Showing 108001 words to 111000 words out of 176422 words

Chapter 37 - YAR BANGAR SIYASA COMPLETE

to bayan rabuwarsu

ya mayar da ita ne har ta samu cikin ko kuma bayan ta fito daga gidan cikin

ya bayyana ? babu me bashi amsa sai su ya sauke ajiyar zuciya lokacin da ya karasa inda yake a nutse yace."Alhaji mu shiga ciki sai muyi maganar." Ga yanayin yanda mai allo ke masa

magana yasa ya fahimci akwai damuwa, jikinsa babu kuzari ya juya yana tafiya me allo ya bi bayanshi.

Mai allo ya zauna kan tabarma yana kallon Ahamdu A nutse ya soma magana kamar haka

"Yau shekaru takwas kenan rabon da Wasila da 'yar uwarta Rashida su

tako 'kafarsu garinan! shiyasa nayi mamaki mutuka! a lokacin da kuka zo min da wannan maganar, amma kuma banyi muku musu ba saboda nasan hakan zata iya kasancewa tunda muma kullum cikin tunanin zuwansu muke nasan duk tsiya yarinyar bata da wasu iyaye sa

i mu, kuma nasan dole watarana zata kawo kanta inda muke duk kuwa da tsananin 'kiyayyar da suke mana ita da 'yar uwarta......Ni da 'Yan uwana da sauran dangi kullum cikin saurare muke da kallon hanya muna jiran tsammanin zuwansu garinan, tun bayan rabuw

ar auranka da ita muka yanke shawara kancewa mun dauke hannunmu da kansu gabakid'aya wanda har 'Dan uwana Habibu da ya fusata yace. Duk ranar da suka shigo garinan to sai ya koresu ni ne na hanashi nace mutukar sunzo inda muke to zamu kar'be su hannu biyu

amma idan basu nemi in da muke ba to zamu kyalesu da halinsu da kuma mahaifiyarsu, to a gaskiya ni nafi gazgata zaton cewar Yaran nan sun bi bayan mahaifiyarsu can garinsu." Mai allo ya 'karashe maganarshi yana so ya tabbatar musu da gaskiyar lamari.....

.Khalifa ne kawai ya iya magana Yace. "Allah shi gafarta malam ko zamu iya sanin garin su mahaifiyar tasu."? Mai allo yayi shiru yana d'an tunani kafin yace." Wallahi sunan garin ya kwanta min a raina, tun da kasan can d'in ba nan ne inda cibiyar mahaifin

ta yake ba, shi kanshi 'kanina Yahuza a hannun Kawunta ya aureta amma dai na ta'ba ji sau d'aya 'kanin nawa ya ambaci sunan garin har yace watarana zai daukeni ya kaini mu gaisa da danginta to kuma sai Allah ya dauki abinshi.

Khalifa da gogan naku bakin

su ya mutu murus! Saboda dukaninsu sun rasa tudun dafawa sun ma rasa wane tunani zasuyi shin yanzu ina zasu samu yaran nan? Su dun tunaninsu babu inda suka dashi sai nan dan suna tunanin itama Uwanin a nan take ashe ba haka bane! Gashi gurin wanda suke tun

anin samun cikkaken bayani shima yace bai ma sannan sunan garin da suka nufa ba........Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un!

Littafin na kudi ne.....!

Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar

*07

084653262*

*BINTA UMAR ABBALE*

[14/08, 12:04 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys

*58*

Cike da farin ciki da walwala ya shiga gidan nashi yana kwalawa matarshi kira..........Kuluwa ta fito daga wani guri wanda alamu suka nuna cewar madafi ne (khicin) hannunt

a da wata katuwar mara da alama kwasar towo take, tace"Malam ganin nan Allah yasa lafiya irin wannan kira hak.....Kafin ta rufe bakinta sai idanunta ya sauka kansu Uwani da 'yayanta, lokacin 'kan'kani ta kirne fuska tana fad'in "A'a yau kuma

Uwani ce a gar

in."? Uwani dasu Wasila duk sunga sauyin fuska a tare da ita, lokacin da take maganar da alama dai batayi maraba da zuwan su garin ba.......Kawu Madu yana washe hakoransa yace." Wallahi kau nima nayi mamaki sosai dan baki ji dadin da nakeji ba, abinci zamu

ci dasu malam tsalha na taso domun in shigo dasu gidan." Kuluwa tace"To sannunku da zuwa ku shigo ciki." Kawu Madu yace."Uwani ku shiga ciki a baku abinci ku huta ai da alama ma kun kwaso rana." Uwani tace"Aikuwa wallahi munsha zaman mota da gajiya." Kawu

Madu ya juya ya fita yana fad'in "Bari nasa Ayuba yaje can cikin kasuwa ya siyo muku ruwan sanyi."

Uwani da Rashida suka shiga daukan jakkunansu dake yashe a tsakar gidan suka nufi dakin Kuluwa, suna shiga katuwar rumfa ce sai dai babu shinfida a cikint

a sai guntattakin tabarmi da ledoji ko ina kaca kaci da kwari ka 'kananin kyankyasai ga wani uban 'kuda da yake tashi a rumfar da wani kafirin zarnin fitsarin yara......Tun lokacin da suka shiga rumfar Wasila ke yatsine ya tsinen fuska zuciya sai masifar t

ashi takeyi aikuwa kafin tayi wani yun'kuri amai ya kece mata! a guje! tayi waje ta nemi bakin rariya ta tsuguna ta dinga kelayashi tana kwallah......Rashida ce tsaye a kanta tana mata sannu duk ta shiga damuwa. Bayan ta gama aman ta bata ruwa ta wanke bak

inta da fuskarta kana ta mike jiri na d'ibarta......Rashida ta rike hannunta wai su koma cikin d'akin girgiza kanta tayi da kyar tace"Rashida rabu dani don Allah zuciya tashi takeyi idan na koma gurin nan zan iya yin wani aman." Aikuwa karaf a kunnan Kuluw

a ta rike baki tana fad'in "Ke ja'ira yarinyar me kike nufi? daga zuwa zaki fara yiwa mutane sanabe da iyayi kina nufin kazama ce ni kome." Rashida tayi saurin girgiza kanta tana fad'in "Ba haka take nufi ba baba." Kuluwa tace"To me take nufi da har zata s

higa dakina ta rugu waje da gudu tana kwara amai." Rashida tace "bata da lafiya ne dama tun a mota cikin ta ke ciwo." Kuluwa ta girgiza kanta tana fad'in "Maji ma gani dai idan tusa zata hura wuta, kome kuke tafe dashi dai-dai nake daku to kaji."! Tana gam

a maganar ta ta shige madafi domin cigaba da aikinta.

Uwani na cikin dakin abin duniya yayi mata yawa, tunani takeyi yanzu wace irin rayuwa zasuyi cikin gidanan! tun da can baya tasan Kuluwa macace mara mutunci da muguwar kaxanta sam bata so kowa yazo i

nda take tabi ta asirce Kawu Madu sai abinda tace yayi yake ji shima wani lokacin tsoranta yake yi, Ta dinga tunanin irin wuyar da zasu sha ita da 'yayanta a gidan dan ga dukanin alamu Kuluwa ba tayi maraba da zuwansu ba, tunani take ko su tafi gidan Kawu

Isa ne? sai ta tuno shi kuma ai bai da gidan kanshi haya yake kuma daki guda ne suke gamutsuwa dashi da matarshi da 'yayanshi.....Iya mai waina kuma ba ita kadai bace a gidanta tana da kishiyoyi kuma babu wadataccen gurin zama, dole dai gidan Kawu Madu din

shine gurin zamansu, Kwallace ta taru a kwarmin idanunta tayi saurin gogewa, lokaci guda duniya ta juya musu baya, sun fara d'and'anar jin dadin rayuwa kuma sun koma gidan jiya............Sai a lokacin nadama mara amfani ta kamata ta dinga tunanin abubuwa

n da suka dinga faruwa a baya da irin kud'ad'en da 'yarta ta rike da samun nasarar auran Ahamdu tayi, Yanzu ne ta gane auran Ahamdu da 'yarta shine rufin asirinsu tasan da Wasilan na gidanshi har yanzu da tuni basu shiga wannan gararanbar ba.

Kuluwa ta sh

igo dakin hannunta rike da wata katuwar langa tana kallon Uwani tace"Naga kamar kema kina cikin alhini da damuwa to Allah yasa dai ba abin kunya kukayi a can ba kuka gudo nan dan naga alamun ciki a tattare da waccan 'yar taki."

Uwani ta kalleta ranta ya

'baci da maganarta amma saboda sanin halinta yasa tace"Eh kuluwa ki daina shakka ko kokwanto Wasila na da ciki amma kuma da Ubanshi."

Kuluwa ta ta'be bakinta tana fad'in "To yanzu naji zance Allah ya rabasu lafiya sai ki kira su kuci abinci gashinan ba

bu yawa dai aci da hakuri tunda ban san da zuwanku ba." Uwani tace"To mungode." Kuluwa ta fita daga dakin, tana gyara daurin zaninta wanda yayi da'kal! da'kal da daud'a!

Uwani ta le'ko tana kiransu Wasila dake zaune jikin bishiyar darbejiya dake gidan..

.......Rashida da kyar ta lalla'bata suka koma dakin....suna shiga ta fito da sauri tana fad'in "Rashida ba zan iya ba wallahi mutuwa zanyi zuciyata tashi takeyi." Karaf a kunnan Kuluwa cikin fusata tace"Ke! buhun ubanki nace! Buhun ubanki kaji min shegiya

r yarinya ciki haukane da zaki zo min gida kina min iskanci! har ki dinga cewa zuciyarki tashi takeyi to bari malam ya shigo wallahi kinji na rantse ba zaki zauna min a gida ni ba'a kawo min iskanci ehe! dama ai baku bane tilashin mu ita Uwanin itace tilas

dinmu dan haka sai ku koma inda kuka fito abin arziki baya zama na tsiya." Takarashe maganar tana kumfar baki kai daka ganinta a fusace take! Uwani ta fito daga daki tana bata hakuri saboda tasan halin ta zata iya cewa su Wasilan baza su zauna a gidan ba

kamar yanda ta fad'a, Hakuri take bata tana karyar dai muryarta sai rawa take! Kuluwa ta cigaba da aikinta tana sababi! da zagin Wasila

Uwani ta dauko langar abinci ta dire a gabansu tana fad'in " Ku kiyaye da wannan matar idan kuna son zaman lafiya b

ana son abinda kikeyi Wasila kinga bamu da gatan da yafi nan, Kuluwa macace mara hakuri zata iya sa Kawu yace ku bar mishi gida kamar yanda ta fad'a saboda haka duk abinda zakiji na tashin zuciya ki dinga daurewa kina hakuri haka take muguwar kazama ce tu

n tana da kuruciyarta gashi har girmanta......Wasila bata iya magana ba rashida ce mai magana tace"Gaskiya Uwani gidan nan baiyi wallahi duba fa ki gani ko ina kazanta da kashin dabbobi dubi bandaki babu kofa sai buhu kiji warin masai dake tasowa har nan k

awai mu zamu tafi Garko ke kiyi zamanki nan tunda kece tasu."

Uwani ta marairaice fuskarta muryarta na rawa tace"Rashida kin san yanda nake son ku kuwa ? bana so kuyi nesa dani shiyasa na'ki aure na 'kare rayuwata tare daku, ina 'kaunarku saboda nasan b

ani da kowa sama daku, Uwata ta mutu Ubana ya mutu mijina ya mutu sai ku kawai nake kallo naji dadi idan kuka tafi Garko kuka barni wace irin rayuwa kuke tunanin zanyi a cikin garin nan."!?

Tausayin mahaifiyar tasu ne ya kama su, sai suka hau goge hawa

ye, suna adduar Allah ya kawo musu dauki da gaggawa amma hak'ikanin gaskiya mahaifiyar tasu tasha wuyar rayuwa ta kuma yi wahala dasu bai kamata su guje mata ba,

Zama tayi kusa dasu tana bud'e langar abincin aikuwa sai wani irin towon dawa ba'ki'kikiri

n yayi musu sallama! towon sai shaining yake ga wata uwar miya kamar fitsarin jaka, sai wake guda guda a cikin miyar tana ta warin daddawa......A guje Wasila ta mike ta nufi bakin rariya ta dinga kakarin amai tana zubar da kwalla! Kuluwa tayi azamar fitowa

daga kicin da ludayi a hannunta....Wannan karon Uwani da kanta taje ta rirrik'e 'yar

tata tana mata sannu ita kuwa sai rike ciki take tana mur'kususu da kiran sunan Allah! Kuluwa ta dinga kallonsu bakin cikin duniya kamar ya kasheta 'Kwafa tayi ta koma k

icin din! Yau ba gobe ba zasu bar mata gidanta dan bata ciki da iskanci da wulakanci......Kawu Madu ya shigo gidan yana sa'be babbar riga sai kawai ya gansu cirko cirko Uwani da Rashida kan Wasila dake durkushe tana kakari......Yace."A'a Uwani meke faruwa

ne Me yasa me ta take amai haka."? Kafin Uwani tace wani abu Kuluwa tayi zuruf ta fito daga kicin fuskarta a murtuke tace" 'Kyankyamina takeyi shine take amai tunda suka shigo gidanan basu shiga dakina ba can bakin bishiya suka zauna saboda suna kyankyamin

a saboda haka yau ba gobe ba zasu bar min gidana dan wallahi ba zan dauki wannan iskancin ba." A take Kawu Madu ya sha kunnu yana kallonsu rai a bace yace."Ashe baku da tarbiya dama? matar tawa kuke 'kyankyami!? to shikkenan dama ai baku ne tilas dina ba M

ahaifitarku ce saboda haka zaku bar min gidana tunda baku da mutunci." Uwani ta shiga share hawaye tana fad'in "Kawu ba haka bane wallahi yarinyar nan nada ciki mai laulayi yana bata wuya dama tun a mota take amai har yanzu ba wai suna 'kyankyamin Kuluwa b

ane."

Yace."Uwani."! ta amsa yace."Shin yaushe kikayi wa yarinyar ki aure babu labari gashi nace tana da ciki."! Kuluwa tace"Nifa malam ban yarda ba wallahi wannan yarinya cikin shege tayi shine suka kwaso jiki suka gudo nan sabida gudun abin kunya dan

haka wallahi ba'a gidan nan ba idan kuma kace tilas sai sun zauna to ni zan fice na baku guri."

Hankalin Kawu Madu ya tashi, Yace."A'a ba za'ayi hakaba Kuluwa ai duk wannan magana ma bata taso ba, ke Uwani zo ki zauna kiyi min bayanin abinda ke faruwa."

Uwani ta bishi kan tabarma suka zauna tare Kuluwa ta 'karaso gurin hannunta rike da ludayi ta zauna kujera 'yar tsugo tana fad'in "Eh ai gwara muji bayanin komai domin mu samu kwanciyar hankali." Uwani ta share hawaye a hankali ta soma warwarewa masa

abubuwan da suka faru da rayuwarta ita da 'yayanta komai bata rage masa ba sai da ta fad'a mishi......Kuluwa tace"Duniya kenan yanzu ke Uwani bakiji kunya ba, wato lokacin da kuka samu kudi kuka samu dad'in duniya baki tuna damu ba sai da wahala ta taso ki

sannan zaki tuna damu ki kwaso jiki ra'be ra'be da 'yaya kizo ki d'ora mana nauyi to ba zata ta sa'bu ba! Mu ba zamu dauki nauyin ki kuma mu d'auki nauyin 'yayanko ba, Dan haka gobe gobe yaran nan zasu bar gidanan suje can dangin mahaifinsu tunda suna ray

e, kema abinda yasa ba zamu kore ki ba saboda mun san ko kinje can gidan Kawunki ba zai kar'be ki ba saboda haka ke kad'ai zamu ri'ke saboda kece tamu."

Kawu Madu yace."Kwarai kuwa Kuluwa wannan magana taki gaskiya ce, Yaran nan baxa su zauna mana a gida

ba sabida bamu da hakki a kansu dan haka kamar yanda kika fada hakane kwana guda zasuyi su bar mana gida suje can cibiyarsu.........Uwani ta dinga kuka tana fad'in "Haba Kawu ku duba al'amarin fa kada kuyi min haka bani da kowa sai 'yayana bani da uwa da u

ba bani da miji sai 'yayana su nake gani naji sanyi a raina." Kuluwa tace"To ai tunda hukuncin da muka yanke bai miki ba to sai ki bi 'yayan naki haba! wannan 'kulafucin son 'yaya dame yayi kama.'' Ta mike tana jan tsaki ta shiga dakinta.....Kawu Madu ma

ya mike yana fad'in "Na fad'a miki Uwani na yanke hukunci Kuluwa ta yanke hukunci saboda haka shawara ta rage gareki." Ya buge babbar rigarsa ya 'kara gaba.

Wasila da Rashida kam! basu ciwo ba dalili dama sunfi son su tafi can garkon shiyasa sukaji dad

in hukuncin da Kawu madu ya yanke a kansu amma basu nunawa mahaifiyar tasu ba, sai suka shiga kwantar mata da hankali da fad'in ko sun tafi insha Allahu zasu dinga zuwa a kai akai suna dubata.....Uwani dai jinsu kawai takeyi abin duniya ya taru yayi mata y

awa bata ta'ba nadamar rayuwa ba irin yau.

Kuluwa ta dinga shige da fice a tsakar gidan tana sakin 'ba'kaken maganganu wanda ya sanya jikin Uwani yi sanyi taji a zuciyarta gwara kawai su Wasila su bar gidan dan ba zata iya jurar rashin mutuncin kulawa t

ana aibata mata yara da kiransu karuwai watarana tana ganin zata iya mayar mata da martani kan maganar da takeyi, ta dinga jin wani irin d'aci! da bakin ciki a raina ashe haka abun yake da ciwo a duk sanda aka danganta d'anka da wannan suna (karuwai) gask

iya ta gode Allah da ya bata 'yaya masu hankali da hange nesa tasan da bada hakan ba da tuni sunanan da kuluwa ke kiransu dashi ya tabbata tunda ita da kanta ta dinga turasu karuwancin, tagode Allah da yasa wannan cikin dake jikin Wasila ta sameshi ta hany

ar halak ba haram ba.

Kuluwa na ganin irin tsarabar da suka kawo sai ta hau washe bakinta ta dauki turmin atamfofi irin na leda guda biyu tace wannan ni zan d'inka in sa a jikina wannan yadin kuma na malam ne, sauran kuma Iya mai waina da Tabawa su ka

safta a tsakaninsu." Su dai kallonta kawai sukeyi duk tabi ta kwashe kayan ta shige dakinta dasu sai murna takeyi ko Kawun ma bata nunawa ba.

Sai dare suka samu suka sanya abinci a cikinsu shima abincin Inna Tabawa ce ta kawo musu cikin katuwar Samira

shinkfa da wake ne da manya da wani uban yaji da yaji gishiri da citta! haka suka cuccusa dan gwarashi kan narkeken towon dawan da Kuluwa ta kawo musu, Wasila dai kad'an taci tasha maganinta ta nemi gefenan tabarma ta kwanta tana mai da nuffashin wahala...

..........Duhu sosai gidan babu wadatacciyar fitala sauro da kwari ka sukayi sallama! Wasila ta gigice ta dinga soshe soshe kukan sauro duk ya cika mata kunne! Uwani tace "Ku tashi mu koma daki mu kwanta kunga mutanan gidan sun shige sai mu kadai a tsakar

gida ga sauro." Rashida tace "Yanzu cikin wannan kazantar zamu mu kwanta ga yara nasan suna fitsarin kwance." Uwani tace"To ya zakuyi ai da zama cikin sauron nan gwara cikin rumfar." Wasila tace"Uwani ku shiga ku ku barni anan Rashida ki dauko min zanin a

tamfa cikin kayanmu in rufe jikina." Uwani tace"Akwai fa damuwa kwanciyar ki anan." Tagoge kwallah tace"Uwani nan yafi min kan in shiga dakin nan inzo ina kakarin amai da daddare d'an abincin da naci ya dawo, kuma wannan matar tazo tana miki masifa."

A

sanyaye Uwani tace"Shikkenan ai." Ta mike a hankali ta shiga dakin rashida tabi bayanta......Nan su kaga yara birjik a rumfar ko wanne ya wargaje kafafunshi wasu sun soma sakin fitsari abinsu sai barci suke.....Uwani ta ra'ba can wata kusurwa ta karkad'e w

ani buhu ta shimfida ita kuma rashida ta nufi dakin Kuluwa dan jakkunan kayan nasu na cikin dakin........Nan ta tarar da Kuluwa ta bude musu kaya sai bunkice takeyi musu, tana ganin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login