Showing 138001 words to 141000 words out of 176330 words

Chapter 47 - ABADAN COMPLETE

HUGUMA   

10 Sep 2026

24

kwanyarta ta kama wanann ta saki wancan,cikin haka tunanin mero ya fado mata,sai taji ranta ya baci,tana son sanin haqiqanin me tsakaninsa da ita kafin komai ya daidaita,a uziyya tayi ta kori tunanin daga ranta don haka dab

i'arta take bata kwana da kowa cikin ranta

πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚

Ta makara sosai gun tashi kuma mami bata tayar da ita ba,bakinta ta wanke da fuskarta ta fito falon bata tadda mami ba sai baaba uwani tana ta gyara kitchen,nan ta tsaya sunq gaisawa har mami

n ta sauko,tayi adonta cikin dogowar riga mai zubin buba saidai ready made ce wannan,bayan sun

gaisa mamin ta gaya mata ta shirya hajiya laila na zuwa anjima zata fara mata gyaran jiki,ita gaba daya kunya ma kamata take duk da ta sani mami bata dauketa sur

uka ba amma akwai kunya tsakani,ta amsa mata da to sannan ta koma daki.

Ta daura towel tana shirin shiga wanka saqo ya shigo wayar sai ta dawo ta duba,number din dazu ce wadda ta tabbatar ta abdallah ce

''baby jiya kin kusa kasheni wlh,sauran qiris n

a gayawa mami yadda kike gara mata yaro,ina gaya miki damuwa ta kika gudu kika barni,me yasa baby

?

,i need your help baby''

bata shirya ba amma sai da murmushi ya subuce mata,ya tuna mata ma,take ta kira mamanta,hira sukayi sosai wadda ta qara mata kewar g

idansu

Cikin kwanakin gyara sosai maryam kesha wanda ko bazawara aka yiwa hakan sai ta tsere ma sa'a,itadai maryam nata ido,wannan qauna da mami kewa abdallah ba kadan bace

πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒ

Zaune suke su biyu cikin fallen dakin nata wanda yafi kam

a da kango,idan ba kyakkyawan sani kayi mata ba zaka tsammaci mahaukaciya ce sabun kamu,tuni ta saje da su tabi sahunsu kamar yadda habiba ta shaida mata,ta tsotse ta rame kamar wadda kullum ake diba ana kada miya,ga uban ciki a gaba ya fito yayi tsororo k

amar dosana shi akayi babu kyawun gani.

''yanzu habiba babu wata hanya kenan ta kubuta''ta tambayeta cikin damuwa

''bana zaton zahariyya akwai''

dariya sukaji ana babaka musu a razane suka daga kansnsu,malam na hayi ne tsaye bakin qofar dakin yana s

higowa

''kuna batawa kanku lokaci ne amma babu wadda ta isa ta kubuta daga gareni,mutane ne ku masu son zuciya,kun bijerewa Allah kuna neman biyan buqatarku kan wani mummunan qudiri naku,yadda kuke da baqar zuciya nina haka nake,kunga kenan zamu je ta tad

da da mujemu,a sannu sannu mata ire irenku zasu ci gaba da shiga masibu kala kala,walau a nan duniya ko a lahira,irin mu muna nan da yawa Allah ya ajjiyemu saboda ire irenku,haka gaba dayq mu da ku kuma sai munje lahira za'a hukunta mu baki daya,ni dama na

riga na sani bani da rabo a lahira,kunga ai gwara naci nawa tun anan''ya juya ya fice yana sheqa dariyarsa.

Hada kai sukayi suka fashe da kuka kowacce da irin tata nadamar,sun qi Allah bayan ya musu ni'ima,idanunsu ya rufe basu ganin baiwar da yayi m

usu da tarin ni'imominshi a garesu sai yanzu da ya karbe abinsa,dama ya fada cikin littafinsa mai tsarki''idan kuka gode min zan qara muku,idan kuma kuka kafirce to haqiqa azabata mai tsanani ce'',sun yarda sun dauki hudubar shaidan,wanda dama bashi da bur

in da ya wuce batar bayan dama ya sani cewa tun can dama shi batacce ne,kuma dama yayi wa Allah alqawari sai ya batar dq bayinsa kamar yadda yazo cikin wasu surori na qur'ani lokqcin da Allah yace ya fita daga aljanna la'ananne ne shi

''kuma la'anata tana

tare da kai har zuwa ranar qarshe''

sai shaidan din yace

''ya ubangiji ka jinkirta min izuwa ranar qiyama''sai Allah yace an jirka maka,har uzuwa rana da lokaci sananne,sai shqidan yqce da ubangiji

''na rantse da isarka da buwayarka sai na batar da su

gaba daya,saidai bayinka daga cikinsu tsarkakakku''sai Allah yace da shi

''haqiqa bayina baka da wani iko a kansu sai wadanda suka bika dagq cikin batattu,kuma haqiqa jahannama ce makomarsu gaba dayansu,tana da qofofi guda bakwai''a wani gurin kuma shaida

n din yace

''zanzo musu ta tsakaninsu data damansu data hagunsu mafi yawansu zaka samesu marasa godiya''

haka ya sake fada a wani gurin cewa

''sai na batar da su,sai na sanya musu buri sai na umarcesu su canza halittar Allah(kamar bleeching yana daya da

ga ciki)

shi yasa Allah da kansa yake fada mana

''haqiqa shaidan abokin gabarku ne ku ruqe shi abokin gaba'',muna mantawa ne da ranar mutuwa ranar tonon asiri ranar hisabi,ranar da duk wata rai saita bi ta saman siradi ta wuce wanda qarqashinsa wutar jah

annama ce,aikinka mai kyau gaskiyarka zumunci da ruqon amana ne kawai zai qetarar da kai cikin salama

Son zuciya ya mana yawa,muna biyewa soye soyen zuciyoyinmu baka iya hana zuciyarka aikata mummuna wanda hakan ke kaimu ga halaka,Annabi muhammad S A

W yana cewa''an lullube aljanna da abinda rai baya so(kamar salla azumi zakka,zumunci,da sauran ayyukan alkahairi da bamu son yi ko muke jin wuya gun aikata shi)an kuma lullube wuta da sha'awe sha'awe(kamar zina,caca,cin dukiyar marayu,annamimanci,sata da

sauran abubuwa da rai kejin dadi yayin aikashi)''

Allah ya sake cewa ba don falarlarsa da rahamarsa ba da duka munbi shaidan face 'yan kadan

Allah kasa mu dace duniya da lahira

Sun jima cikin alhini da jimantawa kansu kafin habiba tace

''zahariyy

a nifa na gaji,anya ba kashe malam zamuyi ba

?

''duk da yadda taso ga neman mafita amma sai da shawara ta tsoratata,don bata manta ba irin wannan kuskuren taso aikatawa ya kawota ga wannan matsayin da take ciki yanzu

''habiba,in sake yunqurin aikata wani ku

skuren kenan

?

''

''kashe malam,zahariyyq rage mugun iri ne cikin al'umma,bakiji abinda yace babe,malam fa bazai taba shiryuwa ba,shin kin san shi mutum nawa ya kashe cikin wannan qazamar harkar tasa

?

(hmmm,sai yanzu data ritsa da su suka san qazama ce)''

c

ikin rashin gamsuwa ta girgiza kai

''wannan shi da Allahnsa amma mu dq muke neman kubuta kuma inamu ina kisa,shawara daya ce kawai tunda mu bamu tsaya munyi karatun addini ba boko muka sa a gaba,ba wasu addu'o'i garemu ba kawai kullum mu dinga karanta mas

a fatiha ba adadi,ai Allah yana jinmu,kuma nasan da yardaraa wata rana zamu kubuta''

take ta yarda da shawarar zahariyyan don tafi tata fidda maslaha

*mrs muhammd ce*

πŸ“šπŸ“šπŸ“š

✍

🏽

✍

🏽

✍

🏽

πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–

🌺🌺🌺🌺🌺🌺

🌺

*ABADAN*

🌺

πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–

🌺🌺🌺🌺🌺🌺



πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ



πŸ’–πŸŒΊπŸ’–



πŸŒΊπŸ’–



πŸ’–

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*

πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–



πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–



πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ



πŸ’–πŸŒΊ



πŸ’–

Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*

πŸ’‘

*_home of expert and perfect wr

iters_*



β–Ά

5

⃣

9

⃣

*An karbo daga Abdullahi dan amru dan Aas Allah ya yarda dasu baki daya,haqiqa Manzan Allah S A W yace''yana daga cikin manya manyan zunubai mutum ya zagi iyayensa(uwa da uba)'',sai sahabbai suka ce ''shin mutum zai iya zagi

n iyayensa

?

'',sai Manzo S A W yace''eh,a zagi mahaifin mutum,mutum(wanda aka zaga) shima ya zagi mahaifinsa(mahaifin wanda ya zageshi din),ya zagi mahaifiyarsa shima(ya rama) ya zagi tasa(wanda ya zageshin)''*

_ruwayar bukhari da muslim ne_

Itakanta ko ba'a gaya mata ba tasan ta canza,wani santsi da qamahi fatarta ke fitarwa na musamman,wani lokaci har shanshana kanta takeyi kota tsaya kallon kanta a madubi,magani masu kyau mamin ke bata na ainihin 'ya'yan itatuwa ba gamje gamjen bature ba

,tana jin naiyinta da kunyarta haka zata karba ta sha tana rufe ido,mamin takanyi murmushi tace

''babu kunya tsakaninmu maryam diyata ce ke kamar yadda nasha fada,namiji kuwa dan son gyara ne bashi da kunya ta wanann bangaren,balle abdallah da ina kula da

rawan kanshi,idan kika zaune kara zube cikin lokaci qanqani zaki wargaje fes babu kunya zai dauko miki wata,shi yasa har yau ina

alfahari da lambar yabo da na karba agun daddyn abdallah har ya mutu yana yabamin,so haka nakeso ki zama gurin abdallah koma k

ifi haka,koda akwai wata ma kisha gabanta''

kunya ta kuma kamata duk da maganar ta taqarshe ta dan haifar mata da fargaba

πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚

Tun ranar bai kima kiranta ba,har ta dinga zaton ko fishi yayi,cikin ranta take jin ba dadi idan fushin kuwa y

ayi,can qasan ranta ake tsinkularta ta kirashi taji muryars amma da zarar tayi kamar ta kira din sai kunya da nauyi su hanata

Kusan tara na dare ne suna zaune ita da mami da baaba uwani,baaban ce ta musu sallama ta wuce bangarenta mami ta duba agogon

kana ta miqe ta haura sama bayan ta ce da maryam tana zuwa,kallo take amma batasan ya akayi idanunta suka kai kan hotkn abdallah window size dake kafe a can kusurwar falon ba,sai ta kafe hoton da ido,a hankali wani abu ya dinga motsa zuciyarta,ta miqa hann

unta ta duba call history inda num dinsa take wadda ko serving bata yi ba,ta shiga canki camkin ta kira ko a'a,kamar wadda aka tankwabi hannunta ta danna kiran gakin ya soma tafiya sai ta qyaleshi.

Daidai lokacin da yake cikin dakin hotel din da suka

sauka,shi da manyan yaransa ne guda biyu,a gaggauce yake shiryawa cikin wadansu baqaqen kaya samfurin kayan jami'an tsor,duk da kqyqn qiki ne amma ba qaramin kyau suka yi masa ba,yana cikin daura belt dinsa bayan ya sanya bindigarsa a aljihun wandon na bay

a yaga shigowar kiran,bai lura ba sosaj ya dauke kai yaci gaba da sanya boot a qafarshi baqi don muhimmin aiki ne a gabanshi bai saba qa'idar lokaci komai nasa a tsare yake

Tana dab da tsinkewa ya kai hannu da niyyar dauke wayoyin nashi ya kashesu don

bazai fita dasu ba,ba dasu zaiyi amfani ba already ya gama maqala na'urar da zasu dinga communicating da abokan aikin nasa a jikinsa,mamaki ya kamashi ganin sunan *honey sweet* bisa screen dinshi,katse kiran yayi kana ya kirata

sai da gabata ya dinga bug

awa kafin ta amsa kiran,a kasalance ta kara wayar a kunnenta hade da yin sallama,duk da kuzarin da yake da shi sai da yaji an zare masa shi tas,shi da yake ta shiryawa a gaggauce yana basu order din baison bata lokaci sai gashi yana shirin kwanciya saman g

ado,yaran nashi suka kalli junansu da lamar tambayar ya haka

?

a tsakaninsu saidai babu damar furtawa oga suka ja bakinsu suka tsuke,alama ya musu da su fita su jirashi a qofar dakin yana tsoron kada ya tafka abun kunya a gabansu,don tunda yaji muryarta koma

i ya kwance masa.

Shima dai a kasalance ya amsa mata sallamar,daga nata bangaren ma wani dafin ya kuma zuba mata,shiru ne ya ratsa tsakaninsu tana jiyo saukar

numfashinsa,ya shiryawa sata tayi magana koda bata so,ya santa da qin yarda da gaskiya ta

wannnan bangaren,saida yayi dariya ciki ciki sannan yace

''Allah sarki baby,kafin kice komai nasan kewata ke damunki kika kira kiji sweet voice nawa ko

?

''

gabanta ya dan fadi ta zaro ido kamar tana a gabansa ne,sai data cire wayar daga kunnenta ta sake

dubawa shidin ta kira sanann ta maida kunnenta

''sai kace wata kai,niba wannan yasa na kira ba,dole ce ma ta sani kiranka''

murmushi ya saki mai sauti wanda ya kusa wucewa da imaninta

''attitude naki din nan yana burgeni,kina da jarumta da yawa,aiki

ne ya cushe min shi ya hanani kiranki my suger''wani sanyi taji yana ratsata har sai data cure gu daya,rake idea din yadda zata bagarar da shi yazo mata

''hmmmm,gida nakeson naje naga mama''

shiru ya danyi kana ya sake sanyaya muryarsa

''nima zanso kij

e ki ganta din,amma sorry baby,gaskiyq ina kishinki da yawa,na tabbatar idan zaki din saidai driver ya kaiki fa,kinga kun kadaice daga ke sai shi cikin motar....har zuciyata ta fara zafi ma wallahi da tuna hakan da nayi''

ta hade rai don gaskiya tana matu

qar son ganin maman

''amma fa ka sani yaushe rabona da mama,tun ranar da kasa aka fiddani a gidan''ta fada cikin shagwabar da batasan tayi ba ma,shikam tuni taso sauya masa lissafi don sai da yayi ajiyar numfashi kana yace

''shine kuma sai kin illata

ni da muryarki

?

''

''me kuma nayi

?

''

''kinfi kowa sani,gaskiya my kiyi haquri idan Allah ya dawo dani na miki alqawarin kaiki da kaina ki wuni har dare sai nazo na daukeki kinji

?

''

hawaye taji kawai na silmiyo mata,don haskiya ta qagu taga mamanta,tayi k

ewarta sosai,sai kuma yqce sai ya dawo sanann zata je,bayan shi kullum sai yaga tashi maman saidai idan baya gari,kasa magana tayi shima shiru yayi yana saurarenta,can qasa ya jiyo kamar sautin kuka,da hanzari ya miqe ya zquna yana fadin

''ya salam,maryam

me yasa kika maida hawayenki masu araha irin haka

?

,daga cewa sai na dawo zaki je

?

''

''eh,ai baka kyauta ba,banson rashin adalci fa abdallah ka san halina sarai''cewar mami data amshi wayar bayan ta maidata handsfree,sam maryam bata san ma ta iso ba s

ai da ta qaraso gabanta

kanshi ya dafe

''shikenan mami nikam abdallah bawan Allah,naga ta kaina an hade min kai''

''har hanci da goshi ma zamu hade maka indai zaka dinga matsantawa irin haka''

''mami ina da kishi sosai kin sani,dole idan zata je mami d

river ne fa zai kaita,mami banason wallahi yani ya kalleta''

''oh abdallah,halin naka dai yana nan,to zuwa kam sai tajeshi haka kawai,wake raba da da uwa,yaushe rabon da tq gansu,haba abdallah''

''shikenan mami na yarda mata taje,amma ba kwana ba,yauwa..

....baaba sule ne zai kaita,kuma don Allah ta saka hijabi don Allah''ya fada a sanyaye,wani mugun kishinta yake ji yana yi kamar yasan gyaran jiki ake mata dan ubansu

kama bakinta mamin itama tayi kana tace

''iyeee,sannu fa ubana''marairaicewa yayi

''ma

mi pleaseeeeee.......''

''ya isa''tayi saurin tsaida shi

''taji zata saka,ince ko shikenan

?

''

''i love u my mommy''ya fada cikin murmushi

''me too my son''ta fada itama,tana shirin katse wayar yace

''yauwa mami.....i need your prayer mami zami fita ai

ki kan mutumin nan kimin addu'a mami kamar kika saba,i know ita ke kaini ga yin kowacce iriyar nasara''maryam dake gefe duk dai taji ba dadi wani kewa da karayar zuciya na son kamata

addu'a tayi masa sosai y

hannayensa a sama kamar suna tare ta gama suka

shafa su duka,sai yaji wata nutsuwa da dukka qarfinsa sun dawo.

Miqawa maryam wayar tayi dom suyi sallama

''baby....ki kulamin da kaina''

''kanka kuma

?

''

''eh i mean you,nine ke kamar yadda kece ni,byee love u much more''ya fada ya katse wayar sai

ya barta da waya a kunne,a sanyaye ta cire wayar bayan ta sauke ajiyar zuciya

πŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒ

Cikin atamfa excellent ta shirya pure cotton,duk da mai qaramin kudi ce amma ta matuqar amsarta,kalar blue black dark blue and navy blue da sea green ce,sai t

a samu kanta tana aiwatar da umarnknsa duk da ba'a tuna mata ba,hijabi ta sanya blur black wanda ya rufe ilahirin jikinta,mai hannu ne hakanan yayi matching sosai da atamfar ta,ita kanta data kalli madubi sai taga tayi masifar yin kyau,hakanan tana jinta c

ompertable sabanin mayafi,duk da cewa dama ita gwanar hijabince musamman sanda tana gida

baaba sule dinne kuwa tana fitowa suka gaisa da kanshi ya bude mata motad duk da bata so kunya ce take rufeta,don aqalla ya kusa sa'an abbanta

Ta dinga kallon un

guwar tasu,babu shakka gida akwai dadi,baka gane hakan sai randa aure ya daukeki daga cikinsa ya kaiki wani gu,komai rashin sukuni na gidanku randa ka barshi sai kaji kana kewa da begensa,ta samu gidan auren da ya ninka gidansu nesa ba kusa ba amma bata da

ina kewar gidansun ba,may b home is nothing but two arms holding you tight when you are at your worst

Cike da zumudi ta saka kai cikin gidan da saurinta saboda yadda jama'ar unguwa keta binta da kallo,suna ganin ta sake zama ta daban,wata ma

yaranta k

e kai mata gulmar maryam tazo sai a hau leqe saboda ta tsaya suna magana da baaba sule ashe mami ta cika boot da kaya bata sani ba sai yanzu yace ta turo yara su kwashe

Farinciki ya cika,zuciyarta ganin gidan qal a share sabanin da da iyakacin tsaftar

qofar dakinsu ne zuwa,cikin dakin nasu,lubabatu ce kan tabarma zaune da qananun qannensu wadanda suke daki daya da da qatuwar farar takarda ta shimfideta kan tabarma ta zana alifun ba'un har zuwa ya'un manya manya da alamu tana koya musu ne shi yasa ko sa

llamarta basu ji ba,kafin ta sake maimaita sallamar ta hango isyaku ya fito daga dakin uwarsa kanshi tsaye yabi takan takardar ya take rubutun kana yayo hanyar waje,lubabatun ce ta yunquro da sauri ta cafko wuyanshi ta baya

''wannan iskancin naka isyaku

ya isheni wallahi yau sai jikinka ya gaya maka''

Da sauri maryam ta qarasa don kada abun ya kwabe tana banbare hanunta daga wuyan isyaku wanda keta kici kicin qwace kansa cike da rashin kunya

''sakeshi lubabatu kinji sakeshi''sai a lokacin taga marya

m din ba musu ta sakeshin ya kuwa fice abinsa da gudu,ta saki fuskarta daga daurewar da tayi tana fadin

''sannu da zuwa adda maryam''

''yauwa lubabatu,karatu ake yi ne

?

''ta dubi yaran kana tace

''eh,makarantar dare suke zuwa malaminsu yace su tabbata su

n iya zuwa anjima zasu je kuma naga basu iya ba''farinciki ya kama maryam ganin an fara samun ci gaba a harkar karatun yaran

''da kyau kin kyauta kuwa lubabatu''

yaran suka zuba mata ido suna shakkad zuwa gurinta,ko dama can ita ba mafadaciya bace bata d

ai shiga shirginsu ne saboda gudun rashin kunya irin tasu,su kuma suna ganin a yanzu ta zama yar gayu kada ta makesu idan suka matso gurinta tunda haka jamila

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login