Showing 12001 words to 15000 words out of 176422 words

Chapter 5 - YAR BANGAR SIYASA COMPLETE

tasan bata kyauta sai bayan ka bar gurin ne ta dago fuskarta nan na ganeta.......Jim! na minti biyu kafin yace."Kyaleta kawai shigo dasu muje dare nayi taci albarkacin abokanan tafiyarta."

Garba baiyi tsammanin hakaba saboda

yasan halin Ogan nashi baya barin bashi babu shakka yarinyar nan na samu dama a gurinshi..........Wasila kam masifa ta hau yiwa su Uwani wai lallai sai sun shiga motar tunda Allah yasa zai tamaike su ita kuma kunya tasa tace dole su dauki kayansu su karas

a da kafa ai sun kusa isa gida babu yanda zasuyi da ita suka dauki ledojin suka hau tafiya fakam! fakam!!! Garba ya cimmusu yana fad'in"Yallabai yace."Ku shigo muje ku kawo kayan." Ya hau kar'bar na hannun Rashida ta sakar masa dan dama ita ta riga ta gaji

tsoron masifar wasila takeji Uwani ta kalli Wasila dake cigaba da tafiya tace"Haba Wasila ki tsaya mana a taimaka mana kinsan fa kafin muje gida mun galabaita gashi kin san inada ciwon kirji idan ya tayar min kamar zan mutu.

Tace"Tunda dai kun nace sai

mun shiga muje amma meye saura anan mun kusa zuwa 'yan babura fa." Rashida tace"Eh duk da haka dai aunty Wasila ai ragi ragi ne." Shiru tayi musu suka kawai tabi bayansu a zahirin gaskiya bata son shiga motar dan dai kawai sun nace ne! Yana hango zuwansu

gurin ya fito daga bayan motar ya bude gaban motar ya zauna gilashinsa ya gyara, ya tamke fuskarsa yayi dakacen hada jiki da ita ko da yake ai itace ta rungumeshi........Yana da tausayi sosai mussaman kan 'yaya mata shine dalilin ma da ya sanya ya tsaya a

mma da yasan yarinyar nan ce mara kunya babu abinda zai sanya ya tsaya ya 'bata lokacinsa Hanyar biri daban ta mota daban.

Suna shiga motar sanyi Ac da kamshi ya bakunce su, Uwani ce a farko sai Rashida Wasila ta zama karshen shiga motar sai dauke ka

i takeyi bata so su hada ido dashi gashi sun zauna a site daya tana kallon fuskarshi ta mirror ya hade rai! sai itama ta hade nata ran! tayi kasa da kanta, ita sam wannan taimakon baiyi mata ba saboda babban abun kunya ne guy nan yaje yaga makwancinta duk

da haka dai ba zata bari su shiga ciki ba a bakin titi zasu sauka.

Jin surutun da su Rashida yayi yawa yana nema ya karasa wata damuwar bayan wacce yake ciki......Sai ya sanya hannunshi ya kunna redio karatun alkur'ani ya soma a tashi daga bakin *Ahamd

Sulaiman* Duk da haka dai su Uwani basuyi shiru ba sai surutu suke suna ta zancan 'barayin da suka tare su.

Gyaran murya yayi sai suka yi shiru suna kallonsa....Wasila ta dan ja tsaki kadan tace"Dan Allah kuyi shiru idan munje gida kwayi maganar haba."

Shiru sukayi basu sake cewa komai ba motar ta cigaba da tafiya.

A hankali ya dago idanunsa dake sakaye da gilas yana kare mata kallo ko da wasa baza kace ita yake kallo ba saboda yanda yake wani basarwa.......Yarinyar nada kyau! sosai sai dai bata d

a kunya ko kad'an! shi kuwa baya shiri da mara kunya marasa ganin girman na gaba dashi.

Dai-dai bakin titin 'yan babura Wasila tace"Ajiye mu anan ba sai ka shiga damu zamu karasa da kafafunmu.

Uwani tace"Haba 'yar nan ki bari mana a karasa damu mana

mutumin nan fa taimakon yake yi kar ki katse masa hanzari." Dan Allah aunty Wasila ki bari a karasa damu." Rashida ta fadi maganar tana karyar da kai.....Sai magiya take mata kamar zatayi kuka."

Yace."Garba shiga da motar nan ka kaisu har kofar gidansu

kar ka dakata maganar ta." Yace."Angama Yallaba.'!

Uwani tace"Mungode sosai Allah yayi albarka alhaji Allah yasa a gama lafiya, Allah ya raya zuria." Ya amsa da "ameen." yana duba wayarshi....Wasila kam! sai shan kunu takeyi sam bata so haka ba dan dai

kawai sunfi karfinta ne.

Wani tsukakken layin suka shiga motar ta dinga gwajab gwajab!! tana cijewa......Ya dan gyara zamanshi yana duba yanayin ungywar kai da gani kasan unguwace ta marasa galihu gidaje kananu babu tsayin katangar arziki ga kwatoci

duk sunbi hanya abun babu kyan gani sam unguwar bata yi masa ba, bai shiga mamaki ba sai da yaji muryata na fad'in"Tsaya anan ga gidanan ai." Yabi gidan da kallo yana mamaki! wai sunan angyara ansa kofa da lokacin buhu ne abun sai ya bashi mamaki dan adam

ke rayuwa cikin wannan gidan rubabbe lokacin damuna mutum na cike da fargaba da alhini kar ya rikito masa amma su haka suke kwanciya hankalinsu kwance......Tausayi suka bashi yanzu ya gane abunda ya sanya yarinyar famtsama harkar Jagaliya talauci masifa n

e! da'alama kuma su kadai suke rayuwa a gidan.....Tunaninsa ne ya katse lokacin da ya hangota tana bude

gidan...Uwani da Rashida sai faman godiya suke masa, Ya bude wani guri a cikin motar kudi ya dauko a daure a kyaure! ya mika ma Uwani ta karba hannunta

na rawa gwiwa kasa ta zube tana godiya yace."Tashi dan Allah kamar hakan bai dace ba nayi niyya ne na baku amma akwai 'yar shawarar da zan baku idan babu damuwa." Tace"To Alhaji Yace."Ki hana 'kanwarki harkar Jagaliya sam bai dace da 'ya mace ba ni zan tai

make ku sannan idan kun samu mijin aure kuyi aure ni zan dauki nauyin komai naku." Sai Uwani ta fashe da kuka tana fadin "Alhaji labarinmu mai tsayi ne Wasila kuma ba kanwata bace babbar 'yata ce sai Rashida su kadai na haifa marayu ne babansu ya mutu tun

kafin suyi wayon haka sannan duk dangi sun guje mu saboda bamu dashi mune muke ciyar da kanmu kaga kuwa har jagajiya ai sana'a ce bazan iya hanata ba tunda gashi ta rufa mana asiri."

Yayi shiru yana sauraronta tausayinta yaji ashe itace mahaifiyar yaran s

hi ya dauka yarsu ce, Ganinta tana kuka ya sanya yace." amma al'amarin akwai hadari a ciki tunda kun daukeshi a matsayin sana'a Allah ya taimaka." Uwani ta amsa da "ameen tana sake godiyar kudin da ya basu....Ahamad ya bawa Garba Umarnin tafiya Garba yaja

motar suka bar gurin Wasila kuwa ta jima da shiga gida sai haushin tsayuwar su Uwani takeyi a waje Allah yasa dai ba ro'konsa suka tsayi ba tasan halin masifar kwadayi da roko na mahaifiyar tata.

*'YAR BANGAR SIYASA!!*



🌺

romantic love story

🌺

*NA:

*

*BINTA UMAR ABBALE

🍒

*

*

🌍

Manazarta Writes asso*

_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_

~~~~~~~~

*NA KUDI NE.......!*

_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtb

ank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 kati

n airtal ko oragne_

*Free Pege10*

Suna shiga cikin gidan Wasila ta rufe su da masifa,"Haba Uwani nifa bana son 'karanta bisabillahi yanzu minti na nawa da shigowa cikin gidanan kuna can kuna maula da zubda mutunci dama tunda naji shiru nace to kun ts

aya roko wane irin rayuwa ce ban saka kaina ba a akanku amma duk da haka sai kun watsa min kasa a ido idan kuka ce haka zaku dinga yi to wallahi zan barku da halinku ko na samu kudi in boye kaya na."

"Haba 'Yar nan, mutumin nan ya cancani a tsaya ayi ma

sa godiya ba don komai ba sai dan taimakon da yayi mana a wannan zamanin ba ko wane mai kudi ne zai tsaya ya taimaki talaka ba yanzu idan da badan yazo gurin ba da me kike tunani zai faru tsakanin da 'barayin nan nasan wallahi sai sunyi mana tas! wannan bu

durcin naki da kike tattalawa su keta shi da wagari ya waya ai dole a tsaya ayi masa godiya ba abunda kike tunani ne ya tsayar damu a gurinsa shine dai yayi niyya ya bamu kudi kingasu ma."

Ta mika mata daurarrun kudin dake hannunta, Wani banzan kallo ta

yi wa kudin kafin tace"Yanda ya baku kudin to ku ajiye ko lissafawa bance ayi ba ni ina da a'kida idan ina son mutum a siyasance ina sonsa idan bana son mutum bana sonsa dan haka banga abunda kudinsa zasuyi min ba tunda dai ina dasu."

Uwani da Rashida s

uka saki baki suna kallonta da mamaki! wannan kudin masu tarin yawa zasu aje to akan me? ai su ba 'yan siyasa bane kuma ai ba ita ya bawa kudin ba su ya baiwa ballanta tace.

Wasila tace"Ko kuna so dai inyi muku bayani dalla dallah akan mutumin nan domin

naga kudinsa duk ya furgitaku."

Uwani tace"To ai kece naji kina wata magana a wannan zamanin ayi maka kyautar kudi ka mayar gaskiya abin da kamar wahala."

"Uwani wannan guy fa shine dan takarar Governor a yanzu dashi suke fafatawa da Governor mai ci

a yanzu kuma duk kudin da kikaga na samu ta bangaran harkar siyasar nan to ta dalilinsa ne dan akanshi muke jagaliyarmu saboda haka duk ranar da mai girma governor yasan da cewar ina bangare biyu a wannan harkar to yan kudin da nake samu zai hanani dazu f

a cewa yayi zai zauna dani na fada masa dukanin bukatuna sannan kuma ya sauke mukamin wani a dora ni a kai nan gaba kadan ina ganin zan zama 'kusa a harkar dan haka banga amfanin da wad'annan 'yan kudin zasuyi mana gobe insha Allah kafin mu isa government

house zan kai masa kudinsa har gida bama bukata."

Uwani tace"Kuma fa hakane maganarki Wasila duk ranar da governor ya gane baki da a'kida to kashinmu ya bushe gwara ki tsaya a bigire guda mussaman yanzu sune ludayin su yake kan dawo zamu kwashi roman d

a mukarad'iya gwara mu tsaya da kafafunmu kafin ya sauka.

Wasila tace"Ashe kin gane abunda nake nufi dan haka bani kudin na ajiyesu taimakon da yayi mana kuwa shine yayi niyya 'yan kudinsa baza su sanya ni na sauka daga a'kida ta ba." Uwani ta mika m

ata kudin ba dan ranta yaso ba sai dan ba yarda zatayi da 'yar tata.

******

Tunda suka doso layin suke ganin cincirindon mutane wasu na shiga wasu na fita ga 'katon gate din da ya zama security ga estate din a bude jama'a sunja dogon layi sai kar'bar t

allafi sukeyi layin mata daban na maza daban.....Camas! tace"Kawata me yake faruwa ne naga mutane sunja layi." Wasila ta gyara ni'kab din dake sakeye da fuskarta tace"Zai wuce kamfen yake domin yaudarar al'umma amma dai bari mu tambayi wannan matar."

"

Baiwar Allah dan Allah me akeyi anan gurin."? Matar ta tsaya tana washe baki tace" Tallafi mai girma Governor mu na gobe yake raba mana mata dubu goma maza dubu ashirin."

Wasila tace"Ke kin samu kenan."? Cike da farin ciki matar tace"Na samu mana gasu m

a nasa a cikin jakata, zuwa zanyi na siyo gyada buhu biyu mu dinga soyawa da yara na kafin muga abunda Allah Zaiyi."

Wasila tayi murmushi tana jan tsaki tace"Kin san wani abu."? matar ta girgiza kai...."Zan baki baki dubu ashirin yanzu kije ki watsa m

asa kudinsa kice baki so kudinsa basu isa su siyi 'kuri'arki ba mulki kuma sai dai yaga anayi." Matar tabi Wasila da kallon mamaki.! Wasila tace"Ko dai kudin da na fada sunyi miki kadan ne to na kara miki talatin akai sun zama hamsin nasan dai zasu isheki

kija jarin ko wace sana'a ce."

Matar tace"Bana son roman baka yarinya in fara gani a'kas! tukkuna." Wasila ta zaro jakarta dake rataye a kafada ta lissafa kudi dubu hamsin cif tace kin gansu a hannuna kina aiwatar da aikin dana saki zan baki su.

La

raba na ganin kudi dumus a hannun Wasila sai ta gigice! tace"To yanzu ya za'ayi na shiga gurinan akwai 'yan sanda sosai a gurin kuma suna ganin shige da ficen jama'a kana suna gane wanda ya fita da wanda ya shiga kuma kina ganin idan na aikata hakan ba za'

ayi min komai ba."

Wasila tace"Karki damu malama muje tare zamu sanyaki a tsakiya ba zasu gane ki ba." Laraba tace."To ku muje." Kai tsaye suka durfafi kofar shiga gurin jami'an tsaron dake tsaye a gurin sukace su tsaya wani abu suka kara a jikinsu mint

i biyu sukace su wuce ciki.......Wasila da Camas! suka kama layi kamar gaske! Laraba kuma ta mike hanya dan isa inda yake tsaye..........Tana zuwa ta watsa masa kudinsa a jikinsa da karfi tace." *Bama so bama yi! wa 'yan nan 'yan kud'in naka basu isa su si

yi kuri'armu bamu ba!.* Ai sai gurin ya kaure da hayaniya Garba da Hadi sukayo kan laraba Ahamad dake tsaye cikin dumbun mamaki ya hanasu dukanta, su kansu Police din dake tsaye a gurin Sunyi mamakin matar amma ya hana a ta'bata komeye dalili oho."

Ya K

alli Garba a nutse yace."Zo ka tsaya ka cigaba da raba musu." Garba ya tsaya inda yake shi kuma ya kalli Laraba dake tsaye jikinta yayi sanyi kalau yace."Baiwar Allah bance dole ki za'be ni a matsayin d'antakarar ki ba wannan kudin da nake raba muku duk ka

rshen wata inayi ne saboda Allah ba da wata manufa fa ra'ayinki ne ki za'be ni ko ki za'bi abokin gamayya ta ni nasan ba zai iya siyan 'yanci ki ba nafi so duk wanda zai za'beni ya za'beni saboda Allah da kishin kansa da kuma 'kasarsa...."

Laraba ta fas

he da kuka tana fad'in"Kagafarce ni yallabai! wallahi bayin kaina bane roman baka akayi min wata yarinya ce yanzu tayi min alkawarin zata bani dubu hamsin idan na aikata maka haka yanzu kuma wad'annan maganganun da kayi sunyi bala'in kashe min jiki don gir

man Allah ka gafarce ni."

Ahamd ya sauke ajiyar zuciya shi sam baiji zafin matar ta saboda yasan irinsu siyansu ake da 'yan kud'i kad'an! saboda an san shi talaka bukatarshi kudi ko ta halilin kakane zai iya siyar da 'yanci akan sabulu ko omo ko sukari.

Yace."Yanzu zaki iya nuna min inda yarinyar take."? tace"Kwarai kuwa Yallabai ai gatacan ma ta kama layi." Ahamd ya goya hannunsa a baya suka mike dogon layin dake jere da mata har suka inda su Wasila suke....."Gata nan Yallabai."! Laraba ta nuna Wasil

a dake tsaye fuskarta da ni'kabi.....Zatin ta kawai ya kalla ya gane ta ya d'an tsirawa idanunta kallo dake ni'kab itama ta sama ido suna kallon juna.....Ya d'an juya a

nutse ya kira police yana karaso yace."Zura mata ankwa ka kai min ita cikin gida."

Camas! tace"Innallihi wa'ina ilahi raji'un! Jama'a me mukayi baiwar Allah me tayi miki zakice itace haka kawai dan sharri! Yalla'bai wallahi ba ita bace hasali ma mu yanzu muka shigo gurin kuma ai ba ita kadai ce mai niqab ba a gurin." Ahamdu ko sauraranta

baiyi ba ya bar gurin.

Camas! ta dinga ihu! tana zagin Laraba Wasila ta dinga turjewa tana fad'in''Me nayi muku wannan sharri tayi min bani bace wallahi Police din yace."Wallahi idan bakiyi shiru ba zan fuxge wannan niqab din dake fuskarki in yaso kow

a ya ganki munafuka kawai."

Jin abinda Police din yace ne sai ta daina turjewa saboda bata so ya cire mata niqab jama'a su ganta akwai tozarci sai kawai ta hau fuffukar 'karya da fad'in"Ai gaskiya daya ce kuma wanda ya zalinci wani Allah yana gani haka

kawai saboda rashin adalci za'a sanya min ankwa sai kace 'barauniya ko kuma wacce tayi kisan kai!! kuma a haka ake cewa za' a iya mulki wannan ba adalci bane wallahi duk wanda ya shiga hurima na barshi da Allah."!!!

Dan sanda kuwa ya tasa 'keyar ta tana

tafiya tana surutai da farfad'ar bakake maganganu masu harshen damo wanda wanda ake dominsa ya sani masu hankali ma a gurin sun gane da wanda takeyi....Angizata yayi cikin gate din yayi ya mayar da 'kofa ya rufe......Ta waiwaya bayanta babu kowa har masu

gadi duk suna waje gefen bainci masu gadi ta zauna gabanta na fad'uwa sai yanzu jikinta yayi sanyi da al'amarin, dole ta cire tsoro da shakku a kan abunda zai faru ita dashi tayi al'kawarin ba zai ta'ba samun nasara a kanta ba.......Can ta hango shi ya f

ito daga wata iriyar kofa ta gilas ya durfafo inda take zaune gabanta ya dinga duka yana daka! mussaman ganin yanda fuskarsa take had'e tamkar hadarin da ya daf da zubar da ruwa.

*'YAR BANGAR SIYASA!!*



🌺

romantic love story

🌺

*NA:*

*BINTA UMAR

ABBALE

🍒

*

*

🌍

Manazarta Writes asso*

_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_

~~~~~~~~

*NA KUDI NE.......!*

_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan kat

in waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko ora

nge_

_*Babu mahalu'kin da ya isa yayiwa mutum abunda Allah bai masa ba, bama nema gurin kowa! gurin Allah muke nema Allah ka yi mana ba dan mu ba*

👏🏻

_

~~~~~~~~~~~~~~

*Page d'in naku ne*

_HAUWA S ZARIA_

*(Mmn Uswan)*

🌺

_MAMAN MAMY_

*(Shal

ele)*

🌺

*Free Pege11*

Ganin ya kusa isowa inda takene ya sanya tayi maza ta yi 'kasa da kanta gani tayi ya kara wani kwarjini da kamala adduar neman rinjaye ta soma sai dai duk wacce ta dauka sai ta subce ta kamo waccen ma ta subce duk sakamakon tsayuw

arshi a kanta ga masifar kamshinsa ya rikirkita mata lissafi.

"Cire wannan ba'kin abun na fuskarki." Yafad'a cikin wata iriyar murya.....Ta dago kanta tana kallonshi, "Kamar yaya na cir.....Kafin ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login