Showing 144001 words to 147000 words out of 176422 words

Chapter 49 - YAR BANGAR SIYASA COMPLETE

/>
ri guda gudun azo a haifi dan da bashi da ido tasan ita dashi duk basu da hakuri a wannan fagen, gashi kuma bata so Inna hajara ta tafi tilas ne ta kama kanta ko ya shigo ta daina sakar masa fuska, wannan ce sha'awar data yankewa kanta.

Hakance kuwa ta

kasance kwata kwata Amadu ya daina ganin walwalarta ko ya shiga dakin ta dinga dauke dauken kai kenan idan ya zauna kusa da ita sai ta sauya guri idan ya dame ta tasa masa kuka tace dole sai ya bar dakin.....Abun da takeyi ya dinga bashi mamaki sosai ya

soma jin haushinta yana dai daurewa ne, kawai baya so ya nuna mata fushinsa, ya kuma lura da yanda Inna Hajara ke zurga zurga a dakin duk sanda ta ganshi ya shiga da safe, dama da safe kawai yake

shiga kafin ya fita da daddare baya dawowa da wuri kafin

ya dawo sunyi bacci sai ya wuce dakinsa kawai, shi ba yaro bane tsaf ya fahimci akwai saka hannun Inna hajaran gurin abinda Wasilan ke masa duk sai yaji zaman matar a gidanshi ya isheshi tunda ba abun arziki take sa'kawa ba.

*****

Yau kwanansu ashirin

da shida kenan har ta soma sallah dan jinin biki da wuri ya dauke mata, tana kwance tana bacci dama 'ka'ida ne idan tayi wanka ta karya sai ta kwanta tayi bacci dan cikin dare ba sosai takeyi ba baby zahra na yawan tashi shan nono.........Cikin shirin fi

ta ya fito daga dakinshi yana sanye da shadda fara 'kal da ita wacce kana ganinta kasan me tsada ce d'inki hannu ne na 'bakin zare wuya da hannuwa sai yay amfani da 'bakar Hula (dara) 'yar gasken mai gashi gashi a jikinta agogon dake hannunsa na dama shima

'baki ne na fatar damisa takalman kafarshi masu gidan ya tsa suma ba'kake sosai yayi kyau tamkar wani sauri dan shekara ashirin da takwas......Suka gaisa dasu Hajja da Inna hajara ya nufi dakin nata, Inna hajara idanunta a kansa tana so tagani idan taga

ya jima bai fito ba tabi bayanshi.

Yana shiga dakin ya tarar da ita tana bacci tana sanye da wani material roba roba dinki riga da siket ne dama can kayan sun matseta ballanta yanzu da ta sake cika da cikowa irin ta haihuwa......A hankali ya isa bakin g

adon ya d'an tsaya a kanta yana 'kare mata kallo.....Cikin baccinta ta dinga jin 'kamshin turaransa, bud'e idanunta tayi sai taga inuwarshi tayi saurin daga kanta tana kallonshi.

Mi'kewa tayi zaune tana mutsika idanunta, a hankali tace"Ina kwana."? Y

a amsa babu yabo babu fallasa......mikewa tsaye tayi tana d'an jan rigarta da duk ta tattare tayi sama, ya bita da kallo tana kokarin wuce shi ya tari gabanta.

Sai ta 'bata fuska tana kallonshi......Shima fuska a 'bace yace."Me yasa kika sauya halinki? wa

ne dalili ne ya sanya duk sanda na shigo dakin nan kike 'bata rai idan na zauna kusa dake ki sanja guri idan na rike hannuki ki saka min kuka meke faruwa dakene."?

Murya a sanyaye tace"Babu komai." Ya had'e ranshi sosai yace."Bana son 'karya ki fad'a mi

n dalilin da ya sanya kike gudana ko zugaki akeyi ne."? Tayi saurin kallonshi......Yace." 'Kwarai kuwa ai da ba haka kike ba cikin 'yan kwanakin nan kika sauya d'abi'u dole ne nayi zargin ko zugaki ake."

Sai ta tsargu! ta dinga kallonsa tana son tayi ma

gana! Sam bata so ya zargi Innarta dan tana so ya cigaba da ganin mutuncinta kamar yanda yake gani ba zata so ya gane cewar Inna Hajara ce ke zugata ba........Tace"Ni babu wanda yake zugani kawai dai ina ganin kamar be dace ba ace muna had'uwa a d'aki ni d

a kai saboda banyi ar'bain ba."

Ya dinga kallonta yana mamakin maganarta akwai kuruciya da rashin wayo a tare da ita, wannan maganar da takeyi sam bata da tushe ballanta makama kuma ba tunaninta bane, yasan innarta ce ke zugata.

A d'an kausashe! yace

." A cikin wane littafin addini ki kaji ance dan mace ta haihu shikkenan ita da mijinta sai ranar da tayi ar'bain? wannan magana da ki keyi irin ta jahilai ce ba'ace dan kin haihu shikkenn sai ki dinga gudun mijinki ba! Ni ba yaro bane na kuma gane abinda

kike gudu shiyasa nace wannan abinda ki keyi ba tunaninki bane zugaki akeyi kuma duk me zugaki zata kaiki ta baro ne Ko yau idan nayi ra'ayi zan iya shigowa d'akin nan na kwana tare dake dama ba'ace lallai ki kwana da wata ba ni zan iya kula dake da yarin

yata." Yanda yake maganar ne yasa ta gane ranshi a 'bace yake sosai to itama ranta ya 'baci sosai jin yana 'kokarin cin fuskar Innarta a gabanta zuwa yanzu ta gane ya gane cewar Inna hajara ce ke zugata.

Murya na rawa tace"Inna Hajara kake kira da jahila

kada ka manta fa a matsayin uwa take a gurina tunda kanwar mahaifina ce." Idanunsa tsaye a kanta yace."Ni da bakina kinji na zageta ko na ambaci sunanta nace da ita jahila." ? sunkuyar da kanta tayi tana kokarin mayar da kwallar dake kokarin zubo mata Tac

e."Ai ka gane itace shiyasa kake kokarin fad'a mata ba'kar magana a gabana to meye laifinta ai gyara kayan ka baya hana sauke mu raba." Murmushin takaici ne a fuskarsa ya bud'e baki kenan zaiyi magana zuruf Inna Hajar

a ta turo 'kofar d'akin ta shigo ka

fad'arta sa'be da baby zahra tana fad'in ''Kina ina ne Wasila zo maza kar'beta ki bata nono kada ta fara wannan kukan nata." Duk suka juya suna kallonta tana tsaye a bakin 'kofar shigowa..........Jikinta ne kuma yayi sanyi ganinsu kamar suna cikin 'bacin r

ai dan ta lura da Wasilan ma kamar kuka take, sai tayi maza ta juya zata futa tana fad'in "A'a Alaji ashe baka fito ba." Yay saurin 'karasawa inda take yana fad'in "Yanzu zan fito Inna bani ita mu gaisa." Ya mi'ka hannunsa ya 'karbi yarinyarsa Inna ta bud'

e 'kofar dakin ta fice da sauri duk kunya ta isheta.....Hannunsa ri'ke da babynsa suka 'karasa inda take tsaye tana shashshekar kuka

Littafin na kudi ne!

Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap num

bar

07084653262

*BINTA UMAR ABBALE*

*BINTA UMAR ABBALE*alliya:

[8/24, 9:55 AM] .: 'Yr Bngr Sys

*75*

_Assalamu alaikum barkan ku da safiya da fatan kun tashi lafiya ya gida ya yara? madallah Jiya na fita anguwa tun safe ban samu nayi typing ba

sai bayan na fita ne na kawo muku uzirina afuwa

👏🏻

da yawa daga cikin ku nasan zasu dauka wani abu daban to nasan wad'anda suka san wacece binta baza su dauki rashin yin typing dina da wata manufa ba, amana d'aya ce kamar yanda na d'auki alkawari kuma na

karbi kudin ku #600 domin ku dinga samun update na 'yar banga sau biyu a rana, to ku sani a cikin ku akwai wad'anda nayi wa uziri suna da yawa, kuma a rayuwa dole sai kayiwa d'an uwanka uziri mutum ba kullum yake samun abinda yake so ba, tinda na fara typ

ing na 'yar banga ban tsaya ba ko hutun sallah ban tafi ba kullum sau biyu nake har 'yan normal gruop suna surutun hakan, ban ta'ba tsallake kwana biyu banyi typing ba inayi iya bakin kokarina duk domin na sauke nauyin dake kaina, Ni ina kokarin rike amana

rku amma kuma wasu daga cikinku suna cin amanata to wannan be dameni ba saboda nasan kansu sukewa, watarana zan tashi bani da chaji watarana zan tashi bani da lafiya ko yarona, kunga typing ba zai yiwu ba, dole sai da nutsuwa nasan dai wad'anda suka san wa

cece binta zasu bada shaida a kanta ban kar'bi kudinku dan nayi wasa da hankalinku ba duniya dole sai kayiwa dan uwanka uziri, saboda haka dik sanda aka ga banyi typing ba to a fara tambayar lafiya tukkuna kafin aji bayani na, ku kar'bi uzirina kamar yand

a nake kar'bar uzirinku...................Assalamu alaikum

🙋🏻

‍♀



_

Yana isa inda take tsaye sai ya rike hannunta ya jata suka zauna kan gado, baby Zahra ya d'ora mata a cinyarta cikin murya mai taushi yace."Ki bata nono kinga tana kuka bana so nag

a momyna na zubar da hawaye."

Ma'kale kafad'a tayi tana goge fuskarta cikin shagwaba tace"Uhm!Uhum! wato momyka ko? to nima ai momyna ka 'batawa rai." Ya rike kafad'arta yana dan sansana wuyanta a hankali yace."Ayi min afuwa nima Inna Hajara mamana ce kum

a kema ai kin san duk abinda na fad'a akanta hakane yanzu gashi data shigo kin tabbatar da maganata ko."? Shuru tayi masa kunyarsa takeji sosai.....Murmushi yay yana dan daga mata girarshi a hankali yace."Ai naga kin fara sallah saboda haka yau dakin nan

zan kwana dan kwana biyun nan kokari da hakuri kawai nakeyi sha'awarki zata kasheni." Cikin wani irin voice ya'karashe maganar.

Kallonsa takeyi tana d'an zum'bura bakinta tace"Ni wallahi A'a so kake ka sake farke gurin bayan kasan sai da aka yanka ni." Y

a wani marairaice fuskarsa yana mata shu'umin kallo yace."Ai naji Likitarki tace gurin ya had'e ranar da mukaje asibiti."

Hawaye ta share tana sake zu'baro baki gaba tace"Eh duk da ya had'e ai amma tace sai anyi wata uku sannan wani abu zai faru." Jikinta

ya sake shigewa ya d'ora ha'barshi kan kafad'arta tare da zura hannunsa ya ri'ko kungunta ya rike sosai yace."Kina so na mutu kenan wata uku da kike magana tamkar shekara uku ce a gurina ai ni yau ma bazan iya hakura ba yanzu kafin na fita zanyi saboda na

san innarki zata hanani shigowa da daddare." Yana maganar yana cusa hannunsa cikin rigarta

Zabura tayi baby zahra dake hannunta ta kusa fad'uwa yay saurin riketa yana dan kallonta yace.''Baki da hankali zaki yar min da momy ko."? Tana tureshi daga jikin

ta tace"To ka daina ta'bani ko kuma in maka ihu! Inna Hajara ta shigo taga abinda kake." Sai yasa dariya yana kallonta yace."Idan kin min ihu! Inna Hajara ta shigo taga abinda nake meye a ciki dama ni nafi so ta gani itace zataji kunya bani ba."

Shiru tay

i masa tana kokarin fito da nono domin bawa baby dake dan kuka......Taimaka mata yayi suka fito da nonon a tare, gabakid'aya idanunsa suka rufe ganin lafiyayyan nonon nata ya cika sosai gashi a tsaye nipple din ya sake tsukewa saboda tsotso, ya sauke ajiya

r zuciya me zafi a hankali ya dora hannunsa saman brest din yana shafawa tamkar wani maraya ya d'ora kanshi a kafadarta......Wasila abu biyu ne suka dameta Yanda yake shafa fatar saman brest dinta shine ya sanya ta shiga wani irin hali gashi baby zahra ta

kama nipple din tana ta tsotsa, sai tsigar jikinta ta dinga tashi duk ta rasa yan

da zatayi sai mutsu-mutsu takeyi tana dan tureshi yana sake makaleta a jikinsa.....Kuka tasa masa tana fad'in "Dan Allah ka bari wallahi babu dad'i."

Ya bud'e jajayen id

anunshi da suka 'kankance yana kallonta kwata kwata ji yay bakinsa yay nauyi ya kasa magana a take jikinsa ya shiga kyarma wani irin sanyi ya dinga ratsa shi.

Tunda taga ya shiga wannan yanayin sai gabanta ya tsananta fad'uwa domin tana gane duk sanda yak

e cikin tsananin sha'awa jikinsa rawa yake.

Baby Xahra ya kar'be daga hannunta ya ajiyeta gadonta dake gefe, tana kallonshi yana kokarin 'balle botiran rigarshi da links....Sai tayi yunkuri barin gurin yay gaggawar rike hannunta.

Bakinta sai rawa yake ta

kasa magana....Murya a hard'e yace."Ki taimaka min na samu stysifiend ba dole sai na shiga wannan gurin ba tunda kince da matsala ke kin san irin dubarar da zakiyi min ko."? Yana wani lankwashe kansa yake maganar.

A tsorace take kallonsa bakinta na rawa

tace"Fita fa zakayi ka shirya tsaf kuma sai kace wani abu ni dai dan Allah ka mayar da rigarka ka tafi inda zakaje."

'Dan 'bata rai yay yace."Wai meyasa ne duk sanda zance miki ga abinda nake so sai kinyi min gardama meye a ciki dan kinyi min dabaru na sa

mu biyan bukata kin san bana neman mata ko? kuma ke kadai ce matata to ki sani wannan halin naki zai iya janyowa na sake aure dan ni mutum ne mai yawan bukata da kuma san soyayya da kulawa."

Jin maganar aure yasa ta soma kuka tana kallonshi tace"To ai ina

yi maka kokari duk sanda zaka zo da bukatarka ina kokarin ganin ka samu gamsuwa ko ranar da zan haihu ma hakane ya faru, yanzu kuma ai haihuwa nayi ba sai ka hakura nayi ar'bain ba." Kansa ya dafe cikin 'bacin rai yace."Ba zakiyi abinda na umarceki ba." M

atsawa tayi gefe tana goge fuska...."Ni dai ka bari nayi ar'bain." ! Yaji kamar ya kwad'a mata mari! Yarinya mai shegen taurin kan tsiya wai meye manufar ar'bain d'in nan da malam bahaushe ya tsira! Tsaki! me kar'fi yaja ya mi'ke tsaye yana maida botiran r

igarsa ya d'auki hularsa da gilashinsa da ya aje ya sanya, ya kama hanya ya fita daga dakin ba tare da ya kalli inda take tsaye ba.

Yana fita ta nemi gefan gado ta zauna tana kuka ita tsoro takeji kada Inna hajara ta fahimci wani abun na faruwa a tsakani

nsu ta tafi kwata kwata bata so ta tafi shiyasa kuma tana jin tsoransa kada yazo ya danneta ya lalata mata d'inki duk da likitan tace gurin yayi normal amma ai baiyi wani 'kwarin kirki ba.

Inna Hajara ce kadai a palo ita hajja ta shiga daki domin daura

alwalar sallahr walha to tana ganin wucewarsa ba tare da ya ko kalli inda take ba sai jikinta yay sanyi a hankali ta mike ta nufi dakin Wasilan.....Ta tarar da ita xaune tana kuka. Zama tayi kusa da ita a hankali tace"Goge hawayenki." Wasila ta goge haway

enta tana sunkuyar da kanta.....Inna Hajara tace"Ni banzo da niyyar na kashe miki aure ba Wasila, na lura mijinki bashi da hakuri ko kad'an, ni kuma ke nake tausayawa saboda irin wahalhalun da kika sha kafin ki haihu Uwa uba akazo aka yanka ki aka d'inke k

amar 'kwarya, dole a sanya ido sosai a kanki domin ingantuwar lafiyarki! Bayan haka kuma dole ne kafin ki komawa miji sai an gyara miki jikinki domin haihuwar da kikayi duk wata ni'ima da kike dashi babu nida a tunanina ma ina so idan zan tafi gida muje t

are dake can in gyaraki sosai da sosai to amma tunda naga take taken mijinki to zan tattara nawa nawa na tafi dama akan dole nake zaune a gidan, bana so yazo ya dinga jin haushina ko ya fahimci cewar nice nake hanaki biya masa bukata."

Tun kafin Inna h

ajara ta 'karasa maganarta ta rike hannuwanta tamau! tana kuka sha'be!sha'be! "Wallahi Inna ba zaki tafi ba sai nayi ar'bain sai kace wata mara gata da galihu! ai haihuwar fari nayi kuma koda zanyi haihuwa goma a gidanan kina da damar da zaki zo ki zauna t

are dani tunda ina cikin gidan.....Inna nasan abinda nakeyi nima bazan yarda ya haike min ba kawai ya cuceni bayan ban gama dawowa dai-dai ba, na amince zan jure ko wane irin fushin da zai dauka dani nasan idan ya gaji zai daina.."

Inna hajara tace"A'a

Wasila ni bazan so kullum ki dinga kwana da tsiniwar Allah da mala'ikunsa ba, kibi mijinki sau da '

kafa kiyi masa biyayya kan abinda yake so ni dai na fad'a miki yau yau zan tafi dan naga kamar haushina yake ji to zai dawo ya tarar na bar masa gidansa.

Wasila ta dinga kuka tana bata hakuri Inna Hajara ta rufe idonta ruf ta fita daga dakin domun zuwa ta had'a kayanta.......Hannunta na kyarma ta d'auki wayarta ta shiga kiransa.....Lokacin yana cikin company sa tare da ma'aikatansa yaga kiran wayar tata

ya'ki dauka har yanzu haushinta yake ji

Ta kira ya kai sau biyar bai dauka ba sai kawai ta aje wayar ta fito palo tana goge fuskarta tasan haushinta yake ji shiyasa bai dauki wayarta ba, tana fitowa palo ta tarar Inna hajara da hajja suna fafatawa, Inna H

ajara taurin kan tsiya ne da ita ta'ki sauraran hajja hannunta ri'ke da jakar kayanta ta kama hanya ta fita Wasila tabi bayanta har wajen harabar gidan......Garba ya iso gurin da sauri ya karbi jakar kayan hannunta shi baiyi tunanin wani abuba saboda ya

dauka inna zata tafi gidane....Can parking ya nufa da jakar kayan ya fito da mota har inda suke tsaye Inna hajara ta bude ta shiga tana 'bata rai! Wasila kallonta kawai takeyi domin ita har ta gaji da magiya da bata hakuri, tana tsaye har garba yaja mota

r suka fita daga gidan, ta girgiza kanta ta juya domin komawa ciki tana kokarin mayar da hawayen dake so ya zubo mata.

Tana shiga ta tarar da Hajja a tsaye a tsakiyar palon itama tana cikin alhini na tafiyar Inna hajaran Tace"Wasila kodai wani abu akayi

wa hajara ne irin wannan tafiya haka da gaggawa, kuma na lura kamar dai ranta a 'bace yake."!

Ta d'an d'auke hawaye a hankali tace"Haka kawai ta tubure wai gida zata tafi babu abinda akayi mata."

Hajja ta zauna kan kujera jikinta a sanyaye tace"To ai shi

kkenan Allah ya sauketa lafiya." Ta amsa da "ameen tana kokarin shiga d'aki.

****

"Haba Uwani wai dan Allah tun yaushe nake miki magiya kan ki kaimu muga d'akin yarinyar amma kin'ki kaimu kullum nayi miki magana sai kice zamuje to sai yaushe zamuje?

kada fa ki manta da cewar kwanaki dani dake mukayi lissafin watannin cikin yarinyar har ki kecewa cikin ya isa haihuwa nace watakila ma ta haihu to kinga yana da kyau muje muga halin da ake ciki." Kuluwa ce zaune a gaban Uwani take wannan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login