musu ba, saidai ta had'e rai.

Zainab ta mata saasauk'ar kwalliyar powder, sai lining na kan ido, da mascara sai can janbaki. Nan da nan fara

r fuskarta ta d`auki haske da sheki tayi kyau matuk'a.

Tana mik'ewa da nufin saka kaya, kirashi ya shigo. Taji gabanta ya fad'i, kamar ta share sai kuma ta d'aga.

"Ranki ya dad'e na iso cikin unguwar fah."!!

Ta waro ido, ta kalli zainab.

Number nawa

ne ma gidan. Baki fad`amin ba"?

Batayi magana ba sai ta turawa Zainab wayar.

Zainab ta rik'e, tasa a kunne, dai-dai lokacin yana cewa, "Kiyi hak'uri nasan na takura miki amma don Allah ki fad`amin."

"Hello." Zainab tace, sai yaji ba muryata ba

. Cikin muryar tausayi yace, "Don Allah ina take me wayar, please kada kuyi min haka."

Cikin muryar shi zainab ta fahimci nutsuwa a tattare dashi, sai ya bata dariya da tausayi lokaci guda.

"Kana ina yanzu."

Ina unguwar da ta fad`amin.

Ina kenan."?

"Sallari tace koh."?

"Eh nan ne."

"House no. 35." Inji Zainab.

Thank you, in sha Allah gani nan."

"Amma please ina take."? Ya tambaya da damuwa.

"Bata kusa ne."

Kamar zai k'ara magana, sai kuma yace, "Okey thank you."

Zainab ta kalli, Hafsah,

lokacin har ta gama sa kaya. A d`auki d'an kwali zata d'aura mata.

"Yaya ya kusa isowa."

Batace komai ba.

Zainab ta mata d'aurin, yayi kyau sosai.

"Kinyi kyau Yaya."

Ta fad'a tare da mik'a mata mudubi.

Hafsah ta kalli, madubin tayi kyau sosai. Tay

i murmushi.

Zainab ta tambaye ta, "Yaya kin fadawa mama."?

Ta girgiza kai, Aa ai ba dad'ewa zaiyi ba kuma friend dina ne fah kawai.

"Hmm, Zainab tayi murmushi.

Sai kawai ta fice.

"Mama, aunty Hafsah wai bak'o zatayi."

"Waye zaizo."?

Nima ban sani

ba, inaga wanda suke waya dashi ne.

Mama tayi murmushi, "Ai shikenan tunda bata gayamin ba."

Zainab tayi dariya itama.

"Idan kinga bata bashi ruwa ke ki kai mishi kinji." Inji mama.

"Toh, zainab tace ta juya ta nufi d'akin da Hafsah take.

T

ana zaune jugum, wayarta na gefenta, wayar na ta fara k'ara, amma ko kallonta batayi ba, kafin Zainab tayi wani yunk'uri har wayar ta tsinke.

Ta kalli Hafsah daidai lokacin kuma, wani kiran na k'ara shigowa.

Yaya menene wai, kiranki ake fah."

Ta yatsi

na fuska. "Ki kyale ni kawai idan zaki d'aga ki d'aga amma fa kyar idan zan fita ma."

Zainab tayi mata wani kallon mamaki, tana so tayi magana amma bata son wayar ta k'ara katsewa ba,a d'aga ba, don haka da sauri ta mik'a hannu ta d'akko wayar, ta d'aga

kiran.

"Hello."

Tace dashi.

Cikin murya mai cike da damuwa yace, _"Don Allah kibawa yayarki hakuri wallahi idan zuwana zai zamar mata damuwa, na fasa, zan juya kawai."_

Da sauri zainab tace, "Aa fah, tana wani abu ne. Kana ina ne."?

"Ina kofar gi

dan da kika fad`amin house no 35."

Okey please ka dan jira. Zainab ta fad'a.

"Okey thank you, amma please ki fad`amin gaskiya meyasa Hafsah taki amsa wayata, kinji, don Allah."

Hafsah ta gyara zama, tana jinsu, tunda wayar kamar hands-free take. Ita

kanta batasan dalilin abinda takeyi ba, kawai ta tsinci kanta da rashin son hada id'o dashi.

Allah babu komai fah.

"Okey thank you."

Zainab ta ajjye wayar ta kalli Hafsah. "Don Allah Yaya ki daina kinga ke fa kika ce mishi yazo."

Hafsah tayi sh

uru, ta zubawa zainab ido kawai.

Zainab taja mayafinta zata fita.

"A kujerun waje zaki ce ya zauna."

Hafsah tayi mata magana.

Ta gyada kai ta fita kawai.

Tana bude gate ta hango bayan shi, yana tsaye daga gefen dama na gidan, ya juyawa hagu bay

a. Babu mota a wajen d`in mota bare ace da ita yazo.

Zainab ta dan matsa har zuwa kusa dashi sosai, sannan tayi mishi sallama.

Assalamu alaykum."

Ya juyo da murmushi a fuskar shi. "Wa alykum salam

Zainab zuciyarta tace, _Masha Allah, amma wannan aun

ty Hafsah take wa yanga. Mutum ne mai kwarjini da cika ido, ga kyau mai d'aukar hankali._

"Kaine bakon Yaya Hafsah koh."?

Ya d'aga mata kai.

"Okey, ka k'araso toh."

Tace dashi.

Yayi mata murmushi tayi gaba ya bita a baya, har suka iso farfajiyar w

ajen can gefe da kujeru a wajen da d'an table.

Zainab ta mishi nuni da kujerun sannan tace, "Ka zauna ga kujera nan, tana zuwa itama."

"Okey nagode, sannu kinji." Ya fad'a a shigen zuci.

Zainab ta k'ara kallon shi sannan ta shige gida.

Yaya Yaya,

gaskiya mutumin ya hadu kinganshi kuwa, wallah Masha Allah, gashi da kwarjini da...

"Hmm, Hafsah ta katse ta."

"Don Allah Yaya ki tashi kije kinji."

Ta kalli Zainab, tana son fita, amma nauyi takeji, amma babu yadda zatayi.

Zainab ta d'auki jan jamb

akin data sa mata dazu zata k'ara mata, ta kauce.

No ki bari zainab haka ma ya isa.

Ta muk'e ta k'arasa jikin mudubi ta kalli kanta, tabbas tayi kyau.

Zainab ta duba ta dakko mata takalmi me sauk'in tudu, ta sanya.

"Zoki raka ni Zainab." Hafsah

tace.

Noo Yaya, kije ke kad'ai, please."

"Aa nace kizo fa."

Please Yaya Allah kikaje ke kad'ai sai kinfi kwarjini a wajen shi.

Hmm, inji Hafsah, a zuciyarta tana cewa, _"an gaya miki so nake na burge shi."_

"Yayah.!!

Zainab ta kirata da k'aguwa.

T

a kalli Zainab ta mata alama da ido, _"mene."?_

"Kina wasting time Don Allah ki tafi kinga babu dad'i fah."

Dole ta bude k'ofa ta fita, gabanta nata fad'uwa.

Yana zaune, hankalinshi gaba-d`aya nakan, flowers (fulawowin) da sukayi wa farfajiyar

gidan ado, don ya gaji da kai kallonshi hanyar fitowa daga cikin gidan.

Ahankali take tafiya, ta k'ara saka yanga akan alhinin yangar da take tata ce ta halitta, saboda bata son k'arasawa inda zata je.

Tana hangoshi tana k'ara rage sauri. Ga k'aruwar

fargaba kuma.

Yana kallon fulawowin har yanzu, gaba d'aya ya bada hankalinshi can, don ya fitar da ran fitowarta kusa.

Hakan da yayi ya mata dad'i bata son ya jiyo sautin takunta, bare ya juyo.

Sai da ta kusa zuwa inda yake sannan ya juyo.

Tunda ya

gano me tahowar ya kafa mata idanu, har ta k'araso inda zata zauna, ita kuwa da kyar take iya cira k'afarta. Tayi k'asa da idonta ga barin kallon shi, dama bata yarda sun had'a ido ba. A hankali ta d'an bude baki ta mishi sallama, sannan ta d'an ja kujera

a hankali ta zauna.

Sai da ta daidaita a kujerar sannan ya bud'a baki shima ya amsa mata, yana k'ara kai idanunshi fuskarta, "Wa alaikumus-salam."

Sukayi shuru tun bayan sallamar daya amsa.

Sai kuma taga ya dace ta mishi sannu da zuwa, tun

da bak'onta ne.

Cikin rashin daga sauti kamar koyaushe tace, "Sannu da zuwa ya hanya."?

Sai yanzu ya ji dad'i sosai har ranshi, don da har ya fara wani tunani. Ya fad'ad'a murmushi sosai.

"Yawwa, sannu kema, hope na sameki lafiya.

Ta fad'a a hank

alin dai.

"Lafiya lau Alhamdulillah."

Suka k'ara yin shuru, shi cikin nazarin irin had'uwar ta, datsaruwarta komai nata yayi mishi yadda yake so, yafi ganin kyanta ma yau fiye da koyaushe da ya tab'a ganinta. Ita kuma cikin k'aguwa da kallon da yake m

ata, da tunanin irin haduwar shi shima da kwarjinin da yake da shi, don jinta take kamar gaban wani sarki take, gaba d'aya ta takura.

"Hafsah, yau gani koh, Allah yayi yau kinga ukhashatu.!!

Ya fad'a da murmushi. Itama ta dan murmusa, bata da abin

yi ko cewa idan ba murmushin ba.

Yayi yar ajiyar zuciya a hankali.

Alhamdulillah.!!

Taji yace, sannan bayan wani d'an shuru ya furta.

"Ki yarda Allah ne ya had'ani dake, kuma shiya san alkhairan da zai kulla tare damu, shiyasa na nace miki duk d

a ke naga kamar takura ne agunki koh."

Ya k'arashe maganar yana k'ara zuba mata idanunshi, ta taga sunyi mata wani _harr_ a nata idanun, kamar wani giftawar haske.

Tayi saurin kawar da idonta gefe tana murmushin zancen shi.

"Da gaske ne kenan ni me

naci ne a wajen ki koh."?

Ya fada shigen rad'a.

Dole ta bude baki don kare kanta.

"Ni bani na fada ba dai.!!

Ta fada tana yar dariya.

Shima dariyar yayi, hmm ai ni nasani, inada naci akan abinda nake so gwara na fada da bakina.

Gabanta ya fadi

da kalmar daya fad'a, _inada naci akan abinda nake so.!_

Sonta yake kenan."?

Ta tambayi kanta, tare da d`agowa ta kalli idanunshi don tabbatar da abinda yace.

Ya jinjina mata kai shikuma, "yes.!!

Ya fad'a.

_Ta kasa tantance me "yes d`in tashi ke

tabbatar wa. Kasancewar shi mai Nacin ko kuma kalmar kan abinda yake son, dayace.? wanda maganar kai tsaye tasan akanta ake yi._?

Suka tsaya shuru shida ita, kowa cikin nazari.

Takun tafiya sukaji daya sa su dukansu juyawa.

Zainab ce rik'e da tra

y na ruwa da lemo sai _cups._

Ta musu sallama sannan ta ajye.

Bata bata lokaci ba ta juya, wanda hakan bai bawa ukhashatu damar yi mata godiyar da yayi niyya ba. Sai kawai ya juya ga Hafsah. "Thank you.!!

Yace mata.

Ta mishi alama da ido. Tana neman

karin bayani akan godiyar.

Yayi mata nuni da tray d`in yana murmushi, sannan yace, "ko ba ni aka kawo wa ba."

Murmushi tayi ita, tace, "hum.."

Kawai.

"Zan iya sha don inajin k'ishirwa.?

Ya tambaya.

Ta d'aga gira kawai.

Ta mishi kyau sosai hakan ya

sashi b'ata lokaci ya kalleta, sannan ya d`auki ruwan ya zuba a kofi, ya d'aga zai sha.

Ta zuba mishi ido ita kuma, sai taga ya fasa.

Batayi magana ko wani motsi ba taga ya d`auki bottle d`in zai kuma zuba wani ruwan.

"Oh sorry ban tambayeki ba ruwa

zaki sha ko lemo. Ni dai nafi ga ruwan."

Batace komai ba, sai mamaki daya bata, _wannan mutum akwai salo!!_

Tace a ranta.

Uhum."?

Ya kuma tambayar ta.

Ta bishi da kallo kawai, sai kawai ya zuba mata ruwan, a cup ya ajye agabanta.

"Gashi."

Yace

mata sannan ya tsare ta da ido.

Ala dole tace, thanks.

Tana ganin yanayin murmushin da yayi mai bayyana tsantsar farin ciki.

Sannan a hankali ya daga nashi ruwan ya fara sha.

Bata da bukatar shan ruwa a lokacin, kuma ko da, da buk'atar hakan ba,zata

sha agabanshi ba.

Sai da ya shanye, ya k'ara zuba wani ya sha, rabi sannan ya ajye, "Thank you."

Yace mata, wanda kafin ya fad'i hakan sai da ta lura da motsawar bikinshi ya furta, _"Alhamdulillah!._

Sukayi shuru, bai k'ara ce mata tasha ruwan ko wa

ni abu ba. Sai kallon agogon hannunshi da yayi.

Itace ta tuna da wata tambaya da tace zata mishi, don tana san tabbatar wa.

Tana fara magana, ya zubo mata idanu, wanda hakan yasa ta dan rikice sai da kyar takai k'arashen jimlar.

Um.. Kace ka taba gani

na a wurare, so ina da inane."?

Ya saki murmushi, sai lokacin ta lura da dimple d`in da yake dashi ya jinjina mata kai.

"Of course naganki sau biyu kafin na ganki a television."

Tana so ta k'ara tambayar shi, "To ina ne."?

Amma bata son ta k'ara tamb

aya.

"Na ganki a gidan biki, sannan na ganki a titi.!!abinda yace kenan yana wata iriyar siririyar dariya.

Sai ta tafi tunani, Gidan biki kuma.. Titi kuma."?

Da kyar ta samu ta tuno irin gidan bikin da yake nufi, da taimakon k'ara kallonshi da tayi ta

ke ta gano shi.

_Mutumin da taji abokan shi sun kirashi da UK ranar bikin Aysha er ajinsu sannan tabbas sunyi magana da Basheer randa suka had'u a titi._

Wato dole yace gidan biki da kuma titi.

Da sauri ta bude baki tace, waye ya baka number ta toh.

"

A hankali kuma cikin nutsuwa yayi saurin bata amsa, "Allah.. Allah ne ya bani.!!

"Hmm, koh."?

Ya jinjina mata kai.

Sannan don kada ya bata damar sake mishi magana ya fara wata magana takaitacciya, amma wacce ta rikita komai nata.

"Tun ranar naji ki

nyi min, naji inason kulla alak'a dake, sai dana rasa hanyar samun contact dinki na gano sonki nake.!!

Ya dago kai sannan ya dora, kiyi hak'uri nasan ba lallai kin shirya karb'ata ko kuma na chanchanci ki soni ba, amma inason ki bani dama mu dinga ko da

gaisawa ne don Allah."

Magiyar da yayi ya k'ara sa mata tausayin da yanayin maganar shi ya sakata.

So.."? Yau kuma"? Yanzu, ake furta mata shi."?

Ji take kamar babu wanda ya taba ce mata hakan a duniya.

Taji zaman

wajen ya gundure ta, kamar t

a tashi bar gurin, amma babu dama.

Gashi shi kuma tun bayan da yayi maganar yayi shuru ya koma kalar tausayi yaki ya k'ara furta mata koda kalma d'aya sai kallon ta da yake ta faman yi...

H hameeed!! Sukaji an kwallo mata wani kira, wanda h

akan ya sasu waige waige shi da ita.

Wata budurwa ce take tahowa daga wajen gate, sanye take cikin riga da skirt na atampha sai wani siririn mayafi wanda iyakarshi kafad'ar ta.

Da wani irin sauri take tahowa. Da alama ba cikin hayyacinta sosai take

ba.

Tana k'ara isowa kusa dasu Hafsah na k'ara fahimtar wacece. Don haka da saurin ta mik'e saboda mamaki.

Da gudu ta k'araso, ta rungume Hafsah gam, kafin Hafsan tayi wani yunk'uri, cikin kuka take magana..

"H. Hamid, Yusuf.. Yusuf!!

Mam

aki ya cika ukhashatu, ya lura ita ma Hafsah a razane take, sannan yana lura da yadda take ta kokarin kwace jikinta.

Da k'yar ta iya kwacewa, suka tsaya kallon juna.

"Ukhasha ya mik'e, ya kalli Hafsah, naga kinyi bak'uwa, koh, bari na barku ku gais

a. Thank you.!!

Ya juya, ya kama hanyar fita. Basma ta bishi da kallo.

Hafsah taji kamar ta kurma ihu, wannan wacce irin masifa ce, Basma a gidansu, a irin daidai wannan lokacin da take da bako irin wannan, kuma yake furta mata abubuwa masu muhimmanci.

"??

Ta bishi da ido har ya isa gate tana gani, sukayi musabiha da mai gadi, yana fita ta juya itama da gudu ta wuce cikin gida, bata tsaya ko k'ara kallon Basma ba.

Aka bar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login