Showing 21001 words to 24000 words out of 176422 words

Chapter 8 - YAR BANGAR SIYASA COMPLETE

naji wannan sa

llama haka to ana zuwa." Uwani tafada tana jan karamin tsaki." Ta kalli Hajara "Ai sai ki tashi kije kece tilas dinsa ni kuwa yace zai min wannan wa'azin sai dai mu kwashi 'yan kallo ni dashi a unguwar nan."

Jiki a sanyaye Rashida ta mike ta dauki yalol

on mayafinta dake kan igiya ta yafa, duk rashin kunyarsu suna shakkar malam mai allo dan baya musu da sauki.........Tana fitowa ta durkusa tana gaisheshi bai amsa ba sai kare mata kallo yake ganin irin dinki dake jikinta atamfa ce duk an kacalcalata saman

nonowanta duk a waje......Girgiza kansa yayi yace"Rashida kece kika dawo kamar ba d'iyan musulmai ba wannan shigar ta jikinki ta sabawa sharia meye abun burgewa anan.? to babu komai duk magana ta kare kiyi maza ki kirawo min daya marakunyar yanzu yanzu zan

tasa ku a gaba mu wuce garko saboda na samu labarin ashararanci da kukeyi a gari mahaifiyarku na daure muku gindi kuna yiwa manya mutane rashin kunya wai Wasila ce take siyasa tana gogayya da maza saboda kasa ta rufe idon ubanku shiyasa annabi yace ka za

bawa 'yayanka mace tagari duk dan gudun faruwar irin wannan, mu ba'a son ranmu dan uwanmu ya auri mahaifiyarku ba saboda sam bata da tarbiya gashi kuma kun dauko irin nata halin to kome zakuyi sai da kuyi amma tilas ku koma can Garko da zama idan Allah ya

kawo muku miji kuyi aur......"Babu wanda ya isa ya rabani da 'yayana wallahi akan wannan sai in maka mutum a kotu."!!!!Uwani ce ke fadar wannan maganar ashe tana la'be tana jinsu......"Haka kawai zaka zo har gida kana zagina malam ka rike mutuncinka da gir

man ka ada can ma ban yarda ba ballanta yanzu da nasan ina da 'kumbar susa a hannuna dan haka ni banga wanda ya isa ya rabani da 'yayana ba."

Malam mai allo yace."Uwani rashin kunya za kiyi min."? Wannan ba rashin kunya bace gaskiya ce, sai da yarana su

ka girma suka zama mutane inacin ganiyarsu sannan za'a lalla'bo kawai saboda an samu labarin mun faso gari ace ga zance ga magana kafad'i idan kana bukatae wani abu yanzu yanzu sai na kira Wasila tayi maka hasafi ba wai kace zaka tafar min da 'yaya kauye b

a."

Malam mai allo 'kwalla ta taru a kwarmin idonsa yace."Baku da kudin da zaku bani Uwani kuma kinyi min abunda yafi haka dan kin zageni a yanzu ba wani abun bane ni dai na gama yanke hukunci ke Rashida idan na isa daku maza jeki had'o kayanku muka ka

ma hanya mu tafi.".

Rashida ta mike ta shiga cikin gidan tana kuka wayarta ta dauka ta kira Wasila ta fada mata abunda ke faruwa.....Wasila tace''Kome zaiyi kar ku sake ku bishi ku kyaleshi a soro idan ya gaji da tsayuwa ya gaji ya tafi masifaffan tsoho

kawai." Uwani kuwa taja tunga ta tare bakin kofa ta rantse babu inda zai tafar mata da 'yaya......Suka dinga tafka rigima da Malam mai allo Uwani ta dinga yi masa rashin kunya kamar ba wan mijinta ba har hankulan mutane ya fara dawowa kansu mutane suka fa

ra taruwa a'lamarin yayi wa malam ciwo a ranshi sai ya fito waje ya tsaya yana tsumayin fitowar Rashida ganin ya fita daga gidan sau kawai Uwani ta rufe kofar gidan ta zura sakata ta koma ciki tana surutai "Idan ka kaji da tsayuwa ka tafi tsoho mai nacin t

siya kawai..........Garba dake can gefe suna magana da wani mutumi ya nuna masa malam mai allo dake bin kofar gidan da kallo yana mamakin rashin kirkin Uwani wato shi suka rufewa kofa, sai ya sanya gefan babbar rigarsa yana goge gumin saman goshinsa.....Ga

rba ya karaso inda yake hannu ya mika masa suka gaisa yace." Aramma idan ba zaka damu ba ina so mu tattauna wata magana da kai." Malam mai allo dake neman wanda zai rarrashe shi kan abunda su Uwani sukayi masa yace."Babu komai yaro ina sauraranka." Garba y

ace."Muje mota arrama." Malam mai allo baiyi shakkun bin Garba ba saboda lokaci guda yaji ya aminta dashi suka nufi inda yayi parking din motar a tare.

_Muje Zuwa_

*BINTA UMAR ABBALE*

[7/18, 2:01 PM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!*



🌺

ro

mantic love story

🌺

*NA:*

*BINTA UMAR ABBALE

🍒

*

*

🌍

Manazarta Writes asso*

_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_

~~~~~~~~

*NA KUDI NE.......!*

_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.054238

2124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars....

...90899076_88137740 katin airtal ko orange_

*PEGE 'DIN YAU NAKI NE*

*Real Eshaa

🌺

*

Marubuciyar book d'in.

*NAGA RAYUWA*

Fatan alkairi har karshen rayuwa aysha Allah ya kawo miji nagari wanda zai rike min ke tsakani da Allah

👏🏻

~~~~

~~~

*Free Pege15*

Cikin nutsuwa Garba yace."Aramma alamu sun nuna kamar kana da ala'ka da masu wancan gidan, dan Allah idan babu damuwa ina so in san wani abu dangane da wata yarinya a gidan mai suna Wasila." Malam mai allo yace."Ni a matsayin mahaifi

nake a gurin Wasila da kanwarta Rashida Yahuza mahaifin yaran kanina ne ciki daya muka fito kuma mu 'yan asalin garin garko ne Yahuza yazo kano neman kudi tun yana saurayi sai ya sai gida yayi aure tare da wannan matar wacce ta kasance a matsayin mahaifiya

r su Wasila da Rashida......Garba ya katse shi ta hanyar fadin"Alhamdullhi dama abunda nake so naji kenan ashe faduwa tazo dai-dai da zama malam idan babu damuwa zamuje can gidan ubangidana wanda shine ya sanya ni nayi masa bunkice akan asalin iyayen yarin

yar to kuma sai nayi katarin had'uwa da kai, kar kadamu arrama idan mun isa sai kayi masa cikakken bayani akan yarinyar." Malam yace."Yaro ina fata dai ba laifi yarinyar tayi ba domin nima abunda ya taso ni kenan saboda na samu labarin cewar tana cin mutu

ncin manyan mutane a gari tana fakaicewa da siyasa wannan shine dalilin zuwa na garin." Garba yace."Kar ka damu arrama alheri ne insha Allahu muje koma meye zakaji daga bakin mai gidana." Malam yayi shiru yana nazari yana tsoro kar daga zuwan sa ya shig

a masifar yarinyar nan tasa a daure shi baiji ba bai gani ba....Girgiza kai yayi yace."Babu

damuwa samari muje kawai Allah yasa alheri ne." Garba ya kunna motar yaja suka futa daga cikin unguwar.

Suna tare da Khalifa a harbar gidanshi suna hutawa motar

su Garba ta shigo cikin gidan.....Can parking spece ya nufa yayi parking din motar ya fito ya budewa malam mota yana fitowa Idanun Ahamdu suka sauka a kanshi A fuzge yaga suna kama da yarinyar babu tamtama wani nata ne amma babu shakka Garba ya iya aiki ba

i dauka futa ta farko za'a samu nasara ba to amma yanda yaga kamilin mutum sai yasha jinin jikinsa anya wannan kudi zasu rud'ashi ko dai ya sauya wata hanyar ne dan baiga alamar zalama ta kudi a idon dattijon ba......A nutse ya mike yana masa barka da zuwa

dake suna zaune a wata rumfa wacce aka kewaye ta da wasu kujeru masu kyau tsakiyar kujerun katon teble ne da lemuka akai kana ganin gurin kasan na hutawa ne....Malam mai allo ya zauna nutse suka gaisa cikin girmama juna......Garba yace."Yallabai Allah ya

takaita mana wahala ina zuwa unguwar nayi katari da wannan bawan Allahn shine yake shaida min shi din shine mahaifin Wasila shima zuwanshi kenan garin to anan na nemi alfarma a gurinshi kan yazo kana son magana dashi."

Cikin girmamawa Ahamadu yace."Alh

amdullahi naji dadi da hakan ta faru dama ni nafi so nayi magana baki da baki da mahaifin yarinyar dan haka Garba kana iya tafiya babu damuwa." Garba ya bar gurin yana godiya....Ahamadu ya sake mikewa Malam hannu suka sake gaisawa Yace."Malam kan maganar w

annan yarinya ne Wasila.'' Malam mai allo ya kalli Ahamadu ganin nutsuwa da kuma a kamala a tattare dashi ya sanya hankalinsa ya kwanta yace."Alhaji ina fatan dai yarinyar nan ba wani laifi tayi muku ba dan wallahi dukkanin abunda takeyi bamu sani ba tunda

bama tare dasu labarin abunda takeyi ne ya iskemu hakan ya sanya hankalinmu tashi, muka yanke shawarar zuwa domun mu tattara su mu koma can inda muke da zama dama kuma zamansu hakan bai dace ba a matsayinsu na 'yaya mata komeye zai iya faruwa da rayuwars

u.

Khalifa yace."Kwarai kuwa malam muma abunda muka hango kenan ya sanya muka sa ayi mana bunkice akan asalin yarinyar sai kuma Allah ya takaita mana lokaci guda kazo gari ashe ma ba a kurkusa kuke ba." Malam yace." Mu 'yan karamar hukumar Garko ne Yahu

za mahaifin yaran ciki daya muke dashi mu hudu iyayenmu suka haifa ni ne babba sai Habibu sai shi Yahuza sannan kanwarmu Kattime To shi kadai ne ya tsalle a cikin mu ya tawo nan yake sana'oinsa har Allah yasa ya samu sana'a ya siyi gida kana yayi aure ya h

ayayyafa yanzu shekaranshi Takwas da rasuwa bayan karamar jinyar da yayi wanda muma sai labarin mutuwarsa mukaji......Dalili kenan da ya sanya nazo da kaina na dauke yaran har da ita mahaifiyar tasu na tafi dasu can garin namu ko sati daya ba suyi ba suka

gudo........Tiryan tiryan Malam ya zayyane musu rayuwar dasu Wasila suka dinga yi tun farkon mutuwar mahaifinsu da irin rashin kunyar da mahaifiyarsu ke sawa suyi musu da yanda shi kuma yayi zuciya ya zare hannunsa daga kansu....Sai wannan karon da yaga ab

un yayi tsamari ya sanya yace bari ya dauki mataki na karshe kan abunda sukeyi.

Ahamadu yace."Arrama yanzu idan ka tafi dasu can Garkon kana da wanda zaka bawa auransu ne."? Malam yace."Ba za'a rasa ba Alhaji kasan shi auran karkara ba'a tsawwala da yaw

a insha Allahu sati biyu ba zasuyi a gida ba zab daura musu aure."

Yace."To idan babu damuwa ni ina son abani auran babbar kuma bana so a ja dogon lokaci idan da hali wannan juma'ar mai kamawa nake so a daure aure."

Malam yace."Alhaji da dai 'kar

amar ka dauka dan sai naga kamar tafi babbar hankali hankalin ka zaifi kwanciya da ita karamar." Yace."Kar ka damu malam shi aure ni'ima gareshi watakila ta sanadiyar auran namu sai kaga tayi hankali fiye da tunani mai tunani idan da hali a amince mun in b

ada sadaki na yanzu." Malam yace."To to ai babu damuwa nima zanfi jin dadin hakan kaga sai in koma gida da karfin gwiwa ta kuma in sanar da 'yan uwa abunda ke faruwa."

Ahamadu yace."Kwarai naji dadin yanda ka yarda dani ka amince min auran yarinyar da w

uri ba tare da kaga waliyai na ba insha Allahu ranar juma'a zamu zo tare da kanin mahaifina Wanda shi kadai ne ya rage min a halin yanzu kasancewar nima tun ban kai matsayin wannan shekarun ba mahaifina ya rasu na rayu tare da yan uwansa wannan kuma da ka

ke gani a zaune kusa dani abokina ne sha'kikina tare mukayi karatu kuma muke harkokinmu a tare insha Allahu tare zamu zo dashi ranar juma'a."

Malam yace."To masha Allah Alhaji ai ni ganin farko da nayi maka naji hankalina ya kwanta da kai wallahi babu d

'ar! zan baka auran Wasila koda banga Waliyinka ba nasan zaka rike mun ita da kyau da amana, babu abunda zance sai dai ince Allah ya saka da alkairi saboda ka gama min komai tunda har ka yarda zaka auri wannan yarinya." Ahamdu yace."Babu damuwa malam, ai

an riga an zama daya kuma Allah dai ya kara girma." Mikew yayi ya nufi cikin gidan..........mintuna goma yayi a ciki ya fito hannunsa rike da wata doguwar takarda dake cike da kudi." Ya mikawa malam na fad'in"Wannan shine sadakin Wasila malam."

Malam y

a kalli uban kudin da ya mika masa sai ya girgiza kai a nutse yace."Ashe baka so auran yayi albarka ba Alhaji Annabi Muhammdu SAW yace."Mafi albarkar aure shine karamin sadaki wannan da yayi yawa duk da ban lissafa na gani ba amma idona ya gane min kudi ne

masu yawa, saboda haka dubu biyar kacal zaka biya sadakin wannan yarinya."

Ahamadu yace."Malam ka ka'rba don Allah ai ba wani kudi masu yawa ba dubu dari ne kacal kuma kasan dai yanda kudin mu suke basu sa wani daraja kar damu insha Allahu aure zaiyi

albarka."

Malam yace."Shi dai ba zai kar'bi wannan zunzurutun kudin ba a matsayin sadakin Wasila ya fiso idan yayi mata aure ta zauna mutuwa ce zata raba.....Ahamadu da Malam suka dinga ta'kardama da jayayya shi ya dage sai ya 'karba shi kuma yace ba z

ai kar'bi dubu dari ba dubu biyar zai 'karba....Khalifa ne ya raba gardama ya ciro kudi daga jikinsa dubu goma ne ya irga dubu biyar ya mikawa Malam yace."Ga sadakin Wasila daga Ahamadu." Malam ya sanya hannu biyu ya kar'ba yana fadin"Ubangiji Allah ya tab

batar da alkairi Allah ya basu zuria mai albarka." Khalifa ya amsa da "ameen rabbi malam muna godiya da karamci."

Ahamdu yaji haushin abunda khalifa yayi masa amma bai nuna ba sai ya aje takardar kudin kan teble din gabansa dauki wayarshi ya kira Garba.

.....Garba na zuwa yace maza ya fito da mota ta zuba kayan abinci komai da koma yazo ya dauki malam ya kaishi har Garko Garba ya wuce da

sauri domin aiwatar da aikin da aka sa shi. Ahamadu yace."Malam yanzu Garba zai kai gida maganar su Wasila kuma da kai

na zan sanya a kai maka su har inda kake daga gobe jibi insha Allahu." Yace."To Alhaji Allah ya saka da alkairi ya biya dukanin bukatu na alkairi."

Bayan tafiyar Malam mai allo Khalifa ya kalli Ahmadu yace."Na lura wannan dattijon na arziki ne wallahi

sai duk naji jikina yayi sanyi musamman yanda naga ya tsaya kai da fata akan ba zai kar'bi wannan kudin da ka bashi a matsayin kudin sadaki na fahimci yana so auranku da yarinyar yayi albarka wanda kai ba haka abun yake ba a zuciyarka, dan Allah ka kar k

a watsa wa mutumin 'kasa a ido ka rike yarinyar nan amana ko dan saboda karamcinsa kamar yanda ka fad'a masa watakila ta sanadiyar auran sai kaga tayi hankali duk abubuwan da suka faru a baya su wuce kamar ba'ayi ba."

Shiru yayi yana nazarin maganar kha

lifa din yace."Nima jikina yayi sanyi lokacin da naga mutumin sam! ban dauka zanga kamilin mutum daga bangaran yarinyar ba ashe ta fito daga tsatso mai kyau gaskiya wannan mutumin ba duniya ce a gabanshi ba ka duba ka gani kudi a wannan zamanin sam basu ga

bansa wasu iyayen da suke so in kaje neman auran 'yayansu ka sakar musu kudi a gurinsu hakan burgewa ce, shi kuma na lura albarka kawai yake nema."

Khalifa yace."Shine ai shawarar da nake baka rike masa yarinyar shine zai sanya ya tabbatar da cewa kai

d'in mutumin kirki ne.""

Murmushi yayi yace.''Kai nifa ina nan kan bakana wallahi! sai naci uban yarinyar nan wallahi in keta ta kuma in saketa."

Khalifa yace."Subahanallahi! wai me yasa kake hakane? ka sani kake takewa yanzu meye amfanin hakan da za

kayi."? Sosa kanshi yayi yace."Ai kai dama ba za kaga amfani ba saboda ba kai akayi wa auran nan da zanyi zanyi shine da manufofi da dama kaga na farko zan tashi daga sunan Gwauro kamar yanda ta fad'a zata zame min garkuwata a siyance na biyu zan dawwamar

da rayuwarta a cikin 'kunci da ba'kin ciki in takure ta guri guda in muzguna mata har sai ta durkusa gwiwa bibbiyu tana bani hakuri na uku kuma na taimake ta daga wannan yawace yawacen banzan da takeyi a gari tana zubda mutuncinta na killace ta a guri gud

a....Na hudu kuma auranta zai wanke ni daga zargin da tasa jama'ar gari suke min....Ita ta nufe ni da sharri ni na saka mata da alkairi kaga anan jama'ar suka ji labarin na aureta za tasha tofin ala tsine da zagi sannan ita da harkar Siyasa har abadah! na

biyar bukatata ta biya na raba abokanan adawata da ita tunda yanxu kamar itace a matsayin yarinyar su wacce suke sanyawa nayi musu abu ba tare da shakkar kowa ba, nasan kafin su samu 'yar siyasa mai mutukar a'kida irinta za'a sha wuya, kasancewar siyasar

mu ta yanzu ta zama sai a hankali duk inda mutum yasan zai samu nan zaije hakanan za kagansu yau su zagi wancan gobe su zagi wanannan sam basu da gwani mutum in dai zaka bashi na 'batarwa shikkenan magana ta kare, amma ita yarinyar ns fahimci ba wannan

ke gabanta ta tsaya bangaransu su kadai shiyasa suka riketa hannu bibbiyu saboda sun lura abokiyar tafiya ce....Kuma kasan ba zasu ta'ba bari tayi aure ba zasuyi ta bata kudi tana shirme a gari rayuwarta ta lalace a banxa a wofi.''''' Khalifa yace."Kayi t

unani me kyau gaskiya amma dai duk da haka don Allah ka sassauta mata idan ta shigo.

Murmishi ya saki mai dauke da manufofi da dama ta'be bakinsa yayi yace."Kana 'bata bakin ka ne khalifa yanda yarinyar nan tasa ni 'bacin rai itama ranta sai ya 'baci."

_Muje Zuwa_

*BINTA UMAR ABBALE*

[7/18, 10:18 PM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!*



🌺

romantic love story

🌺

*NA:*

*BINTA UMAR ABBALE

🍒

*

*

🌍

Manazarta Writes asso*

*'YAR BANGAR SIYASA!!*



🌺

romantic love story

🌺

*NA:*

*BINTA UMAR AB

BALE

🍒

*

*

🌍

Manazarta Writes asso*

_'Kungiyar masu nazari

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login