Showing 27001 words to 30000 words out of 176422 words

Chapter 10 - YAR BANGAR SIYASA COMPLETE

ya amsa da a

meen yana mata sallama har bakin kofa ta rakoshi tana sanya masa albarka

Suhairat dake la'be bakin kofa ta silale 'kasan daki ta fashe da kuka "Shikkenan na mutu ni suhairat shikkenan karyata ta kare zaiyi aure ina zaune duk na kori masu sona saboda

dashi bai san inayi ba na shiga uku na lalace." Kuka take sosai Salimat na bata hakuri Hajjah ta shigo dakin.

Tace"Ke suhairat lafiya kike wannan kukan." Rungumeta tayi tana shashsheka take fada mata tsayin shekarun da tayi tana jiran Ahamdu amma yanzu

yazo yace zai auri wata.

Hajjah tace"Inda Ahamdu zai aureki da tuni ya aure ki Suhairat ni da kaina nace ki hakura dashi ki zabi miji cikin manema auranki ki aura kikaji ni ba zanyi masa tilas ba, saboda yaron ya daukeni a matsayin uwa yana min biyayya

komai nake so yanayi min ban haihu ba amma an haifar min addua ce tsakanina dashi ni dai shawarar da zan baki shine ki hakura dashi ki fito da miji cikin ma nema auranki ki aura magana ta wuce."

Suhairat ta mike daga jin hajjah tana kuka mayafinta ta fi

ga ta dauki handbang dinta ta fice....Salimat ce kawai tayi wa Hajjah sallama tana bata hakuri kan abunda Suhairat din tayi mata.....Tana fitowa harabar gidan taga Suhairat ta figi mota a guje ta fice daga gidan....Girgiza kai kurrum tayi ta sanya direba y

a dauketa domin kaita gida.....' Yan asalin unguwar galadanci ne.

****

Wasila ta tashi da wata iriyar kasala da mutuwar jiki, dan ta jima ma a daki kafin ta fito cikin kayatacciyar kwalliya gold kamar yayi magana a jikinta har yatsun 'kafafunta gold ne

tana sanye da legos less dan gasken tayi daurin ture kaga tsiya gashinta ta daure shi da katon ribbon ya kwanta a kafadarta idan ka kalleta sai ka dauka irin masu shegen karatun nan ce saboda yanda takeyin mu'amula cikin jan aji da isa......Uwani da Rash

ida sai girki suke su sauke su dora suci wannan su sha wannan duniya ta samu.

Tunda ta kunna wayarta sa'konni ke shigo mafi yawanci daga abokanan harkarta ne maza sunfi yawa babu wanda ta duba a cikin messages din wayar dai kawai take latsawa tana ya mu

tse fuska, ita kadai tasan me takeji a jikinta har yanzu gabanta bai daina faduwa ba mutukar zata tuna da mafarkinta na jiya.....Kiran As ne ya shigo wayar ta sai da ta kusa katsewa sannan ta dauka suka gaisa yace anya zaki fito yau kuwa?

Ya mutsa fuska

tayi tace"Yau dai zan huta a gida Gaskiya sai dai gobe." Yace."To babu laifi ko nazo na taya ki hira ne."? a ya tsine tace"Ina da abokanan hira ka huta kawai." Mara zuciya sai ya sake cewa "Okey anjima zan shigo zamuje musha iska." Tace."Ba damuwa sai ka

shigo amma dai ka bari sai bayan sallahar isha'i." Yace."Haka za'ayi gimbiya." Hira suka dan ta'ba tayi masa sallama da fad'in zata kwanta bacci ba dan yaso ba ya hakura. Kashe wayar tayi tana tsaki....Camas! tayi sallama ta shigo palon....Taci uwar kwalli

ya da material mai uban tsada wani shegen dinki akayi mata mai fitar da tsaraici gashi bata sa mayafin kirki ba Camas an samu duniya har mota ce da ita sannan itama Alhaji Ma'aruf yayi mata alkawarin mallaka mata gida cikin gidajensa da yake ginawa.....Tac

e."Kawata ya yau dai duk na ganki babu kuzari ne na jima da zuwa government house ina jiran zuwanki sai yanzu As yace yau ba zaki fito ba sai gobe."

"Camas yau hutawa zanyi wallahi na gaji kullum kana cikin maza shegu suyi ta kare maka kallo wani ma ya

na sane zai zo ya gogi jikinka wai bai sani ba, na kusa daina wannan harkar tunda bukatata ta biya." Camas tace"Wallahi karki soma shin me na kasa yace ballanta ya bawa na sama me kika mallaka me kika ajiye a account dinki karfa ki manta yanzu lokacin da z

aki sake zage damtse ki tatsi abunda kika tatsa wanda ko bayan mulki ya bar hannunsu kin samu kasonki me tsoka ai wallahi ni yanzu na fara har sai naga abunda ya turewa buzu nadi." Ajiyar zuciya ta saki a hankali tace" Duk da haka dai zan dinga daga kafa

ba kullum zan dunga zuwa government house din ba, kina sane dai da kallon da jama'ar gari ke mana ko wasu fa karuwau suke daukarmu, na tsani ace min karuwa wallahi." Camas! tace" Sun dade basu kirani da karuwa ba abunda ya damesu ne idan kace zaka daka ta

mutane sai su cuce ka.'' Shiru kawai tayi tana girgixa kai ta tsani a kirata da karuwa gwara Camas idan sun kirata da karuwa babu laifi tunda tana ta'bawa amma ita ba taji ba bata gani ba ana kiranta da kalmar da tafi tsana a rayuwarta.

****

*RANAR JUM

A'A*

Su shida ne kacal a cikin motar Ahamdu Kawu Almu da abokinshi sai Khalifa da mahaifinshi Alhaji Iliyasu sai Garba dake gaban mota yana draving, kasancewar shine yasan gidan ya sanya zai jagoronce su.....Ahamdu da Khalifa suna sanye da kaya iri daya

farar shadda ce kal dinki babbae riga da yar ciki hula iri daya agogo iri takalamsu iri daya hattata da links dinsu iri daya ne sosai idan ba fada akayi ba ba zaka bambance waye angon ba a cikinsu.

Can bangaran su Malam mai allo kuwa sun shirya tsaf da

n tuntuni malam ya shaidawa limamin dake sallahar juma'a a babban massalacin dake garin cewar bayan an idar da sallah akwai daurin auren da za'a gabatar.......To lokacin da suka sauka garin ana ta shirye shiryen tafiya massalaci dan

haka a gurguje suka dau

ra alwala suka bi ayarin mutane ya zuwa masjid d'in.

Bayan liman ya gabatar da hud'uba kamar yanda addini ya tanada sai aka tayar da sallah........An idar da Allah anyi addua kana kuma aka shiga daurin aure.............Ana shafa fatiha Garba da Khalifa

suka soma rabon alawa da goro gami da dabino cikin bakar leda za'a bawa mutum goro da alawa daurin aure yayi albarka jama'a sai addua suke gami da fatan xaman lafiya ga amarya da ango.

_Muje Zuwa_

*BINTA UMAR ABBALE*

*'YAR BANGAR SIYASA!!*



🌺

romantic love story

🌺

*NA:*

*BINTA UMAR ABBALE

🍒

*

*

🌍

Manazarta Writes asso*

_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_

~~~~~~~~

*NA KUDI NE.......!*

_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudi

n.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan num

bars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_

*Free Pege18*

Su Kawu Almu suka rufawa Ahamdu baya zuwa gidan Malam mai allo dake cike taf da dangi, katuwar tabarmar dake shimfide a tsakar gidan suka zazzauna aka shiga gaishe gaishe 'yan uwa

sai tambaya sukeyo waye angon ne tsakanin Ahamdu da Khalifa.....Ahmadu yayi kasa da kanshi a lokacin sai ya tsinci kanshi da jin kunya duk da a zuciyarsa auran yayi shine da wata siga ta daban amma sai yaji kunyar mutanan mussaman malam mai allo dake ta ka

i kawo yana hidima da mutane kana ganinshi kasan yana cike da farin ciki....Khalifa ne ya dinga nuna shi yana fad'in"Gashi nan wannan ne angon bani ba.'' Tsoffin ciki suka soma yi masa d'an biki suna tsokanarshi da fad'in ya tsinci dami akala tunda ya samu

nasarar auran Wasila saboda haka ya riketa da kyau dan ba karamar mace bace." Shi dai jinsu kawai yake yi yanayin yanda suke mu'amular su ya bashi sha'awa mutuka kuma ya lura suna masifar son su Wasilar halinsu kawai suke gudu, magana cikin magana suke ma

sa hannunka mai sanda kan yarinyar kan yayi hakuri da halinta da dai sauraransu, sai ya kara jin jikinsa yayi sanyi da al'amarin auran yanzu kuma ya soma da ya sani tunda shi har cikin zuciyarsa ba da manufa me kyau ya auri yarinyar ba amma kuma darajar iy

ayenta na nema ta sauya masa tunani.

Lafiyayyan towon shika da miyar taushe aka kawo musu miyar taji manshanu gefe guda kuma ga soyayyan naman zabi nan fal katuwar silba......Babu wanda yayi wasa a cikinsu duka suka zage suka ci abincin dan tsabarta da

kayatuwarsa tamkar a restaurant babu wata alama da zai nuna abincin karkara ne kwanika sabbi aka zubo musu dalili kenan da ya sanya suka saki jiki suka ci suka koshi suka kora ruwa mai sanyi irin na randa.

Bayan sun kammala sai suka shirya tafiya gida

,Malam mai allo ya ke'be da Ahamdu yana masa maganar kan ya za'ayi da tariyar Wasilar Yace." Ya bar komai a hannunshi.'' Malam mai allo yace."Nida nafi so yau yau yarinyar nan ta kasance a dakinta bana so mu shiga hurumin ubangiji ya kasance muna wasa da a

ure, tunda an daura auranan to ta tare a dakinta barin ta haka sasakai zai janyo matsala babba tunda dai ita bata san halin da ake ciki ba.'' Yace."Tabbas maganar haka take malam babu damuwa insha Allah yau zata tare a dakinta kamar yanda ka bukata din." M

alam yace."To bari in baka sadakin a hannuka ka mika mata da kanka tunda dai mu ba ganinta Zamuyi ba." Yace."babu damuwa Malam." ya ciro dubu biyar din ya mika masa ya sanya hannu biyu ya kar'ba, kana ya shiga yi masa godiya sukayi sallama cikin mutunci d

a mutuntawa.....Har bakin mota suka rakosu sai da motarsu ta 'bacewa ganinsu sannan suka juya cike da farin ciki sun auran da Wasila saura Rashida zuciyarsu wasai mussaman malam mai allo yana fatan d'orewar zaman lafiya ga Ahamdu da Wasila.

Cikin mota

tunani kawai yake yi kan al'amarin duk ya rasa wane matsayi zai aje wannan auran nashi zuciyarsa na kawo masa shawarwari iri iri tabbas ko A lahira wani nacin albarkacin wani babu shakka yarinyar taci albakarcin dattijo malam mai allo a gurinsa, da ya dau

ki mummunar aniya a kanta albarkacin mutumin ya rage kashi tamanin daga cikin abunda ya tanadar mata amma dai duk da haka zai ba zai kyaleta ba sai ta gane bata da wayo......Haka suka isa gida tunani duk ya addabe shi yanzu ya za'ayi ma ya tunkari inda ya

rinyar nan take dame zai fara ne." ? Khalifa yace."Naga ka shiga tunani da yawa ka bari muje gida mu dan huta tunani ya dawo tukkuna nasan abunda ke damunka a yanzu amma aka bi komai a hankali mai sauki ne." Ajiyar zuciya ya sauke ya dan gyara zamanshi y

a sake mai da idonsa ya rufe ba tare da yace komai ba.

Cikin wata lafiyayyiyar lifaya ta fito Tana baza kamshi turarruka masu tsada da sanyin kamshi, Tayi ado da gold 'kirar dubai masu jajayen stones a jiki shi kanshi gyaran gashin da tayi wa kanta ab

un kallo ne tamkar wata balarabiya haka ta zama babu shakka kudi na iya canza mutum nan take Wasila ya zanzu dai da zata shiga cikin labarawan Itopia sai ta saje dasu saboda yanda fatarta ta goge ta 'kara fitar da kalarta chocolate color dama can haka kal

ar fatarta take Rashida ce fara itace ta d'ebo haske babansu Uwani kuwa ba za'a kirata fara ba kuma ba za'a kirata baka ba kusan kalar fatarsu daya da Wasilan amma dai yanzu ta Wasilar tafi kyau da gogewa, takalmi mai tsayi ta sanya kasancewar ba ta fiye t

sayi sosai tana tsaka tsaki dai! Hannunta rike da pose da key na motar ta take takawa sannu a hankali.....Camas dake zaune na latsa waya ta kalleta "Wow! Kinga yanda kikayi kyau kawata, gaskiya lifayar nan ta miki kyau wallahi ke kin jima bakiyi kyau irin

na yau ba tamkar wata amarya lalle

ne kawai babu a hannunki da kafafunki.'' Murumsi tayi tace" Haka kawai yau nace bari nayi shigar bare bari ashe nayi kyau."? Camas! ta kwalawa Rashida kira ta fito daga kicin....Ganin Wasila ya sanya ta rude! "Aunty Wasi

la kece dan Allah nima ina son lifayar nan ki siyamin wallahi kinyi kyau! sai kallonta takeyi tana dariya Camas tace " Wai tambaya takeyi tayi kyau shine na kira ki ki fada mata." Rashida ta hau kod'ata "Wallahi aunty Wasila ko makaho ne yazo kusa dake ya

tsaya sai ya kiyayi kansa babu wanda zaice kin hada jinsi da bahaushen mutum kamar wata balarabiya." Ganin yanda suke sambatu ya sanya ta dinga musu dariya...Uwani ma ta fito daga daki ta dinga nata shirma da zasu fita ta dinga yiwa 'yar tata kirari sai ka

ce wata maro'kiya ita Wasila ma dariya suka bata tace"aikuwa dai tunda shigar lifaya nayi min kyau zan dawo yin irinta....

Suna shiga motar kiran As ya shigo wayarta ta dauki wayar tana dan ya mutsa fuskarta.....A nutse tayi sallama da sauri ya amsa

yana fad'in "Gani a bakin gate din gidanki ki fito kawai muje mu dawo dan ma dai nayi alkawari ne da sai nace mu bari sai gobe ma futa yanzu aka kirani a waya karfe goma dai-dai muna da metting da shugaban 'kasa kin san tun safe ya shigo gari yanzu haka s

una tare da mai girma governor."

Tace."To mai zai hana mu bari sai gobe." Da sauri yace." Ai ni kuma ba zan fuskanci komai ba gurin metting din nan mutukar banyi tozali da kyakkyawar fuskar nan taki ba." Murmushi tayi ta kashe wayar ta kalli camas tace

"Ga d'an anace nan ya iso kawai ina zama na wai na shirya muje shan iska komai abunsa dole ya hakura dani wallahi wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa

Camas tace"Tunda dai yaki hakura ba sai kiyi kwance kwance ki kwashi rabonki ba." Ke dai kawai fito mu

je dare nayi kudi kam ai kamar mahaukaci haka yake samun a account. " Camas taji inama itace dan a zahiri As yafi Alhaji Ma'aruf sakin hannu shiyasa taso ace As din ne ke mu'amula da ita tasan da tuni ta wuce gurin........Kamshi turaranta shine ya buwaye s

hi, yana draving yana kallonta idanunsa sun kada sunyi jawur babu shakka yau Wasila ta kaishi makura ga bukatuwa da ita yana ganin koda bai shiga wannan ramin ba a'kalla dai ta bashi dama ya d'an rage zafi a jikinta....Da kyar suka isa 'katon gurin hutawar

wanda sai wanda ya amsa sunansa ke zuwa gurin......gurin tamkar rana ko ina haske tar tar jama'a nata shigowa da motacinsu da yawa daga ciki tare suke da mata wasu karuwansu wasu matayen su kowa harkar gabanshi yake.........As yayi kwance a gabanta yana

lumshe mata shegun idanunsa da suke cike taf da sha'awarta duk sun kankace saboda jaraba, ganin yana matsowa jikinta ne yasa tayi saurin matsawa tana 'bata fuska.....Yace."Yana da kyau yau daya ki bani dama ko yaya ne na ra'bi jikinki babu shakka zuciyata

na azabtuwa da so da kaunarki ki bari na rungume ki ko zanji dadi a jikina"

Ranta a bace ta kalleshi "Haba As wai yaushe ne zaka daina yi min irin wannan maganar? na sha fada maka ni ba 'yar iska bace amma ka kasa fahimta ko dan kana ganin Camas! kawa

ta ce shine nima kake zargin halinmu daya da ita, Wallahi da zanyi karuwanci da tuni nayi amma ni ba layina bane kaje ka nemi karuwa ta debe maka kewa bani ba, idan kudin da kake turo min da wannan niyyar ne to dan Allah daga yau kar ka sake kuma tunda ka

kasa daukata a matsayin abokiyarka to ka goge numbarta dake wayarka

bana bukatar wata mu'amula ta sake shiga tsakanina da kai. Mikewa yayi zaune yana marairace fuska yana so ya kama hannayenta ta fuzge da karfi ta mike tsaye da sauri jikinta na rawa...Cama

s na can tare da wani alaji suna zance ta iskesu rai a 'bace tace" Ni zan wuce gida Kya biyo bayana." Mutumin yace."A bari nazo na kaiku mana." Ko sauraransa ba tayi ba tayi hanyar futa....Ita ko Camas! ganin alhajin nada kumbar susa a tare dashi sai tace

"Rabu da ita Alhajina idan da wata bukata da kake nema a gurina yi min magana kawai kar kaji shakka." Ya shafa fuska yana lumshe mata ido yace."Muje mu kama daki zuwa gobe da safe sai na sallame ki." Ba tare da wata doguwar jayayya ba tabi bayanshi.

As

yabi bayan Wasila yana nema neman duniya bai ganta ba guri ne babba ga jama'a na shiga suna fita ya fita bakin titi ya jima a tsaye yana waige waige bai ganta ba, haka ya koma ciki domin daukar motarshi anan kira ya shigo wayarshi kan lokaci ya kusa da za

su zauna metting dole ya nufi government house din ba dan ransa yaso ba yaso ko yaya ne ya rage zafi da Wasila amma ya dauki alkawarin komai tsantsaninta sai ya rusa shirinta.

Tana ganin futar motarsa ta fito daga inda ta 'buya babu shakka As so yake y

a yaudareta ya rabata da budurcinta wanda da ta jima tana tattalinsa, tabbas zata janye jikinta dashi da lamuransa tunda ta lura shi baya abu dan Allah.

Koda ta fito titin tsif! babu abun hawa na haya dama kuma ba kasafai a dai-dai ta sahu ke shigowa g

urin ba saboda babban titi ne na masu hannu da shuni yawanci motocin gida sunfi karakaina a kan titin.....Tsoro yasa ta kasa tsaida motar kowa sai ta kama hanya ta dingi tafiya ga cokalelen takalmi a kafafunta.

Tana daf da futa babban titi motar ta f

ito daga wani babban layi mai dauke da dogwayen gina gine, dole tasa ta ratse a gefe domin ta bawa mai motar hanya, haushi da takaici ya turnuke ta ganin yanda mai motar ke dallare mata fuska da hasken fitilar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login