Showing 96001 words to 99000 words out of 176330 words

Chapter 33 - ABADAN COMPLETE

HUGUMA   

10 Sep 2026

14

dauke kai ta qaras inda yake,gabanshi ta tsugunna

''inna wuro tace ko zaka fita waje can y

afi iska mai dadi



''tana maganar ne idonta na kallon gefe ba inda yake ba,kai ya guada alamun to cikin zuciyarshi yana fadin

''Allah yama inna wuro albarka,ko banza ta samamin hanyar da yau zan wuni ina kallonki,ko ke ba zaki kalleni ba,'yar qauye kawai''

.

sau uku tana qoqarin dagashi ta kasa,mero na tsaye ta dameta da maganar kaza zakiyi kinga haka zakiyi,ana hudun ne ta taho da sauri zata tayata kama shi

''me haka ne wai mero



lafiyanki



''madyam ta fada a dan zafafe,ita kanta batasan ta fada din ba

sai daga bisani,sai ta waske da aon ci gaba da daga shi din,qarshe inna wuro ce ta taimaka mata suka dorashin ita ta turoshi mero da inna wuron sukayi gaba.

Da ido yake binsu hirar tasu na bashi sha'awa,zaya so ace yana da bakin da zai saka cikin hira

r tasu,hakanan yaji jininshi ya hadu da inna wuro,tsohuwa ce mai karamci da dattako kamar maminshi duk da ta fita shekaru,weather din garin yaji yayi masa kamar a qasashen turai ba cikin qasar kano ba,kanon ma cikin wani qauye.

Murmushin da maryam ta

ga yana tashi kadan kadan kan fuskarshi ya tabbatar mata yaji dadin zaman gun,hakan neya bawa mero damar matso da kujerarta 'yar tsuguno daura da abdallah ,ta fara bashi labaran qauyen da waqoqinsu,al'a dunsu da kuma yanayin shagulgulansu inna wuro na sa m

usu baki jefi jefi,yadda maryam taga ya bada hankalinshi sosai kan meron sai taji baa wai,duk da tana ta qoqarin nutsar da zuciyarta kan meye nata



,Abdallah dama temporary ne jiran samun lafiyarshi kawai take ta kaucema rayuwarsa.

Saidai duk yadda tas

o nutsar da kanta hakanan taji hakan ya faskara,sai tayi zaton zama shirun da tayi ne saboda gaka ta miqe tana fadin

''inna wuro bani garin tuwon nan mana na tankade miki shi''

''kwano biyar ne fa meramu



ba zaki iya ba''

''ai inna babu abinda nake Allah

zan iya ki bani kawai''

hakanna inna wuro ta bata din sai ta tafi can dan nesa da au kadan bakin rijiya ta zauna ta saka kujera ta tsuguno tana son kauda hankalinta daga garesu,duk da tana iya kallosu tana kuma jin abinda suke fada.

A sace yake ka

llinta,qarara ya karanto damuwa cikin zuciyarta saidai miskilancinta da wani dalilinta can maras tushe ya hanata gano me take ciki



me take so



mene kuma bata so,duk sanda ya fusknci zata dago kai ta kallesu sai ya dauke kanshi ya maida kan mero,ita kam mero

farinciki ya cika zuciyarta kamar ta taahi taka rawa,tqu,balaraben nan ne yake ta kallonta,kai gaskiya tafi kowacce mace dake cikin qauyen ni'ima sa'ar zuwa duniya.

har aka kira sallar la'asar yana nan zaune yana sauraron hirar tasu yana kuma tayasu

da murmushi,musamman idan akayi abun dariya,tankaden da ya kamata ace ta gamashi cikin qanqanin lokaci sai gashi zuwa lokacin la'asar din ko rabi bata yi ba,hakanan ta miqe ta karkade jikinta,ta maida saura cikin buhu wani kuma cikin fanteka ta rufe ta sha

re gun

''ayiwa bawan Allah alwala ko



''inji inna wuro,mero ce ta miqe tana fadin

''sai nayi masa inna tunda maryamu na tankade''

''a'ah,ina aka taba haka mutum da matarsa ba wai bat nan bane,haramci ne ai,ki karbi tankaden ita tayi masa alwalar....af,ta

ma kammala kinga,to bata butar''

haka nan taji tana jin haushin meron,ko da tazo miqa mata butar karba tayi ba tare da ta kalleta ba,abdallah ma kan whell chair dinshi yana kallinsu,murmushi ya aubuce masa kana ya duqar da kanshi yana jin wani sukuni

da farinciki na ratsaahi wanda tunda ya kwanta cutar nan baiji irinshi ba sai yau,ya kuma rasa na meye,a gaggauce ta daura mishi alwala ta fuskantar da shi gabas ta bar gurin taje tayi tata,da suka idar ma hirar taau suka zo suka dora,madafa tayi tafiyarta

wata rumface ta bunu dake gefe daya na tsakar gidan,anan din ma tana iya hangosu amma sai ta juya musu baya.

haka ta hana kanta sakat taqi zama gu daya har sai da ta kammala tuwon masarar miyar danyar kubewa,shi kuma abdallah ta dafa miahi couse cous

e da miyar ganye

anan din ma dai suka zauna don cin abincin dare,qemem yaqi couse couse din,tayi mamaki matuqa da taga yana cin tuwon masarar,shi da ko na semovita bai dameshi ba

''ato,dama ai tuwo shine abinci,a tsari na abincin gidan bahaushe ma ahekar

i aru aru ahine abincin dare ba wadannan abinciccikan yahudawan ba da basu qara mana komai face cututtuka''inji inna wuro ta fada har sai da tasa abdallah murmushi.

ido ya zuba mata ganin kowa ya kammala cin abincin ta tattara kwanukan ta wanke ta daw

o ta zauna ba tare da ta sa komai cikinta ba,ta lura sarai da yadda yake kallonta don haka ta canza ma gin zama inda ba zasu iya hada ido ba

''abdullshi me kake kallo ne



,ko wani abun kake so



''inji mero ta fada

kai ya gyada,bayqn ya kalleta,sai ta sake

washe haqora tana fadin

''to me kake so



''ya tsanshi ya nuna saitin maryam,sai ta bi yatsar da kallo har kn maryam

sai ta rage farashin fara'ar fuskarta kana tace

''maryamu magana ye dake ko



''ba tare data dubesu ba tana tsincewa inna wuro qulalai daga

cikin audugar da take kadi,cikin salon dakiya da shariya tace

''magana ta me kenan



''

''nima ban sani ba''meramu ta fada tana komawa inda ta taso ta zauna,qarasowar inna wuro gun yasa suka ci gaba da hirarsu,haka ya qarqci kallonta har ya haqura.

in

na wuro ce ta lura da yadda ya soma lumshe ido

''bawan Allah bacci ina tsammani yake ji''inji inna wuro

''kaishi daki maza meramu,idan zaki dawo kya dawo''ta fada tana janye daeon audugar daga gabanta,yana sane ya lumahe idon yaji dadi da inna wuro ta ma

sa hanya.

da qyar ta samu dorashi kan katifar,ta janyo masa abun rufa kan ta gama lullubeshi ta tuna da ruwan ganyan magaryarta,taso idanunshi biyu yasha,amma duka da haka ta debo cikin tafukan hannunta ta shafa mishi dukka jikinshi,kana ta masa addu'

o'in kwanciya barci ta shafa masa,wani sanyi da nutsuwa yaji suna ratsashi,kamar ta shafa masa ruwan qanqara,ta juya da nufin tashi sai taji an janyota,bata zata ba sabida haka kai tsaye jikinshi ta fada

''ka sake ni''take fada tana mutsu mutsu,saidai ko

ajikinshi,bata son me yasa yake yawan son rungumarta ba haka

''haba ka sakeni nace mana,kayita taba jikin mutane haka kawai''

''jiki na ne,halaliyata,lada ma Allah zaya bani''haka yakeson fada amma ya gaza.

duk yada taso zame jikin nata ta gaza,tana

ji tana gani har gajiya ta sauko mata bacci ya qwace idanunta,yan jin saukar numfashinta cikin nutsuwa,shi din ma idanun nasa a rufen auke sai kayi tsammani bacci yake,saidai sam ko daya,tunanin maryam dinne cike fal da kwanyarsa,yana tausayinta,yana jin s

onta har cikin jini tsoka da bargonsa fiye da da,sai yanzu yake sake tabbatarwa kanshi Alah ne kawai ya bashi maryam din ba mutum dukiya ko qarfin iko ba,maryam din kadarace mai tsada kai tama shallake kadara agunsa,samun mace mai halacci da juriya kan lal

ura da halayen mijinta abune mai,matuqar wuta a wananan zamanin namu,ya sani sarai bata zaman qauye iyakacinta da ahi ziyara ta kwanaki uku,sai gashi yau ta amince ta yarda ta zauna cikinsa shi da ita cikin zuriyarta har zuwa lokacin da Allah zai bashi laf

iya ba tare da damuwa raki ko qorafi ba,lokacin da dukkansu shi da ita basu san sanda zaizo ba don babu wanda ya san iya tsahonsa,baya ga dama da take da shi na tafiyarta ta barshi tunda babu zuri'a ko iddarsa akanta.

A hankali ya dinga tina yininsu

shi da ita na yau,murmushi ya subuce masa,fushi da kishi daya dinga ganowa qarara cikin qwayar idanunta,saidai ita sam bata san da su ba,batasan suna bayyanar da kansu bane su duk yadda kakai ga qoqarin boyesu,murmushi ya subuce masa,ya sanya hannunshi ya

cire dan hijabin dake maqale a wuyanta,ya sake zare ribbom din kanta ya sa hannunshi yana shafa gashin,santsinsa da qamshinsa na burgeta,yayi imani abinda yake ji game da maryam din wani irin jini a jiki da ba kowa Allah yake bawa ba.

Ta sake zubawa q

ofar dakin ido a karo na barkatai,mintina kusan goma ta sake janye tagumin da tayi ta saki ajiyar zuciya ta kalli inna wuro da ta duqufa wajen yin kadinta

''kinga inna meramu shiru bata dawo ba''

''eh.....wata qila itama baccin yayi awon gaba da ita ne,a

i yau kam ta aikatu itama,meramu babu son jiki,harvta fiki son aiki''innan ta fada cikin halin ko in kula don bata kawo komai cikin ranta ba

''amma inna bacci da wuri haka,qarfe tara da rabi fa,yanzu ma wasu suke fita dandali''

''yo su mutan birni barci

da wuri a gunau wani abu ne



,rayuwa suke gida a qulle,daga sallar isha idan suka shige gidajensu suka kulle sai kuma washegari''

''q'nn,bari na tashi nima na tafi''

''da wuri haka



''inna wuro ta fada tana binta da kallo

''eh''ta bata amsa gana zira suda

ddun silifas dinta

''to kinga ga abincin nan kokus yake kome ne



,tafi da shi gida kwaci''duk yadda take kwadayin couse couse rin sanda ake dafashi take fata ya shigo farantinta amma a yanzu sai taji duk ya sure mata,a salube ta dauki kwanon tana fadin

''

an gode sai da safe''

''Allah ya bamu alkahairi''inji inna wuron

bata haqura ba sai da ta je bakin qofar dakin tace

''abdullahi da meramu sai da safe''sau uku tana maimaitawa taji shiru,abdallah na jinta amma maryam batasan ma me ake ba don ta jima ciki

n daddadar duniyar barci ta musamman.

inna wuro ta dubeta

''na gaya miki sunyi bacci,kije kwa hadu da safen,ki gaida su hansai''jiki ba qwari ta fice daga gidan

ko a gida tana kallo qannanta na damben cin couse couse couse din amma ta kasa ci sai id

o kawai data zuba musu tana kallonsu,sau uku babarta iya hansai na mata tayin taci bakinta cike da shi taqi cewa komai,qarshe ma tashi tayi ta shige dan takurarren dakinta wanda zakayi tsammanin duk ranar da aka samu ruwan sama mai yawa zai iya ruftowa maz

auna ciki.

kasa bacci tayi,yau kam ta kai maqura,jin son Abdallan take kamar ta mutu kota haukace,ita kam ko a haka ma zata iya aurenshi,amma idan ta dubeshi ta dubi kanta sai jinta yayi sanyi qalau,tasan wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa,duk da batas

an waye ainihin abdallah ba,amma kallo daya da ta masa ta san cewa ba qaramin mutum bane shi da maryam din ma baki daya

tunanin da ya isheta qarshe kuka ta fashe da shi a haka bacci yayi awon gaba da ita tana Allah Allah gari ya waye ta koma gidan inna wu

ro.

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

Kamar yadda suka amida shi al'adarsu bayan sallar la'asar su zauna hira har salllar magariba wani lokaci har isha'a yanzu ma hakane.

yana zaune kan whell chair wanda yau ita da mustafa suka dorashi don ya dawo daga gona da wuri,

ta karbi dan qaramin alqur'anin da ya gama karatu da ahi daga hannunshi ta ajjiyeshi a muhallinsa,ta dauko roban da take ajjiye duwan ganyan magaryar,wanda ta karanta a yoyin dake cikin surutul A'araf aya ta 117 zuwa ta 122

sai ta cikin suratul yunus aya

ta 79 zuwa ta 81

sai cikin suratu Daha aya ta 65 zuwa ta 70

ayatul kursiyyu falaq da nasi da iklas duka,tana shirin tsiyayowa taji sallamar mero wadda ta fita dazun tace zata je tayi wanka,idan da savbo

maryam ta saba,da safe zata zo da kwalliyarta,idan

ta gama wuninta qarfe uku zata koma gida ta sake wanka da kwalliyarsu irin ta mutan qauye.

a cup ta tsiyayo ta miqo masa,sai ya dan bata rai,saboda dandanon magaryar da baiso,itama kicin kicin tayi,musamman da ta jiyo tana tambayar inna wuro ina suke

basu fito ba,tasan kadan daga aikinta ta fado musu,taji dadi da inna wuron ta ce mata

''zauna anan ki tsinke zogalen nan kada meramu ta fito ta hau aikin,sonke kwana biyu naga gun hira kika fi kauri,duka kin sakar mata ragamar aikin,kullum ita ke ruwon

dare ta barki da lugudar lebe''.

Dariya ta bashi cikin ranshi ganin yadda tayi wani kicin kicin

''lallai ma yarinya,wuyanki ya isa yanka,ni zaki wani budewa ido kamar qaninki,Allah ya bani lafiya zaki gane shayi ruwa ne''hakanan ya karba yayi bismill

ah cikin ranshi yasha donshi kansa yana jin dadin sa,wani lokacin don ya tsokaneta yake qin karba,don ya lura indai yanason ganin fushi da bacin ranta yaqi karba yasha ya kuma zauna sauraren labaran mero

ta bude wata 'yar roba mai kama data naseline,s

aidai ba shi bane ciki,man zaitun ne da na habbatussaudah wanda ta karantawa ayoyin da suka wuce a baya ta qara da ayatushshifa ta tofa aciki ya zama na man shafawarsa ta miqa masa don tana jin kunyar shafa masa,nan ma sai da ya gama shan qamahinsa ya amsa

ya shafa ta maidashi inda yake.

komawa tayi ta zauna kamar ba fitar zasuyi ba,ya zuba mata ido yana son ganin iya gudun ruwanta saidai qememe tayi taqi kallonshi ta fara karanta azkar dinta na maraice,ta kammal ata shiga wasu sabgogin abinta,don har

cikin ranta bata jin fitar,sai data qara kusan awa guda sannan ta miqe ta iso inda yake,ido suka hada sai taga ya dan harareta,dariya ma yaso bata amma sai ta dake ta tura whellchair din a tausashe suka fito.

tana kan tabarmar kabar da suka saba zama

qasan bishiyar dalbejiyar,tasha daobta daidai da irin nasu baki cike da kan ta kile,koriyar atamfa ce jikinta shar wadda hatta da zanan jikinta yanzun da zaka bawa maryam ta zana maka tsab zata zanashi saboda tsabar sawar da meron keyi yau da gobe don bata

da kamarta duk cikin kayanta,gaba dayanta qofar dakin take kallo,gyaran zogalen da aka batan ma ko rabi bata yi ba,inna wuro batasan me ke gudana ba don yau tayi riga malam masallaci ta shiga ta hura wutar tuwon da kanta don kada maryam ta karba yadda ta

saba su ta barsu da shan inuwar qasan bishiya,sai da ta kalli gidan ko ina tsaf ya sha shara sai qamshin qasa yake kamar kullum kana ta juya abdallah can bayan mero yadda ba zata iya ganin fuskarshi ba saidai idan juyowa zatayi,ai kam kamad an tsikareta ta

juyo din tana fadin

''nayi zaton yau ba zaku fito ba ai,har na fidda tsammani Allah''.

kai kawai ya girgiza yana dan qaramin murmushi wanda idan yayi meron kejin duk duniya fa ita an gama biyanta,kallon murmushin take da matuqar

qima don bata taba g

anin wani cikin samarin garin da idan yayi murmushi yake qawatashi ya masa kyau kwatankwacin haka ba.

yau kam innan ta zaunar da ita cikinsu babu batun zuwa kitchen wato rumfar girki,taqi kallo kosa baki ko sau daya cikin hirarsu,ranta take ji yana ma

ta suya,kamar ta kori mero amma sai taga meye nata a cik,bata da wannan hurumin,ita kanta batasan me yake jefata damuwa mai yawa kan lamadin meron ba da abdallah,ita da ya kamata ta zama 'yar abi yarima asha kida cikin sabgar.

Dakinsu ta koma ta dora

doguwar riga kan dinkin atamfa riga da skert dake jikinta,cikin kitchen ta samu inna wuro

''inna naga kuna kusa da rafo,zan qarasa da abdallah can yaga garin naku''

''to Allah ya kiyaye sai kun dawo''

bata kalli mero ba bare tace mata wani abu ta fara t

ura whell chair din abdallah,ya waiwayo suka hada ido sai ta dauke idonta

''ina zaki meramu



''mero ta fada tana miqewa da sauri tare da zura takalmanta ta biyo bayanta,inna dake kitchen ce ta amsa mata

''zasu rafin malam dogo na bayanmun nan''

''ai da n

i za'a,dama ina son in gaya muku idan kuna son zuwa,girin na da kyau aradu''ta fada tana bin bayan maryam

''um hmmm''kawai tace da ita tana ci gaba da tura abdallah.

Tafe suke mero na nunnuna musu gurare,duk da wani gun ma maryam dauke kanta take ba

kalla taake ba,saidai abdallah ya bada hankalinshi sosai bisa dukkana alamu hakan na masa dadi kuma yana fahimtar baya nanta,mero kan makar ta taka rawa don murna,yau gata ka larabawan birni,duk inda suka gifta sqi an bisu da kallo har wasu ma su tambayi m

eron

'''yan uwanmu ne,wannan yaya na ne''haka take fada cikin washe baki,wasu mazan har hannu suke bawa abdallah,ba qyama yake basu nashi hannun suyi musaba,kodama can shi cikin aqidunshi baya qyamar maras shi,duk wanda kuwa sukayi musabahar farinciki da

murna kamar yayi me,musamman idan ya shinshina hannunahi yaji qamahin turaren abdallan,da yawa idan mero tace bashi da lafiya baya iya magana addu'a suke masa sosai Allah ya bashi lafiya.

sannu a hankali suka ci gaba da ratsa qauyen mai cike da ni'ima

kamar yadda sunanshi yake,ko ina ka duba shuke shuke ne koraye shar,a yadda taji mero na gaya wa abdallah haka qauyen nasu yake ko ba cikin damina ba,cikin mintina goma suka iso bakin rafin,ruwa ne mai kyau yake guda na ciyayi baibaye da da bakinshi,wasu

fararen dutsina da jajayene reras a zube a gun tamkar ana sane aka shiryasu,saidai ikon Allah yafi gaban haka ai.

Gab da bakin nan maryam ata ajjiyeshi,suna iya,hango shanu daga daya,bangaren sunata kai kawo,mafi yawancincinsu fararene qal sai kuma ru

wan qasa jifa jifa,shegen surutun mero sai data gaya musu hatta da mai shanun,na wani dan garin ne saidai duk da dukiyar shanun da Alah ya

bashi,matashine don bazai wuce shekara talatin ba,don ko auren fari baiyi ba,gefe ta matsa maryam ta zura qafafunta c

ikin ruwan tana kallon yadda yake gudana,tunanin mama da hindatunta ya fado mata,don kusan babu wanda suke waya da shi a yanzun ,hisham ne yace ta haqura din kada nene ta bayar da nim dinta ayi tracing nasu,da hakan ma saidai abinda take ji yana sukuwa azu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login