Showing 57001 words to 60000 words out of 96447 words

Chapter 20 - Wata Soyayya Complete

03 Sep 2026

17

yin smooth sai wani glowing take ga k'amshi na musamman da koya ta motsa jikinta yake tashi. Sanye take cikin farin wandon three quarter mai d'an fad'i sai half vest pink color ba

komai a kanta sai manyan twist dake kanta wanda ya sauka har kan kafad'unta gaba d'aya hankalinta ya tafi kan cup d'in dake kan cinyarta sai faman sha take tamkar mayunwaciya har wani lumshe ido take tana kad'a kai alamun tana mugun jin dad'in abin.

K'o

far falon aka bud'e Abdallah ya shigo bakinshi d'auke da sallama, shigar k'ananun kaya ne a jikinshi bak'in wando da shirt mai dogon hannu red colour ya matse wuyanshi da tie black color, sanye k'afarshi cikin boot red yayi matuk'ar yin kyau wannan mayen t

uraren nashi na biye dashi kamar bodyguard gaba d'aya hannayenshi soke suke cikin aljihun wandonshi ya shiga takowa idanunshi kyarr akan Janaan wadda sam batayi zaton shigowarshi yanzu ba ganin bai dad'e sosai da fita ba hakan yasa cikin hanzari tayi sauri

n b'oye cup d'in hannunta a bayanta gabanta na fad'uwa sai faman zare ido take tana murmushin yak'e, daga yadda tayi masa sannu da zuwan yasan batada gaskiya hakan yasa yana k'arasawa inda take yaja tunga yayi mata tsaye akai yayi crossing hands d'inshi a

faffad'an k'irjinshi yana kallonta batare dayace komi ba.

K'asa tayi da kanta tana shafa gefen wuyanta ALLAH yasa dai bai gantaba ita kanta wannan shan kwakin datake ya isheta baso take ba to amma ya zatayi da ranta itakuma haka ALLAH ya tsaro mata nata

cikin d'an kimanin watanni biyu da rabi babu abinda take sha'awa sama da garin kwaki Abdallah yayi masifa da bala'in yayi buyagin nashi da hayagagar duk a banza saidai idan baisa k'afa ya fita daga gidan ba.

Ganin baice uffan ba yasa ta d'ago kai ta ka

lleshi taga yadda ya tsareta da ido yana mata wani kallon tuhuma.

"Bakida gaskiya Baby". ya fad'a kanshi tsaye, soshe soshen kai ta fara kamar zatayi kuka itama d'in batace komaiba ALLAH ALLAH take yabar kanta ta cigaba da shan abinta yawunta har gudany

a yake.

Hannu yakai bayanta inda ta sak'e cup d'in ya d'auko shi ya kalli kwakin dake ciki kusan cike, dawo da kallonshi yayi kan Janaan data tsure saboda tsoro sai wuri wuri take da idanu cikin had'e rai sosai yace

"Ban hanaki shan wannan abin ba Ba

by? dan kinga ina lallab'aki shiyasa kike bijirewa maganata ko to bari in dawo miki Abdallah na na asali inci k'aniyarki tunda yanzu bakijin magana".

A marairaice cikeda shagwab'a tace

"Dan ALLAH Yah Abdallah kayi hak'uri please bazan k'ara ba ka....."

Kima k'ara kiga yadda zanyi dake a gidan nan duk abincin gidan nan kirasa abinda zaki dinga ci sai kwaki saboda kijamin magana a wajen mutane ko". ya katse Janaan.

"Yah Abdallah bayin kaina bane fa kafi kowa sanin hakan". tace kamar zata saki kuka.

"

Nafi kowa sani kuwa tunda nina d'ura abina amma kibari ki juyemin abinda ke cikinki nayi alk'awarin aje miki buhu buhu yadda zakifi jin dad'in sha tunda shi kikeso".

Baki Janaan ta tura sosai jin abinda ya fad'a wato ita baya sonta kenan, dariya ta bashi

hakan yasa ya shiga darawa yana cije lips gamida kamota jikinshi ya rungumeta sosai yana shak'ar daddad'an k'amshin dake tashi a jikinta, itama lamo tayi tana shak'ar nashi turaren idanunta a rufe wani tsananin son mijinta na k'ara ratsata ada gani take b

a yadda za'ayi Yah Abdallah yasota har taji dad'in zama dashi sai gashi kuma alhmdulillah komai yazo mata cikin sauk'i batada matsalar komai dashi sai wanda ba'a rasaba wanda kuma zaman aure ya gaji hakan zo mu zauna zo mu sab'a tana fatan ta rayu da mijin

ta har k'arshen rayuwarta.

Daga nan kuma salon labarin yafara canzawa ya d'auketa cak suka nufi bedroom ganin suna shirin zubewa k'asa.

√^√^√^√^√^√•••••••



Rayuwa ta cigaba da tafiya da dad'i ba dad'i dama haka rayuwar ta gada watarana zuma wa

tarana mad'aci ayi kuka ayi dariya da haka har lokacin da kowa zai amsa kiran ubangiji subhanahu wa ta'alah ubangiji ALLAH yasa mudace yasa ranar mutuwar mu tazama ranar farin cikinmu ALLAH kasa mu cika da Imani yabamu sa'ar tafiya alfarmar sayyadil wujuud

sallallahu alaihi wa alihi wasallam (Amin ya Rahman).



Mrs Salees Mu'az

💝

3/5/22, 18:41 - Ummi Tandama

😇

: *WATA SOYAYYA*

💝

Page 32.

Paid book

*TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A 2022*.

© Oum Hanan

Tun kafin cikinta yafara girma ya kaita ta zi

yarci y'an uwa Yola suka fara zuwa suka sauka gidan Momy Maryam taga y'an uwa ta zazzagaya sosai kwanansu biyar anan Yolan suka wuce Kaduna gidansu Janaan.

Tunda sukaje Abdallah yake gumawa Jauhar takaici iri iri rashin kunya kala kala kuma tasan da biy

u yake hakan,su Mama kuwa sai sallamawa zaman falon sukayi Hajiya Yaya ce ma wani lokacin takan ce baza'a takura mata da zaman bedroom ba ta fito falon ba jimawa kuwa zata gudu tana faman mita Abdallah na mata dariya. Gaba d'aya Jauhar ta k'osa sutafi kafi

n

zuciyarta ta buga duk da dai bata gaji da ganin y'ar uwar tata ba amma mijinta yaja mata, ita kanta Janaan d'in yana matuk'ar bata kunya saidai ba yadda ya iya dashi a haka suka gama kwanakin su suka tafi.

Shak'uwa ce mara misaltuwa ta k'ara shiga tsa

kanin Madugu da Janaan duk wanda ya gansu dole yayi mamaki saboda sanin halin shi sai gashi kuma yabawa marar d'a kunya irinsu Aunt jamila da sauran y'an team d'inta

😄

bani na fad'a ba

🥲

.

•••••••••••••



A haka Janaan ta cigaba da rainon cikin

ta wanda tun yana y'an watanni da basu wuce hud'u ba yayi girma sosai idan mutum yagani sai yace yayi wata biyar koma shida school d'inta kuwa tuni ta ajiyeta gefe saboda laulayin datake kullum batada cikakkiyar lafiya hakan yasa dole ta hak'ura duk da yad

da takeson karatunta sosai. Sosai Abdallah yake bata kulawa taban mamaki wanda kowa yagani sai abin ya d'aure masa kai wai Abdallah ne yake yiwa mace haka?.

Ganin yadda take matuk'ar shan wahala yasa Ammi da Ayyah suka nemi Abdallah ya maidata gaban

su lokacin cikinta yanada wata takwas amma idan mutum yagani zai iya rantsewa ya shiga cikin na goma bama tara ba saboda yadda yayi mugun girma ga kumburi datake fama dashi, Nan fa Abdallah ya k'ek'ashe k'asa yace sam shi babu inda zaikai matarshi ko haihu

wa tayi ba inda zata saidai azo a zauna musu saida Ammi tayi masa jan ido sosai harma da Abbie wanda Ammi ta fad'a masa ya kuma ga dacewar Janaan d'in ta dawo gabansu, haka nan dai bawai da son ranshi ba ya maida ita da siyayyar kayan baby daya uban jidosu

kamar hauka.

Kwana d'aya biyu shima sai gashi wai yadawo gidan da zama bazai iya zama acan ba matarshi ba, haka yasa aka gyara masa side d'in daya bari ya zauna a ciki. Sosai su Ammi kejin dad'in irin d'imbin kulawar da Abdallah yake bawa Janaan duk da

dai harda rashin kunya yake had'awa saidai su kauda kai amma suna jin dad'in hakan sosai.

Yauma suna bedroom d'in data sauka bayan zuwanta kusa dana Ammi, yana zaune a tsakiyar gadon ya jingina bayanshi da pillow ya mik'e k'afafunshi dogon wando ne a

jikinshi plain ruwan zuma da farar riga mai gajeren hannu, Janaan na kwance kanta akan cinyarshi hannunta cikin nashi hannun yana mammatsa mata su saboda kumburin da sukayi suma hatta fuskarta ta d'add'aga matuk'a gaya yake tausayawa matar tashi ko ba'a fa

d'awa mutum ba yasan tanajin jiki ya matsu yaga ta haifar masa da abinda ke cikin nan nata kota huta da wannan wahalar.

"Yayanah". yaji muryar Janaan ta ambaci sunanshi cikin sanyin muryarta wanda a yanzu ta k'ara yin sanyi sosai saboda wahalar ciki.



"Na'am MAI SANYIN". yace shima a hankali bayan ya sunkuyo da kanshi saitin kunnenta, murmushi tayi jin sabon sunan daya mak'ala mata kuma yau dama kullum da kalar sunan dayake fad'a mata wani ma idan ya fad'a sai abin yaba mutum dariya.

Bata bud'e idan

unta da suke a lumshe ba tace

"Idan na haihu wani suna za'a sawa babyn?".

"Kibari ALLAH ya saukeki lafiya mana Baby saurin me kike uhmm?".

"Nidai kawai inaso inji ne Yah Modibbo". tace cikin muryar shagwab'a, murmushi yayi yace

"Idan namiji ne z

an maida sunana ne idan kuma baby girl ce zataci sunanki ok?".

Da mamaki tace

"Sunan mu fa Yayanah?".

"Basuyi bane?". ya maida mata da tambaya maimakon amsa yana d'age kafad'a daga zaunen dayake.

"Nikam gaskiya dai.....bai bata damar k'arasa abinda

yayi niyyar fad'a ba ya sunkuyo tareda zura bakinshi cikin nata ya shiga bata zazzafar sumba daga nan kuma ya shiga ragewa kanshi zafi cikin dabara batare daya takurata ba dama a kusa yake an kwana biyu ba'a had'u ba

🙃

.



Tunda cikin Janaan ya

shiga watannin haihuwar shi su Ammi suke zuba ido amma shiru haka dai suka cigaba da jiran haihuwa da kuma addu'ar ALLAH ya sauketa lafiya Abdallah da kanshi yake kashe ayyukan gabanshi ya kaita asibiti ganin likita da kuma yin awo. Lokacin da akayi scann

ing aka tabbatarwa da Abdallah twins ne a cikin Janaan, tamkar zaiyi hauka saboda tsabar murna suna dawowa kuwa ya fesawa su Ammi labari suma sunyi murna sosai tareda fatan sauka lafiya.

√•√•√•√•√•√•√•√

A firgice Jauhar ta farka daga wan

i mummunar mafarkin datayi a daren ranar ganin y'ar uwarta cikin wani hali marar dad'i kai tsaye bazatace ga yanayin da Janaan d'in take ciki ba kawai dai ta ganta cikin wani hali mai wuyar fassara gaba d'aya sai jikinta yayi sanyi taji gabanta sai fad'uw

a yake addu'o'e ta k'ara yi ta k'ara komawa ta kwanta da k'yar barci ya d'auketa bayan dogon lokaci data d'auka idanunta biyu ta kasa komawa barcin.

Washegari kuwa tana idar da sallahr asubah ta dokawa Janaan kira a waya, ajiyar zuciya ta sauke lokacin

da taji Janaan d'in tayi picking kuma muryarta lafiya lau sai lokacin hankalinta ya kwanta sosai Janaan ta shiga tambayarta lafiya kuwa kira da asussuba haka? kawai cemata tayi ba komai kawai ta kirane dai taji lafiyar ta daga nan sukayi sallama.

Tun da

ga lokacin Jauhar taji gaba d'aya hankalinta ya koma kan y'ar uwarta burinta tasa ta a idanunta duk hankalinta yayi Kano dan haka tasamu Mama da maganar tanason zuwa Kano, Mama tayi mamaki k'warai ta tambayeta dalili tace kawai ita haka nan take so taje ta

ga Bloody d'inta, da farko Mama bata yardaba tace ta bari Janaan d'in ta haihu tunda ta kusa amma ta shiga yimata magiyar dan ALLAH ta taimaka ta barta tunda sun samu hutu a school da k'yar Mama ta barta tace zata fad'awa Daddy aji ta bakinshi.

Da dare

take fad'awa Daddy zancen tafiyar da sukayi da Jauhar baija da nisa ba yace ALLAH ya kiyaye hanya ayiwa Ja'afar magana ya kaita.

Kwana biyu da yin maganar Jauhar ta shirya inda driver ya tafi kaita saboda Ja'afar aiki yasha masa kai a office hakan yasa

bai samu kaita ba. Sai ganinta kawai sukayi katsam dan bata sanar da kowa zuwanta ba itama kuma Mama da sukayi waya da Ammi ta manta bata fad'a mata ba.

Rungume juna sukayi sosai lokacin data k'araso cikin tsananin murna da soyayyar y'an uwantaka dake

ratsa jininsu, ta tausayawa Janaan sosai ganin yadda takoma kamar ba itaba tamkar tayi mata kuka, nan suka had'u a bedroom d'in Janaan d'in har da Hassana da Hussaina sunata hira a haka Abdallah ya shigo ya samesu tun kafin ya shigo d'in k'amshin shi ya b

ayyana musu mai shigowar hakan yasa su Hassana duk suka mik'e tsaye suna

jiran ya shigo su fita Jauhar kam tana nan a inda take kusa da Janaan tasan shi dinne saboda yadda bugun zuciyarta ya canza lokaci d'aya gabanta sai wani fat fat yake tamkar zai fasa

k'irjinta ya fito waje batasan meyasa hakan ba kokuma dan ta dad'e bata ganshi bane oho murmushi kawai Janaan take saki tun kafin shigowar shi ALLAH sarki Yah Abdallah gaskiya wanda bai zauna dashi ba bazai tab'a fuskantar shiba yanada dad'in zama ga wanda

bai saniba kuma yanada hawa kai da addaba itadai a yanzu batada kamar shi kulawar dayake bata ko auren soyayya sukayi sai haka ba abinda zatace sai alhmdulillah ubangiji ya karb'i addu'arta yabata zaman lafiya da nutsuwa a gidan aurenta.

Yana shigowa

Hassana da Hussaina suka fita daga bedroom d'in kansu a k'asa sudai duk da ake cewa Yah Abdallah ya canza har yanzu basu tabbatar ba dan zagin dayake musu bai dainaba yadai d'an ragu ba kamar da ba. Farar rigace a jikinshi long sleeve mara nauyi sai wandon

jeans blue black saita gadon tashi wato P.cap white color dake kanshi idanunshi kyarr akan Jauhar da tun shigowarshi ta had'e rai sosai itama idanunta cikin nashi kowa da abinda yake sak'awa cikin ranshi yayin da kowa ya kasa fassara irin kallon da d'an u

wanshi ke jifanshi dashi, sai taga duk ya canza mata kamar bashi ba yayi y'ar k'iba abinshi sab'anin da dayake sai uban tsayin kawai kallo d'aya zakayi masa kasan yana cikin tarin nutsuwa da kwanciyar hankali gashi ya k'ara fari akan wanda yake dashi da ma

sha ALLAH musamman da bak'i sid'ik d'in sajen daya k'ara k'awata fuskar tashi da gemunshi na gayu wanda suke shan uban gyara da mayuka masu matuk'ar kyau da tsada. Ido ta runtse gam zuciyarta na wani irin rawa lokaci d'aya ta saki y'ar k'aramar ajiyar zuci

ya dako Janaan dake kusa da ita bata jitaba.

A hankali ya shiga takawa inda suke zaune bayan ya soke hannayenshi cikin aljihun wandonshi, yana takowa ne yayin da bugun zuciyarta ke k'ara tsananta tayi ta maza ne kawai ta basar ta juyar da kanta gefe tan

a girgiza k'afafunta data d'ora d'aya kan d'aya, k'erere yayi musu akai yayi musu tsaye idanunshi akan Jauhar data juyar dakai wani side d'in.

Rai a had'e ba alamun wasa a muryar shi cikin harshen fulatanci yace

"Ke tashi ki fita zanyi sirri da matat

a".

Da sauri ta juyo ta kalleshi tanajin tamkar ta tashi ta daddalla masa mari saboda mugun haushin daya bata.

"Bazaki fita bane? ko bakya jin yaren danayi magana dashi?". yace still dai da fillacin yana zaro hannayenshi dake aljihu ya kama k'ugunshi d

a duka hannayenshi, a fusace Jauhar ta mik'e tsaye sama da k'asa ta kalleshi itama cikin fulatanci tace

"Dan ALLAH idan ka tashi ka cinyeta gaba d'aya k'arewar sirri mtwss". taja k'aramin tsaki ta nufi k'ofar fita bedroom d'in.

"Cinyewa ta nawa kuma

? ki zuba ido kiyi kallo had'iyeta zan dinga yi ina dawo da ita tsabar yadda nake sonta kwarkwar d'in yarinya kawai". Tsaye tayi a bakin k'ofar bayan ta janyo k'ofar da k'arfi duk yadda taso hana hawayen idanunta zuba saida suka zubo zafi zuciyarta keyi ma

ta tarin tambayoyi ne cike fal cikin ranta amma batada wanda zai amsa mata su, jin takun tafiya kamar an nufo wajen tasan baya wuce Ammi ko Ayyah.

M&S

💝

3/7/22, 21:16 - Ummi Tandama

😇

: *WATA SOYAYYA*

💝

Page 33.

Paid book.

*TOP 10 TAKUN HASKE BA

TCH A 2022*

© Oum Hanan.

Da sauri tasa hannu ta goggoge idanunta sannan tabar wajen cikin sassarfa ta nufi bedroom d'insu Hassana.

"Yah Modibbo wai sai yaushe ne zaku daina y'ar tsama da Bloody dan ALLAH?". Janaan tace tana kallonshi.

"Ranar

datayi hankali". yabata amsa kai tsaye yana zama kusa da ita.

"Da da yanzu fa ba d'aya bane Yah Modibbo yanzun surukar kace fa".

"Idan ban bige miki baki ba kice......kukan shagwab'a tasa masa wanda yasa ya kasa cigaba da maganar ya janyota jikinshi

yana fad'in tayi masa shiru zai gaisa da baby's d'inshi.

Tunda Jauhar ta fahimci abin na Madugu wulak'anci ne saita daina shiga bedroom d'in Janaan dan bayan wannan ya k'ara zuwa ya sameta suna zaune suna hira da Janaan lokacin su su Hassana suna school

ranar ma kam baiyi mata magana ba sai gani tayi ya rungume Janaan d'in yasa bakinshi cikin nata ita kanta Janaan d'in abin yazo mata unexpected, abin yayi matuk'ar k'ona mata rai tashi tayi ta fita tanata faman masifa harda cemasa jarababbe da cikin ma ba

zai bar mata y'ar uwa ta huta ba ( Hajiya Jauhar

🤣

).

Tunda daga lokacin ta janye shiga bedroom d'in saidai su had'u a falo dasu Ammi ayi hirar cikin jama'a tasan dai duk iskancin shi da rashin kunyarshi bazaiyi a gaban su Ammi ba amma abinda ya bata m

ugun mamaki rannan a gaban Ayyah yayi hugging d'in Janaan ya k'ara mata da peck a goshinta Ayyah sai kauda kai tayi k'arshe kuma ta tashi ta bar falon tun daga nan ta sallamawa Madugu da aikinshi lallai a hakane har ake cewa yayi hankali? indai hakane kam

da sauranshi ALLAH ya shiryashi.

Friday morning.

Tun bayan sallahr asubah Janaan takejin jikinta ba daidai ba ga ciwon baya da mara kad'an kad'an dake damunta idan suka murd'a mata saikuma su saki. Abdallah daya shigo lokacin dazai fita office ya

ga yanayinta duk

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login