Showing 141001 words to 144000 words out of 176422 words
raba 'yar uwarta da wannan wahala da take ciki.
Dr Nasir na komawa dakin sai yaga nurses din sun rufu a kanta, tun kafin ma ya
fadi abinda ke bakinsa daya daga cikinsu tace"Dr insha Allah zata iya haihuwa da kanta dan gashinan yaron ya soma fitowa sai da babu karfi a jikinta wanda zata taimaki kanta."
Dr nasir yace."Alhamdullhi kuyi mata duk wani kokari da kukeyi mu gani idan bat
a haihu ba nan da minti goma za'ayi mata Cs domin ceto rayuwarta.
yana gama maganar sai ya fita daga dakin yaje yana shaidawa Amadu halin da ake ciki hannunsa ya daga sama yana rokon Allah ya sauketa lafiya.
To cikin ikon Allah Wasila ta dan samu karfi
da kuzari a jikinta ta dan dunga taimakawa kanta gurin yin nishi yayin da su kuma narses din suke mata dabaru irin nasu, har Allah yasa kan babyn ya soma fitowa sai kawai suka yanke shawarar yankata domin rage mata wahala guri daya suka yanka, aikuwa tana
yin wani yunkuri babyn ya fito tare da mahaifarshi.....Lokacin taji wani irin sanyi duk wani ciwo da takeji ya dauke da kyar ta kalato miyau ta hadiya ma'kogwaronta ya bushe kamas.
Cike da farin ciki narses din suka shiga gyara babyn suna kwarzanta kya
wun yarinyar gata katuwar gaske tamkar ba haihuwar fari ba.........Wasila na jinsu sama sama tsabar wuya da galabaita ta hanata motsa koda d'an ya tsanta ballanata ta bude ido taga abinda ta haifa.
Da saurin nurse ta fita cike da walwala da farin ciki t
a samesu sunyi jugum jugum da sauri tace"Dr ta haihu yanzu an samu baby girl." Dr Da Amadu suka mike da sauri sai suka soma rige rigen shiga dakin Amadu sai washe baki yake kamar gonar audiga.......Ita kam rashida zubewa tayi a gurin tana sujjadar godiya g
a Allah.....Dukaninsu suka shiga dakin, muryoyinsu ya sanya Wasila dan bude idonta tana kallonsu dishi dishi taga sai murna da farin ciki sukeyi suna dariya, rintse idanunta tayi tana ajiyar zuciya tabbas sai yau tasan tazo duniya ashe haka mahaifiyarta ta
sha wuya kafin ta haifeta.......Dr Nasir ya kalli Amadu dake kokarin zuwa gadon da take kwance yace."Yallabai ina ganin dole ayi mata karin jini saboda ta zubar da jini da yawa." Yace."Dr ayi komai idan da hali ma za'a iya daukar nawa idan zaiyi dai-dai da
nata." Dr Nasir yace." okey to zan gwada yanzu."
Kusa da ita ya tsaya yana dan kallon fuskarta lokaci kankani ta rame duk tayi zuru zuru, ya kama hannunta ya rike cikin nashi, idanunta ta bude tana kallonshi, a hankali yace."Sannu." Kanta ta daga mishi
ta maida idanunta ta rufe.........Hajja da Rashida suka karaso gurin suna mata sannu ba tare data bude idanunta ba ta daga musu kanta.....Hajja ta kalleshi da fadin "Gaggawa ta sanya bamu dauko komai ba dole aje a dauko mata kaya t
unda na jikinta sun b
aci." Yace."Bari na koma gidan yanzu." Hannunta ya saki da sauri ya fita daga dakin........Suna tsaye ita da rashida nurses din suka fito daga wani daki sun shirya baby tsaf da ita cikin kayan sanyi tana kamshin turare me dadi.....Hajja ta sanya hannu ta k
arbeta sai washe baki take tana musu godiya........daya daga cikin narses din ta tsaya kusa da Wasila tana mata magana......bude idanunta tayi tana kallon narse din da kyar tace."jiri ne kawai ke damuna sai bacci." Nurse din tace"To bari na taimaka miki mu
je toilet na gyara miki jikinki sai ki kwanta kafin Dr ya shigo." Daga kanta tayi narse din ta kama hannunta suka mike tsaye a hankali a hankali suka nufi toilet din dake cikin dakin.......ma dai-daicin ruwan dumi narse din ta hada mata ta zaunar da ita a
jikin ruwan kana ta samu towel mai tsafta da wani ruwan d'umin tana dan danna mata jikinta.........Fitowa tay daga toilet din wanda yayi dai-dai da shigowarsa dakin hannunsa rike da ledoji Hajja tace"Yawwa kayan ne ko."? Yace."Sune Hajja ina take.'? ya fad
a yana rarraba idanunsa a dakin....Hajja tace "Tana bandaki." Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya dan tsaya kusa da rashida yana le'ka fuskar babyn tashi.....Hajja ce ta karbi kayan hannunsa ta mikawa nurse din ita kuma ta kar'ba ta daukar mata riga da zan
i na atamfa da pants da audiga guda biyu, ta juya da sauri ta koma toilet din
Rashida ta mi'ka masa babyn tana murmushi tace"Yayana kamarku daya da yarinyar na dauka ma zata dauko kammanin anti na saboda wuyar data bamu kafin tazo duniya." Murmushi yay
i ya karbi yarinyar yana kallonta yace."naji dadi da tayo kammanina rashida nima ai nasha wuya kafin na sameta."
Rashida na cike da farin ciki tace"Ubangiji Allah ya rayata ya bawa mamanta lafiya." Ya amsa da "ameen lokacin da yake kara bakinsa kunnan yar
inyar yana mata hud'uba gami da kiran sallah.
Ganin nurse din ta fito da ita daga toilet din a kimtse gashi tana tafiya da kafafunta sai ya sauke ajiyar zuciya yana sake godewa Allah da ya sanya komai yazo cikin sauki.......Dr ne ya shigo yace." Yallaba
i zamuje yanzu a dauki jinin." Sai yay gaggawar mikawa rashida babyn dake hannunsa suka fita daga dakin tare da dr din.....Rashida da hajja suka nufi gadon da Wasila ke kwance suna sake yi mata sannu, kai kurrum take iya daga musu bakinta ya mutu murus har
yanzu tana tuno irin bakar wuyar da tasha acikin awannin da suka gabanta, rashida ta dan zauna kusa da ita a hankali tace"Anti wasila baki dauki babyn ba." idanunta ta bude a hankali take kallon rashidan da babyn tayi murmushi a hankali tace "Rashida yari
nyar na kama da babanta ko."? Rashida tasa dariya tana kallon Hajja tace" Eh mana nida hajja ma haka muka ce." Murmushi ta sakeyi ta rufe idanunta a hankali tace"Allah yayi mata albarka." Rashida da hajja suka amsa da "ameeen"
Bacci me nauyi ne ya dauke
ta wanda tana baccin dr yazo yayi aikinshi ya gama ya fita Amadu kam fita yayi harabar asibitin ya dinga kiraye kirayen waya yana shaidawa 'yan uwa da abokanan arziki karuwar da ya samu.
Karfe bakwai na safe Khalifa da matarshi suka shigo asibitin.....
.....Khalifa ya dauki babyn ciki da farin ciki yake mata addua da fadin Afnan ta samu 'yar uwa dama kullum maganarta yaushe momynta zata siyo mata kanwa."
Hajja da rashida suka saka dariya ya kalli Wasila dake dan murmushi yace "Sannu Wasila Allah ya kara
lafiya kin iya haihuwa gaskiya kin biya mu tunda kika iya haifo mai kama damu." Murmushi tayi cike da kunya ta sunkuyar da kanta kasa, hafsa ta zauna kusa da ita tana mata sannu da jiki hafsa tayi sha'awar yarinyar wasila taji inama itace ta haihu ita yan
zu cikinta watanshi hudu da sauran lokaci.
Bayan sun koma gida misalin uku na rana sai ga mutanan garko Inna hajara da bitan da kuma matar kawu Habibu mai suna Saratu, mai allo ne yace maza maza suzo su gane masa abinda aka samu kafin yazo.......Su Wasi
la sunji dadin zuwansu sosai, nan inna hajara da bitan sukaga irin daular da Wasilan ke ciki dukaninsu mamaki suka shigayi babu shakka ba karamin mutum yarinyar ke aure ba, lalacewa sukayi gurin kalle kalle a gidan har gariba tayi gashi mai allo y
ace s
u koma da wuri, Aikuwa Wasila tace ba xasuyi tafiyar dare ba sai da su bari sai gobe.....Inna hajara tace"Wai ni jama'a gidanan ba'a ganin fad'uwar rana ne? nifa tunda na shigo gidanan nake ganin yanayi daya baka gane ya yanayin gari ya yake wai ashe har m
agariba tayi bamu sani ba oh."
Rashida ta dinga mata dariya tana fad'in "Nima lokacin da nazo gidan haka nayi ta sai da nasaba tukkuna nake ganewa idan lokacin sallah yayi zakiji kiran sallah ko kuma ki kalli agogo."
Ina hajara tace"Yo duk cikinmu waye y
a iya agogo ai kina sake baki sanar damu lokaci ba." Wasila dake zaune kusa da bitan tana shayar da babynta nono tace"Nifa Inna ba zaku koma da wuri ba dukaninku zaku zauna sai anyi suna nayi ar'ba'in tukkuna."
Inna hajara tace"Ashe dai baki da hankali wa
sila yo ai idan wasu suka gamu rud'u rud'u sai su dauka kwadayi ne ya zaunar damu yanzu ma dan dare yayi ne shiyasa da tuni mun tafi." Wasila tace"Dan girman Allah inna ki zauna ko bitan ku taimaka min." Bitan tace"Idan banda abinki wasila wannan baiwar Al
lah na zaune tare dake tana iya bakin kokarinta a kanki ai idan muka zauna sai taga kamar mun raina kokarinta ne." Hajja dake kokarin 'karasowa inda suke tace"A'a bitan ni bazance komai ba wallahi ni kaina zanfi jin dadi ace wata daga cikinku ta zauna tare
damu har yarinyar nan tayi ar'bain." Bitan tace"To sai dai ko Hajara amma dai sai abinda malam yace Hajja tace"malam ba zaice komai ba insha Allahu.
Koda Amadu ya dawo gidan ya tarar dasu Inna hajara sai yaji dadi sosai ya shiga har inda suke suka gai
sa a mutunce yana tambayarsu mutanan gida da malm mai allo, sukace kowa lafiya lau malam yace ayi maka barka kafin yazo.....Yace."Insha Allah gobe zan sanya Garba yaje ya daukoshi domin yazo yaga abinda aka samu.
Kafatanin ma'aikatan gidan babu wanda
bai shigo yaga baby ba, dukaninsu suna cikin farin ciki mussaman Garba da Abdulhadi aranar Amadu yayi musu kyatuttuka duk domin farin cikin da suka nuna bisa ga 'karuwar da ya samu.
Wasila taga gata da kulawa gurin Hajja da inna hajara babu abinda takey
i sai aukin bacci idan kuwa kaga baby a hannunta to nono zata sha yarinyar na tsakanin hannun Hajja da inna Hajara watarana kuma rashida itake rainonta idan tana gida......Malam da Kawu Habibu sunzo sunga baby sun sanya mata albarka sosai nan Amadu ke sha
ida musu sunan yarinyar Fad'imatu sunan mahaifiyarshi kenan.....Malam da kawu suka sanya mata albarka da adduar Allah ya sanya ta zama mai taimakon addinin musulunci.
Ranar suna Wasila ta fito tamkar wata amarya taci gayu sosai da wani uban les Hafsa c
e ta dauko mata me make up tayi mata kwalliya sosai ta shiryata hannayenta da kafafunta sun sha jan lalle wanda yayi masifar kyau yayi jawur abun sha'awa, gold din dake jikinta kuwa abin kallo ne dan ana ya gobe suna ya shigo mata da kayan barka ita da ba
by set din akwatina shida shida makil da kaya iri daban daban wasu a dinke wasu kuma ba'a dinka ba ga uban gold kirar dubai da ya siya mata har kala uku yari da sar'ka da zobuna da abubuwan hannu ko ina na jikinta walwali yake yi.....Hafsa ta gayyaci kawa
yenta manya mata su kansu sai da suka raina kwalliyarsu ganin kwaliiyar mai jego din ta mussamance.......Zeey da Suhairat kam kasa zama sukayi a cikin gidan tsabar bakin ciki da yayi musu yawa ko wacce ta silale ta gudu ba tare da mutane sun fargaba.
Ama
du kam tun da safe kafin ya fita da yaga kwalliyar matar tashi hankalinsa yay bala'in tashi ganin tamkar an 'bare ta daga leda tayi wani 'bul-'bul ta cika ta batse tayi uban kwarjini irin na jego sai daukar ido takeyi, kafin ya barta ta fita daga d'akinsa
sai da ya latsata iya son ransa ya tsotsi bakinta ya tayar wa da kansa hankali mutuka, sai da taga yana kokarin shige gona da iri ne yasa tasa masa kuka tilas ya kyaleta jikinsa na kyarma ya shiga goge mata fuska wai baya so ta 'bata kwalliyarta, da kya
r ta samu ta kufce daga hannunsa, aikuwa bata sake komawa dakin ba har ya fito tana jinsa suna magana dasu Hajja taki fitowa daga daki sai bayan ya fita daga gidan ne ta fito ta cigaba da hidima da mutananta.
******
Bayan suna da kwana biyu gida ya da
wo normal
Hajja da Inna hajara suna zaune a palo bayan sun karya Wasila na cikin daki tana kimtsa kayanta irin wanda ta samu masu uban yawa turaman atamfofi babu adadi ga uban kudin da bata san iya adadinsu ba, dan abokananshi kyauta kudi suka dinga y
i mata wanda takasa irgasu ballanta tasan adadinsu, shi kansa khalifa kyautar kusan dubu dari biyu yayi mata tare da sit din akwati cike da kayanta dana baby Zahra......Ya shigo dakin cikin farin yadi anyi masa dinki irin na zaman gida, idanunsa sakaye
da farin gilashi, tana ganin ya shigo dakin sai gabanta ya fad'i! ciki ciki ta amsa sallamarshi tana dan gyara kafafunta, ya karaso ya zauna kusa da ita yana nani'karta, kamshin turaransa ya bugi hancinta, ajiyar zuciya ta sauke lokacin da taji saukar han
nunsa a bayanta yana tattare gashin kanta daya sauka a bayanta, kafad'arta ya rike sosai ya matso da ita jikinsa murya a kasa yace."Laifin me nayi ne aka daina shigowa gaishe dani da safe."? Dan turo bakinta tayi gaba! Ya sanya dan yatsansa kan le'banta n
a 'kasa yana shafawa cikin wani irin salo, kallonshi tayi da idanunta da suka dan soma sauyawa, ya dan daga mata girarshi guda daya da munafikin murmushi a fuskarshi.........ta mai da kanta kasa gabanta na faduwa kadan kadan......Cikin wata irin murya yac
e." To tunda ke kin kasa zuwa inda nake ni gani nazo kin san hausawa nacewa garin masoyi baya nisa duk inda kika shiga kika 'boye sai na biki." Shuru tayi masa ba tace komai ba, ya sanya hannunsa ya tallafo fuskarta suka kurawa junansu ido.....Wani irin z
allan sonta ta dinga hangowa cikin kwayar idanunsa, ta dinga kallon kyakyawar fuskarshi wacce annuri ke sauka akai a take taji wani masifar kaunarsa na ratsa ilahirin jikinta.....Lumshe idanunta tayi gabanta na wani irin bugawa da karfi da karfi.....Tana j
in sanda yake lasar le'bunanta yana dan tura harshensa cikin bakinta ta wani makale a jikinsa tana sake ri'keshi a jikinta, harshensa dake wasa dashi saman le'bunanta tayi gaggawar sarkafoshi dana ta shiga tsotsa da sauri da sauri tana shafa wuyanshi da sa
isayyar sumar kanshi...........
Littafin na kudi ne.......!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Wasap numbar
*07084653262*alliya:
'Yr Bngr Sys
*74*
Inna Hajara ce ta murd'a 'kofar dakin hannunta rik
e da baby zahra dake kukan yunwa tashinta daga bacci kenan tun bayan wanka safe da akayi mata bacci ya dauketa shine ta tashi tana kuka.....Inna hajara na fad'in "Ai dolene ki tashi da yunwa 'yar nan....kasa k'arasa maganar tayi ganin Amadu zaune a kusa da
Wasila tayi fi'ki fi'ki da ido shi kuma ya sunkuyar da kanshi 'kasa kunyar duniya ta isheshi Allah yasa ma sunyi gaggawar sakin junansu lokacin da sukaji muryar Innan, to amma dai duk da haka inna hajara sai da ta fahimci wani abu tunda dai ai ita ba ya
rinya kankanuwa bace." A'lamarin ya bata mamaki sosai dan dukaninsu suna zaune a palo sam basu ga sanda har ya fito daga dakinshi ya shiga dakin ba, Karasawa tayi tana dan gyara fuskarta tace"Kar'beta ki bata nono kada ta soma wannan kukan nata kin san ba
zakiji da dad'i ba." A sabu'le ta kar'bi yarinyar tana kokarin fito da nono.....Ya mi'ke tsaye yana dan gyara gilashinsa, ba tare da yayi kuskuran kallon innan ba yace."Inna antashi lafiya ya kwanan su Fad'ima." Inna Hajara itama dake ta iya duniyan ci sa
i ta maze kamar bata gane komai ba tace"Lafiyarsu kalau Alhaji ga Fad'imatu nan tayi wayo tubarkallah.'" Dan mirmushi yay yace."Allah yayi mata albarka." Inna ta amsa da "ameen." Yana fita daga dakin Inna hajara ta zauna kusa da ita fuskarta murtuk!!!! tac
e"Wallahi duk sanda na sake gani ya shigo dakin nan kin sakar masa fuska ya ta'baki sai ranki ya 'baci kwana tara da haihuwa har kin soma sakarwa miji jiki ke wace irin 'kwad'ayayya ce ne? ashe baki da wayo Wasila! ashe kin mance irin wahalhalun da kika sh
a kafin ki haihu shine sabida rashin kamun kai zaki saki jikinki har ya shigo yana tatta'baki ko."
Wasila ta kama kuka tana kokarin kare kanta Inna Hajara tace"Rufe min baki ni bana son shashancin banza da wofi! kefa da kanki kike fad'a min anyi miki d'
inki a matuncin ki to har yaushe ya warke da zaki komawa miji shashasha mara wayo kawai."
Cikin kuka tace"Wai Inna me kika shigo ki kaga munayi kawai sai faman fad'a kike min ke baki shigo kinga munayin wani abu ba."! Inna Hajara ta kai bayan hannunta
ta make bakinta tace"Dan Ubanki yarinya xaki mayar dani." Wasila ta kame bakinta tana hawaye.....Inna Hajara ta cigaba da sababi tana fad'i na shigo dakin na ganku makale da juna kuna tsotsa tsotse sannan ki raina min hankali."! Da sauri ta sunkuyar da ka
nta 'kasa tana mamaki ashe duk gaggawar sakin junansu da sukayi sai da ta gansu kai Inna hajara muguwar 'Yar sa'ido ce........Inna hajara tayi 'kwafa cike da takaici tace"Wallahi zan saka ido sosai a kanki duk ranar da na kara ganin kin sakar masa jikinki
har kuna rungume rungume da tsotse tsotse to a ranar zan tattara nawa nawa nayi tafiyata tunda ke kin zama mara kamun kai da rashin kintsi.......Har yaushe akayi abun ? guri duk a d'anyace baiyi kwari ba amma saboda rashin hakuri irin naki ki biye masa ya
cuceki a banza a wofi."!!! Cikin kuka tace"Ni Inna abar maganar dan Allah naji shikkenan zan kiyaye dan Allah kada ki tafi." Tsaki Inna hajara taja tace"Ai bana magana biyu na sake gani da idona sai dai ki nemeni ki rasa a gidanki." Tana gama maganarta ta
fita daga dakin ranta dik a bace
Wasila kuka taci ta 'koshi ta share hawayenta tana cigaba da shayar da babynta tana tunanin abinda ya faru tsakaninsu itama fa ta hango wautarta gaskiyar Inna hajara haihuwar fari tayi, ya kamata ace ta kame kanta a gu