Showing 129001 words to 132000 words out of 176422 words

Chapter 44 - YAR BANGAR SIYASA COMPLETE

biyu anan gaba dan ga

skiya ina da ra'ayin yin hakan." Alhaji Muktari ya bashi hannu suka tafa.....Amadu kuwa kallonshi yay da mamaki a fuskarshi yace."To tunda ka tona asirin ranka sai na fad'a mata kasan ni da Hafsa akwai amana ba zan yarda kaci amanarta ba."

Khalifa yasa

dariya yana fad'in "Kafi tsuntsu gudu dan Allah! haka kawai Allah da annabi sun halasta min ace kada nayi, Kasan Allah idan lokacin aurena yazo dole ne Hafsa tayi hakuri dan ina da wannan niyyar." Amadu ya dinga girgiza kai yana kallonshi, shi kam a nashi

ra'ayin bai son had'a mata biyu ko sama da hakan a ganinshi duk damuwa ce mutukar matarshi zata dinga dauke mishi dukanin laluranshi bai damu da lallai sai yayi wani auran ba koda kuwa ya samu mulki a nan gaba.

Tattaunawa suka shigayi da sabbin tsare t

saren da zasuyi mutukar Allah ya cika musu burinsu akan abinda suke nema mutukar sun samu nasarar d'arewa kujerar mulki to babu shakka Al'ummar jahar kano da katsina zasuyi farin ciki zasu ga sauyi ta ko wanne 'bangare

Misalin 'karfe tara da rabi na da

re suka fito daga gest house d'in Alhaji Muktar yace yana so ya duba Wasila kafin ya koma dan gobe da asubah yake so su wuce, To dan kar ya watsa masa 'kasa a ido ne ya sanya ya amince da bukatarsa, saboda baya son abinda zai sanya girma da mutuncinsa ya

zube a idonshi, baya so suje gidan Yarinyar tayi wani abun wanda zai nuna babu jituwa a tsakaninsu domin har yanzu ya lura da ita bata wani saki jikinta ba sosai.

Goma shaura motarsu ta shiga cikin gidan garba nayi parking ya fito cikin sauri ya bu

de musu kofa suka fito, tare suka nufi cikin gidan dukaninsu harda khalifa.

Rashida ce ita kad'ai a palon tana kallo Hajjah tuni ta shige daki ta

kwanta dan tanayin sallah isha'i take kwanciya, Wasila kam bata jima da barin palon ba itama wanka ta s

higa tayi ta kwanta dan har yanzu jikinta bai dawo dai-dai ba akwai sauran gajiyar hanya

Rashida ta mi'ke tsaye tana musu barka da zuwa, ta gaishe su a nutse tana kokarin shigewa Har zai yi mata magana sai kuma yaja bakinshi yayi shuru ya kalli Abokan n

ashi a nutse yace."Bari na fito da ita." Khalifa yace"Kada kayi wannan dad'ewar da ka saba." 'Karamin tsaki yaja ya yana girgiza kanshi ya tura kofar dakin ya shiga wanda yayi dai-dai da lokacin da ta fito daga toilet jikinta daure da towel iya cinyarta..

...Sallamar dake dauke a bakinsa ce ta gagara fitowa, da kyar ya janyo dauriyarshi da jarumtarshi ya shiga dakin, 'Dan tsayawa tayi tana kallonshi tana turo bakinta gaba, shiyasa ta'ki shiga dakinsa ta gudo nata ashe bata tsira ba yazo zai takura mata, 'Ba

ta fuskarta tayi ta wuce a hankali taje ta zauna gaban mirror tana bud'e man shafawa

Bayanta ya tsaya yana kallonta ta cikin mudubin tana shafa mai a hankali tana shafawa a hannunta, ba tare da yace komai ba ya sanya hannunshi cikin vasilin din ya som

a shafa mata sassan jikinta, jin saukar hannunsa a jikinta ya sanya ta sauke ajiyar zuciya me tafe da tashin tsigar jiki, hannunsa ta cire wanda yake kokarin cusawa cikin towel din ta sake daure kirjinta dashi, bai ce mata komai ba, ya dan rankwafa a hanka

li ya d'an ja 'kafafunta ya soma shafa mata vasilin din a cinyoyinta da kafafunta.......Ido ta tsira mishi yayin da kanshi ke 'kasa, taji wata 'kwallah na kokarin zubo mata daurewa tayi ta dauke kanta da sauri lokacin da ya dago ganshi, bayan ya gama shafa

mata vasilin din, Ta mike tana sake rike daurin towel din a kirjinta wardrobe ta nufa ya bi bayanta, kayan bacci masu taushi ya dauko ya rike hannunta a hankali yake kokarin kwance towel din, tasa kuka tana tureshi, ya mi'ka mata kayan da fad'in "Kiyi gag

gawar sanyawa tunda baki so nasa miki akwai 'baki na jiranki a palo abokina ne yazo duba jikinki.'' Cikin rawar murya tace" Ni ka fita to nasa kayan zan fito yanzu." Harararta yayi yace."Meye abinda zaki 'boye min a jikinki ? wai ke dan Allah yaushe zaki d

aina wannan 'kauyancin ne? Shiru tayi mishi ta nufi bed da kayan a hannunta, zama tayi gefan gado ta soma zura dogon wandon tana kare cinyoyinta da towel, shi dariya ma take bashi wallahi, yay tsaye a kanta har ta gama sanya kayan ya mi'ka mata 'katon hij

ab d'inta na sallah tasa kana ya nuna mata hanya da hannunsa......Gaba tayi yabi bayanta haka suka fita palon.

Alhaji Muktari ya kalleshi a lokacin da suke karasowa inda suke yace."Ashe dai da gaskiyar khalifa shiyasa kafin ka shiga ya tuna maka.'' Ama

du yayi sauri bagarar da zancen dan baya so ta fahimci inda zancen nasu ya dosa, shi baiga wani dad'ewar sa a ciki ba sa'ido ne kawai irin na khalifa.

Ta gane khalifa, d'ayan ne bata gane ko waye ba, a nutse ta zauna kusa da mijin nata ta shiga gaishe

su, Alhaji Muktari ya shiga mamakin 'kan'kanuwar yarinyar wai itace matar abokinshi Yo ai wannan za tayi sa'ar babbar 'yarshi Sa'adatu, babi shakka dole abokin nashi yace bashi da sha'awar 'kara wani auran saboda yasan yana da wacce zai mori 'kuruciyarshi

da tsufanshi.

Cikin kulawa yake amsawa ya dan tsokanta ita kuma sai sunkuyar da kanta take kunyar mutumin takeji sosai ganin kamar ma ya girmi mijin nata, Wanda sam ba haka bane Alhaji Muktari sa'an Amadu ne dan shima baifi shekaru arba'in da biyar ba ,

kawai dai dan yayi aure da wuri ne kuma yana da jikin girma ba kamar Amadu da bai da 'kiba ba, Tana zaune tana sauraransu suna hira duk ta 'kosa ta bar gurin ta d'an muskuta a hankali zata tashi, Ya ri'ke mata hannunta ba tare da ya kalleta ba ya juya s

uka cigaba da magana da Khalifa, tamkar zata fashe da kuka haka ta kalleshi to meye amfanin zamanta a gurin bayan sun gaisa ba sai ya kyaleta taje ta kwanta ba......Kirane ya shigo wayar Khalifa sai lokacin suka san dare yayi sosai sha d'aya da rabi Hafsa

taji shuru bai dawo ba ta kira wayarshi, Ya mike da sauri yana kallon agogonshi, yace"Ashe dare yayi sosai sha d'aya da rabi yanzu." Duk sai suka mi'ke tare Alhaj

i Muktari yace."To Uwargida kuma amarya xamu tafi Allah ya 'kara sauki ya kuma saukeki laf

iya insha Allahu muna nan zuwa ni da iyalina duk ranar da kika haihu." Tace"To Allah ya kawo ku lafiya mungode." Ta kalli khalida da yayi gaba hankalinshi duk yayi gida tace"A gaishe min da Afnan da momynta." Yace."Zasuji insha Allahu.......Ta dauka zai m

usu rakiya sai taga ya tsaya bakin kofa yana fad'in To Alh sai munyi kenan a sauka gida lafiya nagode da ziyara insha Allah nima ina nan tafe." Khalifa yace."Wai kana nufin daga nan zaka tsaya."? Yace."Meye a ciki to akwai gajiya a tare dani ina so huta ne

." Khalifa yasha jinin jikinsa, ya kalli Wasila dake tsaye a kusa dashi yabi ya rike mata hannu gam kamar wacce zata gudu.....Yace." 'Kanwata ina fata baki mance abinda Dr Aliya ta fad'a miki ba ko." Wasila tayi jim!! Tana nazari sai kuma ta kalli Khalifan

jikinta a sanyaye ta daga kanta.' alamun bata mance ba........A ranar da akayi mata d'aurin mahaifa Dr Aliya ke shaida mata cewar dole ne ta nemi wata hanyar domin biyawa mijinta bukata mutukar ana so cikin jikinta ya zauna lafiya to banda yawan sex da ay

yuka masu tsauri, a lokacin da Aliya ke yi mata wannan jawabin sam bata d'aukeshi da mahimanci ba saboda tasan bata da aure lokacin, To da yake duk a gaban khalifa tayi jawabin yasa yanzu ya sake tuna mata kuma ta gane inda ya dosa, tabbas kuwa dole ne ta

yi taka tsantsar dan tayi bala'in sanin waye Amadu idan ya hauta ya dunga suburbud'arta mancewa yake da kowa da komai a lokacin shi dai burinshi kawai bukatarsa ta biya........Hannunta ya rike zugwi zugwi! ya nufi bedroom dinshi da ita, ya mai da 'kofar d'

akin ya rufe da key, sai sannan ya sakar mata hannu, jikinta babu kwari ta nemi gefan gado ta zauna, shi kuma ya nufi toilet domin watsa ruwa.

Ya fito daure da towel ya ganta zaune tana gyangyad'i Gyaran murya yay ta zabura da sauri ta bud'e idonta tana

kallonsa, gabanta ya fad'i ras!

ganinsa daure da guntun towel! da sauri ta haye bed din ta ja blanket ta rufe jikinta har fuskarta, ita kam ko me zaiyi ba zata bari ya hau kanta ba gani take idan ya sa mata wannan 'katuwar abar tashi zata iya haihuwar dol

e....Ganin razanar da tayi ya bashi mamaki sai kawai ya girgiza kanshi ya bude sif ya dauko jallabiya da gajeran wando yasa a jikinshi, kana ya nufi ke'bantaccen gurin da yake ibadarshi, kafin ya isa kira ya shigo wayarshi ya dauka yana dubawa Khalifa ne,

Yace."Dama dazu ina so nayi maka bayani to babu dama gaban Mutane.....Khalifa ya fad'a mishi sharud'an da Likita ta fad'a kan Wasilan ya cigaba da cewa ko za kayi kar ya wuce sau d'aya dan kar ka wahalar da yarinyar mutane kuma ka wahalar da d'an dake ciki

nta......Yace."Okey shine naji kuna magana da ita d'azu kuna wani 'boyewa."? Khalifa yace."Meye abin 'boyewa nifa zumud'in da naga kana yi ne yasa na tuna da maganar kai ma kanka ko ba'a fad'a ba ai ka d'aga 'kafa! A hasale yace."Kai kaga ki likita tace k

o bata ce dama ni banyi niyyar yin komai ba dan haka sai da safe." Kashe wayarsa yay ya ajeta yana jan tsaki ya nufi kan dadduma......Khalifa kam nashi 'bangaran dariya yasa dan ganin yanda lokaci 'kankani zuciyar abokin nashi ta hasala....Wasila kam tun t

ana rawar jikin ta daina dan bacci me dad'i ne ya dauketa cikin bargonshi mai cike da kamshin turarirrkanshi masu dad'in 'kamshi da kashe jiki.

Littafin na kudi ne!

Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah!

Whasap numbar

*07084653262*

*BINTA UMAR ABBALE*'Yr Bngr Sys

*66*

Nafila yayi raka biyu bayan ya idar da sallahr sai ya bude al'kur'ani mai girma ya karanta iya yanda ya sawwa'ka ya jima hannunsa a sama yana addua sannan ya rufe da fatihatulkitabi ya s

hafa a fuskarshi, a nutse ya mike ya nufi bed din ya xauna yana kallonta bacci take sosai kuma daga ni tana jin dadin baccin a hankali yaja bargon ya shiga ya kwanta kusa da ita tare da d'an jawota jikinshi ya d'ora hannunshi 'kasan mararta yana shafawa a

hankali a hankali bakinshi na motsawa da alama addua yake yi a nutse ya tofe musu jikinsu bakid'aya kana ya ja bargon sosai jikinsu ya rufe idanunsa yana adduar Allah ya taimakeshi bacci mai nauyi ya daukeshi, cikin ikon Allah kuwa baccin ya daukeshi, ku

ma baccin da ya jima baiyi Irinshi ba.

Wajejen karfe hud'u shaura na asubah ta farka da wata matsananciyar yunwa, jiki na kyarma tayi yunkurin mi'kewa, yay gaggawar rike ta idanunsa ya bude ke kyace dama ba bacci yake yi ba, Amadu bashi da nauyin bacci

ko kad'an, a hankali yace."Menene."? Shiru tayi tana mutsika idanunta, sai ya mi'ke zaune yana me cire bargon dake jikinsu ya sanya hannunsa guda a jikinta ya shafa wuyanta, babu alamun zazzabi a jikinta, Yace."Menene? ko zakiyi wani uzirin ne? muryarta na

rawa tace"Yunwa nakeji." Yace."Yunwa."? Daga kanta taji hawaye na kokarin zubo mata, Yace."Dama baki ci abinci ba kika kwanta."? "Naci dama duk dare ina tashi

naci abinci." Ya shiga girgiza kanshi a hankali ya mike ya sauka daga bed din ya fita daga dakin

Kicin ya nufa yayi dube duben shi babu abinci sai kawai ya jona kettle ya dora ruwan tea yana tsaye yayi ya juye mata a cup ya nufi dakin dashi, lokacin ta fito daga toilet daure da alwala dan an soma kiran sallah." Ya aje tae din kam bedside yana fad'

in "Ga tea nan babu abinci a kicin din wallahi." Zumbura bakinta tayi ita me zatayi da wani tea banda ya sata jin wata yunwar, Fita tayi daga dakin Yabi bayanta kicin ta nufa, ya tsaya bakin kofar kicin yana fad'in "Ki koma ki kwanta bari na tashi hajja s

ai ta sarrafa miki wani abun." Girgiza kanta tayi tace"Kawai tana baccinta sai a tasheta tayi girki nima zan iya." Shiru yay yana kallonta tana kunna gass cocar, Shi da kansa yayi alkawarin daukar dukanin laluranta baiyi tsammanin harda shiga kicin ba, a l

okacin da suke tare a can baya bai santa da wannan cin abincin ba yanzu dai yafi tunanin cikin da take dauke dashi ne ya sanya ta, kicin din ya shiga ya kar'be tukunyar hannunta wai zai d'ora mata abincin......Tausayi ya bata ta kar'bi tukunyar taje ta zub

a ruwa ta tazo ta dora tukunyar gefanta ta bude taga lafiyayyar miya wacce taji nama zu'ku zu'ku.....Sai kawai ta bud'e sto ta dauko supargetti guda d'aya, yay daurin kar'bar taliyar a hannunta, ta rike tana girgiza mishi kai tace"Ka barshi zan dafa babu w

uya fa." Ya d'an tsira mata idanunsa itama shi take kallo tana sake jin wani irin yanayi a jikinta gaskiya ta lura ya mato akan sonta, da girmanshi da komai ya dinga biye mata da dukanin abinda take so.....Yace."Kin tabbata zaki iya." Daga kanta tayi yace

."Okey bari nayi wanka da alwala na wuce masjid.'" ya wuce ta bishi da kallo tausayi tausayinsa take ji a cikin ranta.

Tana tsaye taliyar tayi ta tsaneta kana ta juye cikin fulas ta dauka ta nufi daki dashi, lokacin har yayi wanka ya sanja jallabiya ha

nnunsa rike da cazbaha, sai kamshi yake ta matsa mishi hanya shi kuma ya fita ba tare da wani yace da dan uwanshi komai ba.

Kicin din ta koma ta dauko plate sannan ta samu wani abu ta zuba miyar a ciki ta dawo dakin ta zauna kasan kafet a nutse ta zuba

abincin ta soma ci sai da taci ta koshi sannan tayi sallah ta koma ta kwanta, bacci na fizgarta taji shigowarshi.......Ta bud'e idonta a hankali tana kallonshi lokacin da yake kokarin karasowa kusa da ita......Zama yayi gefanta a nutse yace."Tashi zamuyi

magana." Ganin babu wasa a tare dashi yasa ta mike xaune tana wasa da hannunta.....Cikin kulawa ya kalleta yace"babu gaisuwa ko."? Ta dan kalleshi da gefan ido sai taga ya tsirawa jikinta ido, kanta ta sunkuyar a hankali tace "Ina kwana." Ya amsa da sakakk

iyar fuska kana yace."Ya kwanan boy." Shiru tayi yace."Kamata yayi ma kafin mu fara magana na fara gaisawa dashi." ba tace masa komai ba, dan janyota jikinsa yana laluben jikinta, hannunsa ya d'ora saman mararta yana shafawa, ta dinga jin hucin numfashin

sa a fuskarta, rintse ido tayi gabanta na faduwa tsigar jikinta na tashi, ya d'ora bakinshi saman goshinta tare da fad'in "Allah yayi miki albarka." Ta bude idanunta dake rufe tana kallonshi, mikar da ita yayi zaune yace"Yanzu hankalina ya kwanta na dub

a yarona yana da kyau ma muje kuga Dr insha Allah." Ba tace komai ba tana dai kokarin gyara rigarta, sai da ya tabbatar ta samu nutsuwa kana ya kalleta a nitse yace."Wane guri kika tsaya a karatun ki na al'kur'ani da hadisai nasan dai kinje isilamiyya ko.

'? Taji gabanta ya fad'i! ta kalleshi idanunta na kokarin kawo ruwa, ina suka ga gatan da

zasuyi karatu....Shiru tayi masa tana wasa da yatsun hannunta, Yace."Koda yake dai yanzu ku kin fad'a min ga inda kika tsaya bai da amfani tunda dai ba tilawa kikeyi

ba, yanzu ki shirya ko ince ku shirya keda kanwarki insha Allahu kullum da asubah zamu dinga zaman karatu dani daku zamu fara tun daga fatiha da izinin Allah zamu sauke al'kur'ani mai girma mutukar kun bani had'in kai! Idan kin san ba'ki kin iya karatun

al'kurani da sauran litattafan addini insha Allahu karatun nasara (boko) ba zai miki wuya ba zan d'anko muku mai muku lesson kafin ki haihu sai ku koma makaranta ko bakya so."? Yafada yana kallonta cike da kulawa......Hawaye ta share murya na rawa tace"In

a so mungode." Yace." Kin kammala secondary skul ko." ? Shiru tayi kunya duk ta isheta, ya sake maimaita tambayarshi, da kyar tace "Tunda muka fad'i jarrabawa muka daina zuwa." Yace."Okey duk ba wani abun bane insha Allah zakiyi karatu mutukar kin mai da h

ankalin ki ni kuma zan tsaya miki da yardar Allah." Hawaye taji sun zubo mata a fuskarta, tace"Mungode Allah ya saka da alkairi." Sai ta fashe da kuka harda shashsheka, rungumeta yayi sosai yana rarrashinta tare da shafa kanta, tayi luf a jikinshi tana sau

ke ajiyar zuciya.....Ya dago ta daga jikinshi yana goge hawayen fuskarata yace."Ki rabu da wannan 'kawar taki wacece sunana? bata da kirki duk wani lalacewa da rayuwarku tayi da ita da kuma rashin gata wanda baku dashi amma insha Allahu nine zan zama gatan

ku in dai zaki zauna dani da tsarkakkiyar zuciya abinda ya faru a baya ya wuce a gurina na yafe miki insha Allah Allah ya yafe mana gabad'aya." Hannunsa cikin nata tace"Dama tuntuni mun rabu da Camas! nagane ita ke zugani ina yin wasu abubuwan marasa ky

au tunda abun nan ya sameni ta gujeni ta gudu da kudina kusan miliyan biyar har yanzu ban san ina take ba."

Yace."Duk abinda kikace ta aikata miki zata iya domin nima na nemi taimako a gurinta lokacin da muke neman ku kafin kuje gurin mai allo, yarinya

r ta'ki ta bani cikakken bayani 'karshe ma sai ta daina d'aga waya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login