Showing 135001 words to 138000 words out of 176330 words
/>
''dubeki,a hakan zaki fita,shiga toilet kiyi wanka''
ido ta zazzaro duk da bata kallonshi,kamar yasan zaro idon tayi kuwa yace
''eh,ko ba zakiyi ba kije ki daura alwala muyi salla azahar tayi mu samu ladan jam'
i nasan yanzu masallaci sun riga da sun idar''
son fitar take don haka ta koma ta daura alwalar,kaya ta samu ya ajjiye mata da ido ta dubi kayan ya fahimci tambaya take
''ki sauya kaya na jikinki sunyi squeezing da yawa ko''ya bata masa ba tare daya dube
ta ba,ba musu don itama ta yarda haka dinne ta debi kayan ta koma toilet ta canza ya jasu suka bada sallar azahar,suna idarwa ko ko addu'a bata tsaya yi ba ta dauki key din dakin da ya dora sama dressing mirrow,shima baice komai don yasan yau kam ya samu d
ama mai yawa,binta yayi da kallo har ta fice
A falo ta taras da hindatu da mami nata hira abinsu kamar wadanda sukayi shekara da sanin juna
''sai yanzu adda maryam har ina shirin kkmawa inda na fito''inji hindatu da sauri ta mata alamar don Allah tay
i shiru don hindatu qanwar abdallah ce yanzun ta bata kunya,ashe mamin ta kula suka hada ido kunya ta kamata,sai yanzun ta gane wayo wato abdallah ya mata da ya sata canza kaya,tunda mami ai zata iya gane ba da su ta shiga ba,mamin gwanar kawaice da basarw
a sai kawai ta miqe ta koma samanta ta basu gu
ajiyar zuciya ta saki tayi harr da idanunta,hindatun dai tace
''ko kunya bakwaji adda maryam,kubar mamanku zaune ita daya ku qule daki kuna cin soyayyarku''ido ta zare mana
''yi mana shiru mara kunya 'yar l
ukuta kawai,wai hindatu haka kika koma
οΌ
,kina kallon kanki a madubi kuwa,lallai jabir shima da shi da ya barki kika yi qiba irin haka''
dariya tayi''ni da shi duka bamu ganin qibarmu,amma kowa sai ya ce mun zama 'yan lukutaye ni da shi''
''eh gaske''marya
m ta fada tana kallon hindatun yadda ta koma,tayi bul bul ta sake zama fara,hira tayi hira qarshe ma dakin,maryam din suka koma,sai da suka shafe aqalla kusan awanni biyu suna hirar yaushe gamo.
Har kusan qarfe uku na rana suna hira kafin tayi hara
mar tafiya,a falon suka sake taras da mami hannunta dauke da poil paper ta nufi dakin abdallah hindatu tayi mata sallam,cewa tayi ta jirata ta koma sama ta dawo dauke da turaruka ta bata,hannu bibniyu hindatu ta amsa ta mata godiya kana maryam ta rakota.
Wata sabuwar matrix ash colour taga ta saka muqulli ta bude,baki maryam ta kama
''ah,lallai yarinyar nan jabir na shagwabaki,yanzu shikam ya yarda ya bawa hindatu mai shegen rawar kai mota take ja
οΌ
''dariya hindatu tayi
''kai adda maryam,an girma da y
anzu,idan da rabo ma nan da wata bakwai sai kizo suna''
duka ta dan kai mata
''eh lallai hindatu baki da kunya,laifin jabir ne''sai da ta shiga cikin motar ta zauna kana tace''zan biya gida fa na gaida mama,me zan ce mata
οΌ
''take kewar gidan duk ta kamata
,tana son taga mamanta sosai,watanni kusan nawa ta share rabonta da ita,tun ranar da aka fiddota zuwa fidan mijinta
''kice ina gaidata sosai da sosai,sannan nima ina nan zuwa''
''amma adda maryam duk ranar da zaki din zaki biyo min ko don Allah''ta fada
taba yin kalar tausayi duk don tazo mata din,murmushi tayi
''kai hindatu''
''eh mana,baki fa taba zuwa min ba adda''
''to naji,zanzo insha Allahu''
''yauwa adda ta''ta fada tana dariya ta eufe murfin motar kana ta tada ta taja,bata bar gurin ba tsayawa
tayi taga irin driving din hindatun,sai da ta fice a daga gidan kana ta saki yar qaramar dariya tana girgiza kai
''hindatu,hindatu''abinda ta fada kenan cikin zuciyarta ta juya ta koma cikin gidan.
Kitchen ta shiga kai tsaye da zummae dora musu girk
in dare,saidai abun kunya ta tadda mami harta kammala ta adana cikin warmers baaba uwani na gyara kitchen din,cikin kunya ta fito ta koma dakinta,wanka ta shiga tayi kana ta fito ta sauya wasu kayan,doguwar riga ta sanya ta atamfa wadda ta kamata daga sama
daga qasa ta bude sosai,ta mata kyau qwarai cikin ragiwar dinkunanta ne na fitar biki da bata kammala sakawa ba.
Mami na gaba abdallahn na gefanta,security din abdallah ne guda biyu riqe da akwatunansa,yayin da ita kuma ke binsu a baya a haka suka is
a harabar gidan inda dalla dallan motocin da gwamnati ta sakewa abdallah guda biyar ke jiransa wadanda da su zasu rakashi airport su kuma su wuce abujan su hadu a can.
Duk suka shafa addu'an da mami ta gama jero masa kana ta dan matsa don basu damar s
allama,hakan yakeso don dama tun dazun idanunshi na cikin nata,moment nasu na dazun kawai ke masa kai kawo,ji yake kamar ya dawo da hannun agogo baya,hannunshi ya miqa mata idanunshi fal so qauna da bege,a kunyace ta miqa masa nata hannun,cikin motar ya ja
nyota a tausashe,saura kadan ta fada cinyarsa ya rungomota jikinsa kana ya miqa hannu ya rufe
murfin motar driver najin haka ya kunna motar ya jata,mami na can suna magana dasu ibrahim sai gani tayi har motocin sun fice.
Gam gam ya hade hannayensu waj
e guda kana ya kwantar da kanshi kan kafadarta,yadda bata ce komai ba shima haka,kowannensu da abinda yake saqawa ranshi a haka har suka isa filin sauka da tashin jiragen sama na malam aminu kano dake nan kanon dabo
Ahankal motocin suka koma tafiya kasanc
ewar sun fara shiga cikin airport din,sai a sannan ya fara magana
''ina fata zaki cika zuciyarki da soyayyata kamar yadda tawa take cike da taki kafin na dawo,duk da na sani cewa ko a yanzun ma nasan cike take din saidai dama da aka hanata,abu daya da zan
gaya miki maryam am sorry to say bazan iya cika miki alqawarin da na daukar miki ba,bazan iya sakinki ba maryam har *ABADA* ke din tawa ce''ya qarashe maganar yana daga kansa dagq kafadarta,wata farar envalope fara qal ya ciro daga aljihun suit dinshi ya
bude tafin hannunta ya saka mata,dai dai lokacin da motar tasu ta tsaya aka bude masa murfin.
''Allah ya qaddara saduwarmu,sai Allah ya dawo dani,kimin addu'a don muhimmin aiki zan gabatar wanda koda shine aiki na qarshe da zan aiwatar insha Allahu sa
i na gabatar da shi,alhj hamza ya jima yana cutar da society dinmu,ya dade yana ha'intar qasarmu yana lalata rayuwar matasa maza da mata,yana shigo da mugayen makamai da qwayoyi,in sha Allahu wanann karon qarahensa yazo,ki saka ni a addu'o'inki,idan kuma n
a mutu shikenan sai a darus salam''
wata muguwar faduwa gabanta taji yayi,a hankali ta furta
''Allah ya tsare,Allah ya bada sa'a''saidai bata san ya ji ba ko baiji ba don ya fice da hanzarinsa ganin sun kusa makara yana baiwa driver din da ya daukosu uma
rnin ya fara maida masa ita gida sannan su kama hanya,binsa tayi da kallo shi da security dinsa har ta daina ganinshi,drivern ya dawo ya rufe murfin kana yaja motar
Batasan dalili ba kawai dai taji zuciyarta ta hade envalope din da ya bata tayi tsakiy
ar hannunta tana jin qamshi na fita daga jikinta
*mrs muhammad ce*
π
πππ
β
π½
β
π½
β
π½
ππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
πΊ
*ABADAN*
πΊ
ππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
ππΊππΊ
ππΊπ
πΊπ
π
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI
MUSA HUGUMA*
πΊππΊππΊπ
πΊππΊπ
πΊππΊ
ππΊ
π
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*
π‘
*_home of expert and perfect writers_*
βΆ
5
β£
8
β£
*Daga abu hurairah R.A yace:Manzan Allah S A W yace''na haneku da
yin hassada,domin hassada tana cinye kyawawan ayyuka kamar yadda wuta take cin karmami(yayi,itace)*
Cikin motar laqwas jikinta yayi gaba daya,tana jin wani abu mai kama da kewa na shigarta kamar wadda aka cirewa wani muhimmin abu daga sassa
nnin jikinta
Dakin ta ta wuce kai tsaye ta fada gado tayi ruf da ciki,kasala take ji da canjin yaynayi cikin jikinta,sai taji gidan ya mata fayau kamar ita daya ce a ciki,ganin matuqar taci gaba da zaman a haka kasalar zata rufeta da gasken ya sanyata
miqewa ta fito kai tsaye tayi sashen baaba uwani
A tsakar gidacta tatar da ita kan tabarma tana gyara zogale,kan tabqrmar ta isa itama tasa hannu tana tayata suna hirarsu,qarar wayarta ya katse musu hiran kiran raliya ne,tana murmushi ta daga sanan t
a mata sallama
''maraaba da dawowan diyana''cikin sauti mai dauke da farinciki ta maida mata amsa
''uwar gida kuma amaraya agidan muhammad nasir''
dariya itam tayi cike da nishadi
''a wannan kirarin ai sai ku,ku da ludayinku ke kan dawo''
sai da suka
gama zolayar juna kamar yadda suka saba sannan suka fara gaisawa
Hira sukayi mai tsawo wadda har baaba uwani ta kammala gyaran zogalen ta kwadanta basu gama ba
Har bayan magariba tana gun baban suna hirarsu,sai sallamar mami kawai sukaji
''zuw
a nayi na duba dama,nayi zaton bai dawomin da ke ba''
kunya ta kamq maryam din ta sunkuyar da kai tana murmushi,tana idar da sallar isha'i ta yiwa baba sallama ta koma bangarensu
Ta kammala shirin naccinta tsaf ta haye gadonta,saidai ko guda baccin d
a take da muradin yi bata ji alamunsa,wata iriyar kewa da madaici na daban take ji na damunta,juyi take tun daga farkon gadon zuwa qarshensa,tayi hakan yafi sau a qirga,tana son qaryata kanta kewar abdallah take saidai ta gaza,sai ta tsinci kanta da muradi
n jin muruarsa saidai ko kadan ba zata iya kiransa ba,hasalima bata tunanin akwai lambar wayarsa cikin wayarta,ta miqe a hankali ta jawo side drower ta ciro envalope din da ya bata dazun,dawowa tayi kan gadon ta kwanta ruf da ciki,a hankali ta farketa,kudi
ne sababbi fil a miqe yan dubu dubu masu yawa suka fado,yar qaramar takarda ce maqale jikin bandir na kudin,ta cirota ta budeta,karo na farko da idaninta suka ci karo da kyakkyawan rubutu wanda bata yaba ganin kamarsa ba
''kiyi amfani da su idan buqata t
a taso miki,love you so much my sugar''
dunqule takardan tayi ta dorata saman kudin
Ta sake bude cikin envalope din take taci karo da wata takardar fara qal mai adon furanni wadda ba shakka itake tashin qamshin nan,ajjiye envalope din tayi kana tasa
hannu biyu ta ware nadin da aka yiwa takardar,sallama ce a farkon takardar cikin kyakkyawan rubutu da harshen larabci
_qoqarin mantawa da wanda kake so is like trying to remember some one you never meet,i know we feel d same baby saidai bansan me ke yaw
o cikin zuciya da ruhinki ba,dont let your ego stop u from doing whats right,duk abinda nayi nayi ne saboda ke,duk abinda kike gani na miki laifi a akansa saboda ke na aikata,sonki ne sanadi baby,i cant express my feelings a kanki baby,ban taba sanin haka
so yake na sai a kanki,zan iya cewa kai tsaye ke kika koya min so,nasan kina tunanin na auroki ne kan tilas,ba haka bane na aureki saboda sonki da qaunarki da nake,nayi tsammani zaki qini zaki qi sona hakan ne yasa ban nemiki kai tsaye ba,but sorry for hur
ting u baby_
_kalmomi na sun bata ranki hakan ya sa kika riqeni,na sani na kuma san na fada,but banda ke baby baki ciki amma duk da haka am sorry again for my words and action last time,ina sonki baby ina sonki,am not with you to play games,ina fatan
komai zai gyaru kafin dawowata,bazan iya jurar rasaki ba bazan iya ba,zanso ace ko yaushe kina tare da ni,baby ina da qarfin buqata tun ba yau na na sani,idan kika qi ni bazan iya sakinki ba duk tsanani matuqar ina raye amma ina fatan bani dama nayi aure,k
oda babu komai tsakaninmu ganinki da zamanki a matsayin matata kawai ya wadatar da ni,ke ta dabance baby ki yarda,inajin komai nawa daban duk lokacin da muke tare,am feeling safer when iam wrapped up in your arms then ever
before,duk lokacin da nake kusa d
ake baby am overwh
elmed with happiness,kin soni kin ceceni kin kubutar da ni kin kuma tserar dani,shin wannan ba so ne ba baby
οΌ
bai isa a kira waannan so ba
οΌ
,so mai ma kuwa mai tsada,so mai cike da sadaukarwa da fansa
οΌ
,kin min abinda 'yammata da yawa suka k
asa min,na haqiqance u are what i have been waiting for my whole life,so na haqiqa so na gaskiya,kina sona ba tare da kinsan ma kina sona din ba baby_
_alhamdulillah finally a found someone who loves me just for me,ba don wani abu da nake da shi ba,bu
t ban manta ba i promise sai na ninka sona cikin zuciyarki fiye da da,nasan nayi nasara duk yadda kika kai ga boye hakan alredy na ganahi cikin idanuwanki koda zaki qaryata ni,abu na gaba shine ki fadamin shima na tabbatar miki cewa sai nayi nasara nayi al
qawari,TO THE MOST BEAUTIFUL GIRL IN D WORLD,AM SORRY BABY,_
Lumshe idanunta tayi tana jin wani abu da bata taba jin irinsa ba na ratsata,gaba daya abdallah ya gama kasheta,muguwar kasala ce ta lullubeta,sai ta ninke takardar ta lalubo jakarta da take
ajjiye muhimman abubuwanta zata jefa ciki idanunta suka sauka kan takardar,takarda ce data dauketa washegarin daren da abdallah ya fara cuta,sam ta mance da ita,da sauri ta daukota ta bude ninkin da tayi mata,rubutune mai kyau kamar wancan saidai bai kai
yawan wancan ba
_idan da kina da masaniyar tun yaushe na fara sanki ba zaki nemi abdallah ya rabu da ke ba,na soki a lokacin da bakisan akwai mai sonki ba cikin duniya,maryam tun kina 'yar secondry school na fara sonki,cikin kulawaata da sa idona kika
kammala universty dinki,can you remember sau nawa kike zuwa registration ace miki an dau nauyinki saboda hazaqarki cikin dalibai
οΌ
,zaki iya tuna samari nawa kika yi suka tafi basu sake dawowa ba
οΌ
,har kina tsammani ko matsala ce daga gareki,kin kusa auren j
abir a lokacin bani qasar nan ban sani ba na tafi jinya na gubar da naci london,cikin qurarren lokaci na samu labarin hakan ina can,sauran qiris na rasa raina san da na samu labarin zakiyi aure amma da yake Allah na sona ya tsinke lamarin,dalili kenan da n
a nemi sabon mai dafa min a binci saboda na sani bangarenki ne........._
Iyakar rubutun dake ciki kenan saidai tasirin da ta yuwa zuciya da gangar jikinta mai yawa ne har ta kasa zama ta miqe tsaye,da gaske abdallah yake
οΌ
shekaru nawa nufinsa yana tare
da sonta,abdallah ya dade tare da ita ba tare data sani ba
A hankaki wasu abubuwan da suka dinga faruwa da ita a baya suka dinga fado mata,sautari akan tsaya da mota ta alfarma da niyyar rage mata hanya,a lokacin haushi da takaici na kamata ne don tana t
sammanin 'yan kama wuri zauna ne kawai wadandq suke barewa duniya gyada taci keson hilatarta,saidai bata taba katarin ganin fuskar abdallah cikinsu ba,duk cikin nashi salon game din ne kamar yadda ya mata kan ABDUR RAHIM
οΌ
.
sai kawai taji murmushi ya s
ubuce mata
abdallah
οΌ
abdallah
οΌ
,wanne irin mutum ne kai abdallah,basira da wayinka sun isa,you have play good game with me''ta samu kanta tana fada cikin zuciyarta,sai ta koma bakin gado ta zauna tana tuna abubuwa masu yawa a wancan lokacin,tasha ganin ab
ubuwa masu yawa da suka sa ta dinga jin tsoro har take ganin ko jinnu gareta
Wayarta dake silent taga tana haske,ta miqa hannu ta daukota daga gefan pillow,baquwar number ce,sai data daga kai ta kalli agogo qarfe sha biyu da minti goma sha biyar na da
re ,ta maida kanta kan wayar tuni har kiran ya tsinke,tana shirin maida wayar wani kiran ya sake shigowa,da tayi kamar ba zata daga ba daga qarshe ta daga din ta kara a kunnenta kana tayi shiru don tantance waye
''assalamu alaikum''muryar abdallah ta daki
dodon kunnenta,kasa zama tayi sai ta sulale ta kwanta ruf da ciki saman gadon saboda wani makami da ya aikowa zuciyarta,sake maimaita sallamarsa yayi wanda wanann karon sai da ta lumshe idanunta,lebanta ne suka amsa ba tare da ko wane harafi ya fita ba
'
'baby nasan kina jina,zuwa yanzu na tabbatar kin karanta saqona''itama so take ta dan rama ko yaya ne kafin ya dawo kano,muryarta low sosai wanda ko kai dake dakin babu lallai kaji me take fadi
''ban duba ba,don bani da time na duba takardu''murmushi ya s
aka mai sauti da wata 'yar shashsheqa wanda har sai da ta jiyo shi,tsigar jikinta ta zuba
''baby,baby,baby,kullum kina yiwa kanki qarya me yasa
οΌ
,i know tuni saqona ya isa,ko kice eh ko kice a'ah,na kira ne dama naji muryarki ko zan iya bacci,sai nakejin d
ama mu koma qauyen ni'ima muyi zamanmu,atleast acan zamu dinga kwana daki daya,idan da rabona ma sai in kwana cikin ni'imtacce jikinki,baby na kasa mance moment namu na dazun ina jin kamar ya dawo,i want feel you beside me,i want to feel your lips......on
my neck and.....baby i want.... Iwant''ya fadi kamar mai tsoron magana
''i want to run my head along your chest,kiss your lips....''ai bata iya jumurin sauraronsa ba ta katse kiran nasa ta jefa wayar gefanta bayan ta tsura mata ido
Tana kallin kiran
nasa amma bata jin zata iya dagawa yaci gaba da horata babu gaira babu dalili,shi dole sai ya tada zaune tsaye,sai da ya hada mata missed call kusan goma sanann ya haqura,qarfe saya da kwata ta sauka a gadon ta shiga bandaki ta daura alwala tayi nafila rak
a'a biyu ta kwanta,tunani ne fal