Showing 42001 words to 45000 words out of 176422 words
malam mai allo ya bashi aurena da sadaki dubu biyar, Kiyi kokarin ki samo min mafita Camas! kaina ina cik
in masifa_ Tana gama rubuta test din ta tura mata ta goge numbar da test din dan kar ya gani......Ta kira Rashida itama tana ringing bata dauka ba da sauri ta shiga kiran wayar Uwani is swich Up! Tsaki taja tayi shuru can ta yanke shawara Numbar As ta sany
a a wayar ta soma kiran shi aikuwa kamar jira yake yi ya daga wayar, ta sauke ajiyar zuciya da sauri ta nufi dakin tana fad'in"As 'Yar gaske ce! Daga daya bangaran As yace."My love ina kika shiga munanan hankalinmu a tashe mahaifiyarki da kanwarki sun shig
a damuwa yanzu haka ma duk muna tare dasu da Camas kawarki.
Kuka ta fashe masa dashi tace"As Ina gidan Ahamdu Musa a halin yanzu.......Tiryan tiryan! ta shiga warware masa abunda ke da akwai! As ya shiga tsananin tashin hankali da bakin kishi Ahamdu Mus
a ne yayi masa wannan wulakancin? ya za'ayi ya jima yana rainon abu ace lokaci guda wani yazo ya lalata masa shiri!! Yace." Wallahi karya yake mu zaiyi wa wannan wulakancin wato ta in da ya bullo kenan to ki kwantar da hankali kuma ki tsaya kai da fata kan
a'kidar ki duk rintsi kar ki sauka daga ra'ayin ki ni nasan saboda wata manufa tashi ya sanya ya aure ki ba wai dan sha'awa ko wani abu makamancin haka ba, domin tuntunin nasan wannan mutumin bashi da lafiya tamkar mata maza yake babu wani abu da zai iya
a kanki, duk da haka dai ki kiyaye zamu dauki kwakkwaran mataki a kansa, sai ya sake ki komai abunsa wato ya gano kina da muhimanci a tafiyarmu shine zai dauke mana ke to daga nan government house zan nufa domin mu san abinyi."
A hankali tace"Nima zarg
in da nake yi kenan ya aureni domin ya rusa tafiyarku ganin ina da muhimanci a tare daku shiyasa ya 'bullo ta wannan hanyar As kuyi da gaske na lura da gaske yake dan Duk ya tara ma'aikatan gidansa a aikana yace su sanya idonsu a kaina gidanshi tamkar kurk
uku yake ko ina a rufe babu ta inda zan taimaki kaina." Jin wannan maganar tasa As ya sake zabura! Yace."Aikuwa duk yanda zamuyi ki fito daga cikin gidanan zamuyi kar ki damu."
"Shikkenan As ina saurare dan Allah ku taim.......! maganar ta katse lokacin d
a ta ganshi a gabanta, bakinta ne ya soma kyarma!! " Ra....shi..d ki cewa...U....! Hannu ya mika mata alamun ta bashi wayar.....Dai-dai da lokacin da As yake cewa"My love kina ji na ko? ki kwantar da hankali ki saki jikinsa dashi ki nuna masa komai ba kom
ai bane ta kanki zamu shirya plan dinmu a kansa ai ya janyowa kansa tabbas ajalinsa na kusa."
Ahamadu najin muryar As din tar! dake saboda rashin dubara hands free ta bude ko kuma dai ta manta ne oho!!! Jajayen idonsa ya ware mata Hannu ya sake mika mata
a karo na biyu!!! Ta mika masa wayar jikinta sanyi kalau....Wayar ya kara a kunnansa, Har yanzu As nata surutu da fad'in"My love kina jina kuwa kinyi shiru, karki wani damu da wannan abun zamu dauki 'kwakkwaran mataki a kansa." Kashe wayar yayi ya tsira m
ata rikirkitattun idanunsa....."Waye kika ce min zaki kira."!? Yafada yana kallonta cike da tuhuma....."Rashida c.....! Kafin ta karasa ya bata wani lafiyayyan mari! Ihu! ta kurma! ta haye kan bed ta tsaya hannunta dafe da kuncinta......A zabure! yace."Ni
zaki rainawa hankali ko? Waye wannan da kika kira har yake kiran ki da masoyiyarsa."!.....Cike da rashin gaskiya tace"Kanwata ce Rash.....Bed din ya haye! ta manne jikinta jikin bango tana kare fuskarta,Wuyanta ya dam'ka! da karfi ya shake mata magogwaro
yana mata kamshin mutuwa! Ta dinga 'kifta ido tana kakari idanunsa sun gwalalo sunyi jawur had'e da tara ruwa.....Lokacin duk wani tausayi da imani nasa babu so yake ya kashe ta, babu abunda idan ya tuna yake sake dugunzuma masa zuciya sai muryar gardin mu
tumin dake kiranta da Masoyiyarsa (My love) ba za'ayi haka dashi ba gwara kawai ya kasheta ya huta tun kafin ta tarwatsa masa zuciya.......Idanunta ne suka soma lumshewa jikinta ya soma shikawa luuuuuu! tayo jikinsa......Ya sake ta ta fadi kan bed din Ta s
uma! daukar ta yayi ya kai ta can bakin toilet ya ajiye ya bude firji ya dauko shegen ruwa mai sanyi kai tsaye ita ya nufa ya hau tuttula mata a fuska da jiki! Ta bude ido a zabure! tana a tishawa, cigaba yayi da zuba mata ruwan sanyin a jikinta, cikin r
ashin tausayi.......Saboda rashin kwarin jiki yasa ta koma ta kwanta jikinta yayi lakwas! sai makyarkyata takeyi tana jin saukar ruwan sanyin a jikinta amma ta kasa motsawa sai wasu irin hawaye ne masu zafi dake ziraro mata.....Sai da ya juye mata babban g
ora na ruwan swan kana ya jefe ta da goran ruwan ya sanya kai ya fice daga dakin ranshi ba'ki'kkirin.
Littafin nan na kudi ne! Idan kika futa da book din nan Ke da Allah! Ki ka karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap numbar
*07084653262
*
*BINTA UMAR ABBALE*[07/08, 11:49 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys
*25*
Ransa a 'bace ya fita ya iske Garba da Hadi a bakin mota suna jiranshi tun kafin ya karaso Garba ya bude masa mota ya shiga kana kallon yanayin yanda ya fito kasan babu wasa,
su kansu su Garban sun sha jinin jikinsu, sukan kwana biyu ba suga irin wannan fuskar shanun daga gurun ogan nasu ba, duk ranar da yayi irin wannan 'bata ran to babu shakka akwai abunda ya faru.....Da wuya kaga fushin Ahamdu dalili kenan da yasa idan anyi
masa abu a take yake ramawa saboda shi bashi da ri'ko ko 'kan'kani ! ko wane irin laifi zakayi masa ba zai gaba da kai amma wannan karon yarinyar nan ta kaishi bango dole ne ya nuna mata fushinsa mugun kishi ne dashi mussaman kan abunshi, idan yana da abu
yasan halalinsa ne baya so kowa ya ra'beshi, yayi masifar jin ciwon wannan kalma da As ke kiran yarinyar dashi (my love) idan ya tuna ji yake kamar ya zai shake dan bakin ciki!.........Maigadin gidan Khalifa ya bude gate din Hadi ya shiga da mota Khalifa
na tsaye harabar gidan dama already Ya kirashi a waya ya sanar dashi gashinan kan hanya, da kanshi ya karasa inda motar take ya bude masa kofa ya fito yanayin yanda ya ganshi a hargitse ya sanya yasha jinin jikinsa babu shakka akwai abunda ke faruwa.....Ta
re suka jera suna tafiya har zuwa cikin gidan...Ya samu kujerar dake daura da kofar fita ya zaune hade da cire hularsa, Khalifa ya tsaya kanshi tare da fad'in'' Akwai damuwa a tare da kai dama tunda naji kace ga nan nasha jinin jikina Allah yasa dai lafiy
a." Kafin yace wani abu Hafsa ta fito daga daki taci kwalliya cikin boyal mai ruwan zuma tace"Lallai ango ne a gidan da muna cewa zamu zo gashi har na shirya sai kawai ka kira waya kace kaganan." Ya dan saki fuska kadan yace."Zuwana ba zai hanaki zuwa ba t
unda kin san gidan sai kiyi tafiyarki." Tace"Ai amarya bata sanni ba mun bari dai sai ranar da kake gida sai muje Ga Zeey ma tazo yau kwananta biyu har ita muka shirya zamuje muga amarya sai kuma kayi mana bukulu."
Cikin 'kosawa yace."Wai ke dole sao d
a mijinki zakije gidan ne? nifa bana son gulma irin taku idan yawo ne ya kama watarana ma bakya tambayarsa kike tafiya to tunda kin samu abokiyar tafiya ba sai kuje ba, muma mafi jin dadin sakewa a gidan dan idan kinanan kin dinga zurga zurga kenan kina ha
nashi fahimtar magana." Dariya tasa tace" A'a dai gwara muje tare da mijina in yaso sai ka gabatar damu tare a gurinta amma yanzu idan munje nida zeey bamu san abunda zamu ce mata ba tunda ba saninmu tayi ba."
Khalifa yace."Ke da Zeey din ai gulma ce za
ta kaiku ba wani abu ba." Yar dariya tayi tace "Lallai Abban Afnan Wai gulma ni da nake so ma amaryar ta zama 'kawata sai kuma naje gulma." Yace."To meye na gayyato zeey dole sai anje da ita." Hafsa ta diririce! "Abban Afnan meye haka? Wallahi katari akayi
Zeey tazo kai kanka ka san Zeey bata san Governor yayi aure ba, sai da tazo taji labari to meye a ciki dan taje gidan ai matar mutum kabarinsa wani baya auran matar wani hakanan wani baya auran mijin wani." Ahamdu Yace."Kinji mijinki naso ya tona miki as
iri duk kin diririce to ai nagane komai." Rantsuwa ta soma yi tana so ta fahimtar dashi ba haka bane....Zeey ta fito daga dakinta, Siririyar mace ce fara mai fadin fuska da manya manyan ido da hanci mai fad'i sai bakinta mai dan tudu dai-dai misali bata da
wata cikakkiyar 'kira ta matantaka! amma kuma kallo daya kayi mata zaka gane cewar wayayyar macece mai tarin ilimi da kagani kuma tana da shekaru ko kusa ko alama ba zaka hada shekarunta dana Wasila ba
ta girme ta da kusan shekaru bakwai Wasila yanzu tan
a matakin shekaru 18 Yayin da Zeey ke da 26 Fuska a sake ta zauna kujerar dake fuskantarsa tana fadin"Ango ashe ana ganinku gaskiya Yallabai kayi wuyar gani ko a waya ba'a gaisawa.
Akwai kyakkyawar fahimtar juna a tsakaninsa da Zeey dan haka sai ya sak
i fuska kadan yana fad'in"Kece mai laifi ai da baki kirana a waya kin san al'amura da yawa sun sha kaina sai hakuri."
Murmushi tayi tana mamakin maganarshi wai fadi yake bata kiran wayarshi abunda a rana sai ta kira sau goma yaki dauka gajiya tayi da wu
lakanci ta kama kanta amma saboda ya kare kanshi yake kokarin dora mata laifi....Cikin bagarar da maganarsa tace"Kawai dai ka fad'i hakane domin kaji dadin bakin ka amma sau nawa zan kira wayarka kayi dauka gashi zahiri tana shiga babu amsa..
Kare kansa
ya hauyi tace"Governor kenan ashe kayi aure babu labari."? Ya dan sosa kanshi still da murmushi kadan! wata iriyar kunyar ta ce ta kamashi amma dake namijin gaske ne sai ya basar yace."Wallahi kuwa lokaci yayi kisan kuma dama haka lamarin aure yake idan
Allah ya kawo shi bagatatan sai ayi." Tace"Hakane to Ubangiji Allah ya sanya alkairi." Yace."Ameen nagode kwarai yanzu ki bani numbar ki sai nayi seving ko." Ta kalleshi da mamaki tace"Au! kace ma baka da no dina."
A wayance yace."Kwanaki na bawa Garb
a Wayar ya rage min numbars na jama'a sunyi yawa ashe ya had'a da taki dalili kenan da ya sanya duk sanda kika kira bakya samun amsa akan lokaci." Yafadi hakane dan ya kare kansa amma tun ranar da sukayi musayar numbar ita dashi yana futa ya goge numbarta
a ganinsa sam bai ga amfanin ajiye numbar mace a wayarsa ba.
Zeey kuwa ta yarda da maganarsa dan haka da sauri ta soma fad'o masa numbar yana sanyawa a wayarsa yayi serving tare da fadin'" Kinga ma dunga gaisawa lokaci zuwa lokaci." Zeey tace"Aikuwa da
i kam." Hafsa dake shirya abinci a dining tace"Governor yau fa mutuminka nayi ban sani ba ko zaka ci ko da yake amarya nasan kafin ka fito ta cika mata ciki da girkinta na amare.
Hararata yayi yace."Wai kina nufin Towo ko me."? Tasa dariya da fadin "d'a
yan ne." Yace."Alkubus."? Eh tafada tana murmushi....Yace."Ai ko d'awisu ta bani sai naci ko da cikina zai fashe." Duka suka kwashe masa da dariya Khalifa yace." Ai na sani ko ka koshi sai kaci wannan abu ni ban san me kake ji a cikinsa ba fulawa kayan bas
ir." Mikewa yayi yana fad'in"Ballanta na ma ban koshi ba dan har yanzu 'bacin rai ya hanani cin wani abincin kirki." Sai da ya fadi maganar kuma ya dawo yana da ya sani ganin dukaninsu sun sha jinin jikinsu.....To dai babu wanda ya sake tado da maganar su
ka zauna a danning Hasfa ta zubawa kowa nashi....Ahamdu ya riga kowa cinyewa Ya sake zuba wani da kanshi Hasfa sai tsokanarsa take da fadin"Allah yasa santi yasa ya manta hularsa.
Sai bayan sun kammala cin abincin ne ya kalli Hafsa a nutse yace."Wane gu
ri ake miki d'inkunanki."? Ta kalli Khalifa dake goge bakinsa da tissue! Khalifa yace."Kana so ayi wa amarya kenan."? Ina so dai in siya mata d'inkakku a gurin nasan ba za'a rasa ba.' Khalifa yace." Bari nayi wanka nazo muje Yakasai Gidan Murtala." Yace."K
ayi da sauri yamma tayi."
Khalifa ya mike ya nufi daki Hafsa tabi bayansa domin hada masa ruwan wanka.....Ahamdu da Zeey suka shiga hira abunda ya shafi harkokin Siyasa da yanda talakawa me faman shan wuya a wannan gomnantin.
Khalifa ne yake draving s
hi kuma yana zaune a gefansa suna hira Khalifa yace."Yanayin yanda ka shigo dazu ya sanya hankalina ya tashi to amma ganin ka sake kana hira dasu Hafsa yasa hankalina ya kwanta da har nayi tunanin ko kai da mutanan ne."
Tsaki yaja Yace.'' Khalifa nayi a
bu yazo yana damuna kwata kwata yanzu na dawo ina dana sani da auran wannan yarinyar da nayi tsakanin jiya da yau ta zame min masifa da kyar nayi bacci n dare da sassafe muka tashi da masifa abincin kirki ta hanani naci.....Babban abunda ya 'bata min rai d
a ita shine na bata waya ta ta kira gidansu, ta kira min wani shege wai ni zata rainawa hankali naji muryar namiji take cewa dani kanwarta ce a take na sumar da ita kasan dai halina in raina ya 'baci."!
Khalifa yace."Subahanallahi! gaskiya Wasila bata
kyauta ba! Magana da wani namiji bayan tana da auren wani a kanta......"Za tayi abinda yafi haka ma tunda jahila ce shiyasa na tsaurara matakan tsaro a kanta." Khalifa yace."Kaima matakin da ka dauka yayi tsauri gaskiya ya kamata ka zaunar da ita ka fada m
ata yanda al'amura suka kasance a tsakaninku nasan halinka da isa da jin kai! Dole ta shiga rudani da tashin hankali tunda katsaham! taji labarin auran kome zata iya yi a wannan lokacin."
"Khalifa yarinyar fa babu irin rarrashin da banyi mata ba ta'kiji
saboda tsabar rashin mutunci dazu ni tayiwa Allah ya isa."! Khalifa yace."A kan me? Shiru yayi nauyin fada masa abunda yasa yake....Yace." Dole ne fa kayi hakuri da duk abunda za tayi maka gaskiyar magana kenan kuma kai kanka kasan duk yawancin abokananta
maza ne abokan hurd'arta do ka fuskanci wannan matsalar."
"Khalifa kasan Allah kasan Annabi Ba zan lamunci wannan iskanci ba, Zan iya raunatata nayi mata illah mai muni mutukar naga da aurena a kanta tana mu'amula da wani namijin a waje, shine dalilin
da ya sanya ma duka na kwace wayoyinta na cire sim car din ciki na karairaya su....Domin nasan tilas mutsiyatan nan ba zasu rabu da ita ba tunda sun san tana musu amfani, Sam kar kayi tunanin ko sonta nakeyi kawai ina kishin aure na ne banda haka babu abu
nda ya shafeni da duk wata rayuwa da zata jefa kanta a ciki.''
Khalifa yace." Kai ma kuma kayi gaskiya nan, Amma dai duk da haka ina mai baka shawarar karka tsawwala mata da yawa ka tausaya mata." Yace."Idan ta tausayawa kanta shikkenan idan bata tausay
awa kanta ba ita ta jiyo."
Sosai ya sissiya mata kayan sawa masu tsada da dinki irin na 'yan burni shaddodi da lesuna sunfi yawa a cikin kayan kwata kwata atamfa hudu ce sai material uku sai dakakkun shaddodi da lesuna wanda aka zuba musu dinkuna ma
su kyau....Manya manyan ledoji hudu aka cika da kayan....Yaran dake aiki a shagon suka kai kayan mota Ahamdu ya fito da kudi ya biyasu suka fito daga gurin......Sai da ya koma gidan Khalifa ya dauki motarshi kana sukayi sallama da juna ya wuce gida.
Su Uwani da Rashi Da Camas! har magariba suna bakin gate din gidan Ahamdu kamar wasu Mayu sai naci sukewa masu gadi su bude musu sun'ki Daga karshe ma da suka takura musu bulala suka fito da ita sukace idan basu bar gurun ba sai sun zanesu, babu shiri suka
bar gurun ransu idan yayi dubu ya 'baci!
Tun bayan futarsa a dakin take kwance a gurun tana tsiyayar da hawaye sai wata iriyar makyayata takeyi tana zabura sanyi sai ratsa jikinta ya keyi 'kashushuwan jikinta tana jinsu tamkar ana kwankwasa su da du
ste takure jikinta tayi guri guda jikinta sai d'ari yake yi yana mazari!!! Kafin kice kwabo ta soma ficewa daga hayyacinta.
Littafin na kudi ne......!
Kika futar min da book Ke da Allah! Kika karanta baki biya ba kema Ke da Allah! Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[07/08, 11:49 pm] +234 803 238 4602: 'Yr Bngr Sys
*26*
Yana tura kofar dakin ya ganta a kwance inda iya ajiyeta tun safe zuwa wannan lokacin ta riga ta gama fucewa daga hayyacinta domin idanunta sun juye sunyi fari t
as ya tsun hannuwanta duk sun tankware sun tsaya cak! babu abinda yake aiki a jikinta a lokacin sai saman idonta dake dan harbawa kadan kadan Numfashi kuwa da kar take jawo shi yana kufcewa.....Da mugun sauri ya dire ledojin dake hannunsa ya nufi inda take
, hannu yasa ya tattaro ta jikinsa yana tatta'ba ta, Yayi gaggawar cusa hannunsa cikin rigarta wani mugun zafi yaji a jikinta ya cire hannunsa sauri ya kinkimeta ta mike sambal tamkar Matacciya kan bed ya kwantar da ita, juyawa yayi da azama! sai kuma ya d
awo kanta ya tsaya duk ya rude kansa ya juye ya rasa ma wane taimako zai mata....da alama daf take da shekawa barxahu ganin yanda take jin jiki da jawo nufashi da kyar! A gaggauce ya nufi toilet dinshi ya ciko karamar roba da ruwa ya dauki