Showing 123001 words to 126000 words out of 176330 words
babu kowa a dakin nata sai ita kadai,suna tsaye har ta sallame,duk da batasan kosu waye ba da fara'arta ta karbesu
''ya zaku tsaya ku zauna m
ana''ta fada tana miqewa tare da ninke abin sallarta
sai data ajjiye musu ruwa da lemo kana ra dawo ta zauna mami nata kallon ta,take ta tuna mata da maryam dinta babu tantama ita tayo,kyau tsafta da kirki
Sun taba lemon kana suka gaisa,mami ta dubet
a
''nasan baki sanni ba hajiya''murmushi tayi
''gaskiya kam,ban gane fuskar ba''
''nice mahaifiyar abdallah surukinki''
Sabuwar gaisuwa suka sake yi da mamin cikin mutunta juna kana daga bisani mamin ta gabatar mata da abinda ke tafe da su,sosai mama t
aji dadi don ko mamin bata fada ba takowar da tayi ta fara neman yaran ya tabbatarwa mama sihirin dake jikinta Allah ya kawo lokacin karyewarshi
a nutse mama ta gaya mata inda su maryam din suke,fadar irin dadin da mamin taji bama ita kadai ba harda baab
a uwani bata baki ne
''ba shakka gobe zan je na dauko yarana,alhmdlh Allah na gode maka''
a take ta daga waya ta kira baffanta ta sanar masa,cewa yayi ta jinkirta zuwa goben,don bai kamata kai tsaye a dawo da su din ba,akwai abubuwa da ya kamata mafin da
wowar tasu,baya ga haka magani yake karba,ta bari nan da wasu yan kwanaki idan ya gama tsara komai zai mata maganar
Bata musa din ba saboda tasan baffab akwai hangen nesa,cikin farinciki da zumudi suka baro gidan zuciyoyinsu fal farinciki da godiya ga
Allah,ba qaramin qimar mama mami ta sake gani ba data hada diyarta da danta ta kaisu ga mafaka cikin ikon Allah,sosai ta kuma ganin qimarta
ππππππ
Washe gari hisham ya shirya don komawa katsina,yanason duba company din abdallah guda biyu dake
can wanda abdallan yace a fidda wa ma'aikatan companies din salary dinsu tunda wata yazo qarshe
Kai tsaye ya isa dakin tsoho alhaji wanda dama abdallah na ciki suna tare bayan gama shan rubutunshi wanda ya zama shine ruwan shansa a yanzu,yana duqe g
aban tsohon
''banda abunka hisham tafiyar dare ai sam bata da dadi,da ka jinkirta zuwa gobe''cewar tsoho alhaji da yaje yiwa sallama,murmushi yayi kanshi a qasa
''banso komawa ba ma malam,naso naga yadda jikin abdallah zai kaya duk da yanzun ma alhmdlh y
ana gayamin yana jin canji a jikinsa,tafiyar ce ta zo min haka amma insha Allahu kwana uku kawai zanyi na dawo''
''to shikenan Allah ya tsare hanya,a gaida manyan''
''ameen ameen,Allah ya qara girma''ya fada yana miqewa,ya juya ya miqawa abdallah hannu s
uka yi musabaha,inna wuro ta shigo da jarka biyi daya man shanu ne a ciki daya nono tace ya kaiwa gwaggonshi,godiya ya mata sosai kana suka juya dukka zasu rakashi bakin motarsa
hannunta taji an riqe da sauri ta juyo,abdallah ne,ya wani narke yana mat
a wani krin kallon dake sake karya duk wani makaman zuciyarta,tanajin da biyu yake mata irin wannan kallon
''baby maryam''
''abdallah mene haka''ta fada a zuciyarta
''inaji a zuciyata na kusa warkewa nan kusa,hakan na nufin mun kusa rabuwa
οΌ
''
wata mumm
unan faduwar gaba taji,ta lumshe idonta kana race cikin muryarta nai sanyi
''sun fita fa,ka sakarmin hannu muyi sallama''
''hisham ai ba baqo bane,gwara ki zauna nayita kallonki,naga alama da gaske so kike kifi qarfina,tun jiya rabona da na ganki,jiyan m
a batan kai nayi na sa kai na bandaki ashe kina ciki kina wanka''
Ba tare data shirya ba ta waiwayo tana dubanshi idanunta a waje,take kuma suka kawo qwalla,dama abinda yakeson gani kenan
''ina wanka
οΌ
,ba kaya a jikina kenan''
dariyar da bai shirya b
a ta subuce masa,ya dinga yi yana kallonta,sai yaga gaba daya ta kuma qaramar yarinya sosai da bazata wuce shekaru sha hudu ba
''wai ke kam shekarunki nawa,i thought ba zaki wuce twenty four ba,kamata yayi Allah a maidaki shekara goma,dubeki kamar wadda a
ka cewa saurayinta ne ya ganta''
ta lura ma ya maidata wata abar tsokanarshi bayan wasan kura da yake mata da zuciyarta duk lokacin da suka hadu
''Allah sai na gayawa inna wuro leqen mutane kake a bandaki...''
''a'ah,ba dai mutane ba gyara zancanki
yammata,leqen mata ta nake,sai kuma mero......''
''mero
οΌ
''
ta maimata sunan ba tare da tasan ta fada din ba
girarsa ya daga mata
''eh mero mana,itama matata ce baki sani ba
οΌ
''ai a,hanzarce ta qwace hannunta ta fice a dakin,dariyarsa yasha sosai yana ra
ina wayon maryam din da ta gaza gano abinda yake nufi
Ta gama shirin baccinta ciki doguwar riga mai sulbi mai hannun shimi maroon doguwa ce har qasa ta maida qaramin farin hajabinta jikinta ta haye gadon inna wuro tana karanto addu'o'in bacci,bayan ta
kammala ta ja bargon inna wuron ta lulluba zuwa qugunta bayan ta lumshe idonta
Da sauri taji an yaye bargon,ta bude idanunta inna wuro ce tsaye a kanta riqe da torch light donta kashe qwan solar din dakin
''me nake shirin gani meramu
οΌ
''
cikin rashi
n fahimta tace''me ya faru inna
οΌ
''
tana nuna qofar dakin nata da yatsanta tace''ki baro dakin mijinki kizo kimin qabe qabe kan nawa gadon da yake ni ba miji gareni ba ko
οΌ
''
fuska ta yamutsa
''kai inna,naga dai tsoho alhaji ai yana da turakarsa ko
οΌ
''
''iyeeee''ta fada tana kama haba
''to tashi ki barmin daki,idan yaso in kinga dama kiyi shimfida a tsakar gida ki kwana can''
ta sake yamutsa fusjar tana kallon innar ba tare da ta ko motsa da niyyar tashin ba
''kai inna ni wallahi kamar ma kwanan nan
kin tsaneni''
''eh koma me zaki fada ki fada amma saikin fitarmin a daki,dama kuma ni bana tarayya ai da mai kynnen qashi....zaki taahi ko sai na samo madoki
οΌ
''ta fada tana dube duben abinda zata dauka na duka din,tasan kadan daga aikinta yadda take qaun
ar abdallah yanzun ta maketan ta sauko tana guna guni taja bargon
''ajjiye min bargona,kuma kuna da shi''ta fada tana kallonta,tilas ta ajjiye mata din ta fito
tana gab da shiga dakin taji maganar tsoho alhaji yana fitowa daga dakinsa,ta qarasa cikin
girmamawa,wata 'yar farar roba ya miqo mata yana fadin
''da dakinnaki zani,tunda kuma gaki shikenan,wannan maganin banason ya wuce yau ba'a shafa shi ba,daga cinyoyin abdullahi zuwa yatsunsa na qafa,a tabbatar ko ina ya samu,kada ki barshi ya taba da han
nunshi don a qa'idarsa wani ke shafa maka,sabida jikin shi har yanzu akwai ragowar abinda aka yi masa''
''to malam,Allah ya qara girma''ya amsa nata ya juya ya koma dakinsa ita ma ta shige
kan katifar ta hangoshi zqune jingine da pillow,laptop ce kan
cinyoyinshi kallon wani film yake na tarihin sayyadina umar,vest ce a jikinsa da short nicker wanda iyakacinshi saman gwiwarsa,dauke kanta tayi da sauri,shima tunda ya amsa mata din ya maida kansa kan allon computer din,ta haura kan katifar ta dauki pillo
w qwaya daya,har zata sauka sai ta tuna da maganin
''tsoho alhaji yace a shafa a daren nan''ta fada tana miqa masa maganin
fuskarshi ba walwala yace
''wa kike son ya shafamin bayan na jishi yana gaya miki kada na taba
οΌ
''shiru tayi cikin rashin sanin ams
ar da zata bashi,bata ankara ba taji ya damqi hannun nata bayan ya ajjiye computer din tasa can gefe ya janyota yana fadin
''malama zauna ki shafa min''take kuwa ra samu masauki kan cinyoyinshi,qoqarin miqewa tayi take amma ya danne rigarta,yasa idanunshi
sosai cikin nata
''kika sake kika gudu....q'nnn,ni dake ne''ya fada cikin dakiya
''dagan rigarta to zan shafa maka''
bai amsa mata ba sai hannu da yasa yana qoqarin,zare hijabin jikinta,hannayenta ta hada ta cukuikuye hijabin saboda rigar jikinta m
ai fadin wuya ce bugu da qari kuma mai lafewa ce a jiki
kicin kicin yayi da fuska kamar bai taba dariya ba
''ki bar ganina a zaune bazan iya tashi ba,to kada ki kuskura na sa miki qarfina zaki sha wuya,daga ni sai ke a dakin,na bama kallonki zanyi ba,zan
cire miki don kada ki shafa min ba daidai ba ko ki bata hijabin naki,ki shafa min kawai idan kinso ki koma soro ma ki kwana''
ta gama amanna da gaske yake ganin uadda yayi maganar ba wasa a fuskarshi,sakin hajibin tayi yasa hannunshi ya zare shi ya ajjiy
e mata shi gefe
''fatabarakallahu alhsanul khaaliqin'' ya ambata cikin ranshi saboda ba qaramin kyau night gown din tayi mata ba
''tafaddal''yace da ita bayan ya tattare short nickers dinsa can sama,kallo daya tq masa ta dauke kai,bata taba ganin wan
i namiji a haka ba tunda take,santalan santalan fararen cinyoyinshi masu wadatar gargasa baqa suduk suka bayyana
ta lakato maganin mak kama da man kadanya ta mutstsuka a hannunta,tamkar wadda zata taba kunama haka ta dora hannunta kan cinyoyin nasa,sai da
ta runtse idonta kana ta fara shafa masa a hankali tamkar mai sanda
Shiru ya ratsa dakin dukkaninsu suna ji cikin jikinsu kada ma abdallah yaji labari,ajiyar zuciya ya dinga saki a bobboye idanunsa kan maryam wadda bata sani ba gaba daya wuyan rigart
a yayo qasa,tsuntsu biyu ya dinga jifa da dutse tsaya sam ita bata sani ba,har ta gama durqusan nata ta zauna sosai
dan jan qafar tasa yayi yana fadin
''kaiiiii'' da sauri ta dubeshi tana fadin
''da zafi''kai ua girgiza murmushi ya qwace masa don dama i
dn nata yakeson gani ya gani din ya kuma gano abinda yakeson ganowar
''nikam gaskiya da biyu kike min irin wannan shafar mero''
baki ta muguda masa
''kada ka sake bani sunan wannan baqaiyiyar budurwa tak,ni ba suna na kenen ba''mirmushi ya kuma saki sab
oda tsabar iya tsokana
''ke da ita din ai duka jirgi daya ya kwasoku,gwara ma ita tunda ta iya ta sace miki miji''haushin da ya bata yasa ta kasa tanka mishi,sai qara speed din shafar da take masa da tayi
ya sake fadin
''wayyo Allah''bata ko kula shi ba
har sai data gama ta rufe man tana shirin miqewa sai ya sake fincikota jikinsa baki daya ya matseta,tana sonvta qwace amma yaqi don riqon tsauri yayi mata
''ki hutar da kanki yau a jikina zaki kwana,ina zaman zamana kin jawomin,dole ki ragen zafi kafin n
ayi aure tunda ke kika jawo komai''
Da gasken kuwa yake don tuni har ya fara sakin layi,hannunshi ta riqe tamau tana kiran sunansa,a hankali ya janye hannunshi yana fadin
''am sorry na manta''ya fada yana kissing goshinta kana yaja musu bargo ya rufe
su,tun tana a darare a jikinsa har ta saki jikinta jin shiru bai qara motsawa ba,da alama ma bacci yayi awon gaba da shi,don dole ta saki jikinta amma still tana jin yadda zuciyarta ke gudu,daga bisani ita din ma wani daddadan bacci ne ya sureta
*mrs muhammad ce*
π
πππ
β
π½
β
π½
β
π½
ππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
πΊ
*ABADAN*
πΊ
ππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
ππΊππΊ
ππΊπ
πΊπ
π
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πΊππΊππΊπ
πΊππΊπ
πΊ
ππΊ
ππΊ
π
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*
π‘
*_home of expert and perfect writers_*
5
β£
4
β£
*_Allah yana cewa cikin alqur'aninsa mai girma''haqiqa ji da gani da zuciya dukkansu akwai tambaya a kansu''(ranar qiyama
game da abinda suka ji ko suka gani)_*
lokacin da mami ta koma gida ita da baaba uwani bayan tayi horn an dage mata makeken get din gidan ta wuce ciki sai ta lura duka ma'aikata da security na gidan na tsaye ne cirko cirko a guri guda
kan t
a fito daga cikin motar ibrahim ya qaraso cikin girmamawa
''lafiya ibrahim,me ya faru na ganku a tare guri guda
οΌ
''
mamin ra fada tana kashe motar tare da qoqarin fitowa daga ciki
''wallahi mami hajiya nene ce
οΌ
''
''nene
οΌ
,me ya faru
οΌ
''ta tambaya d
on wata irin tsanarta tame ji na mamaye zuciyarta,macan da ta jefa tilon danta cikin bala'i,macen da taso ganin bayan su ita da yaran da tafi qauna abdallah da maryam,ta mata alkhairi ita kuwa ta maye gurbinsa da sharri,ta zauna da ita zuciya daya yayin da
ita take zaune da ita da ziciyoyo barkatai marasa kyawun manufa,ko a mafarki daidai da rana daya bata taba qullatar nenen da sharri ba sai gashi abun mamaki ita din taso abzata cikin wani rami mai tsananin hadari badan Allah ya dibi ysarkin zuciyqrta ba y
a tsallakar da ita daga dukkan wasu tarakuna data dana wa rayuwarta
''ina baya ina rangadin gidan su husaini kuma suna nan zaune da sauran abokan aiki,kawai saiga husaini yazo yayi kirana waiga nene can babu ko kaan arziqi sai daurin qirji ta fito a g
uje daga bangarenta wai fita zatqyi nemansu adnan,kuma idan ta gansu sai ta kaagesu don sun cuceta sun ha'inceta sun gudu da dukiyarta,da farko na zata ma qarya yake saboda naga ko motsi bata iyawa komai sai an mata,amma da na bisi sai na gasgata maganarsa
,to muna shawarar yadda zamu hanata fita sabida kowa yana tsoron tabata tunda ba muharramrsa bace kawai sai ta faki ido ta fice a guje,muka bita tuni har ta fita daga gidan,muna daf da zamu cimmata wata mota ta tsaya,wadan nan mutanen da kika ce kada mu sa
ke barinsu kwanaki su shigo gian nan sune aahe a ciki suka figeta suka jefata ciki,na sa bindiga na harbi tayar har sau biyu saidai ban samesu ba''
shiru mami tayi tana jinjina kai,ibrahim ya kuma cewa
''amma mun dauki nimber din motar,gata''tsaida
shi tayi
''babu bin sahunsun da zamuyi ibrahim ka qyaleta da su,qila hakan da Allah ya mata shine mafi alkhairi a gurinmu,bata dace da zama cikin mu ba shi yasa Allah ya hadata da mutanen da suka dace da ita''tana maganar ne
yanayin fuskantar ya sauya sab
oda bacin rai da tashin hankali,ibrahim ya dubi mamin,shekara da ahekaru suna zaune tare,macace mai tausayi jin qai da taimako ga na qasa da ita,ya tabbatar ba qaramin abu bane zai sanyata tace a qyale nene ba,duk da idanuwansu sunga wasu muggan ayyukan na
nene da yadda ta so maida uwar dakin tasu mamin amma ya tabbata da abinda ta aikata din yafi haka,take kuwa ya cukuikuye takardar ya yagata gutsi gutsi
''ku koma bakin aiminku ibrahim,kowa yasa cikin zuciyarsa tamkar ma baiga abinda ya faru,irin nata huk
uncin da Allah zai mata kenan,don na tabbatar ba mutanem arziqi ne suka dauketa ba,kowa ya shuka na gari kai nasa''
''gaskiya ne mami,Allah ya shige gaba''
''ameen''ta fada tana juyawa cikin gidan,cikin zuciyarta tana qara jin imani kan cewa duk abinda z
akayi kayishi domin Allah,matuqar kace don wani zakayi shi to kana tare da wahala,zaka kyautatawa mutum iyakar iyawarka da zuciya daya amma shi sam bai gani,qarshe ya buge da cutar da kai ko ya shiga sahin manyan maqiyanka na farko,amma idan kayi ne don Al
lah koda shi din wanda ka yiwan bai gani ba baka da kaico ballantana asara zaka samu ladan aikinka ne gaba ga Allah,Allah kasa mu dace,ka bamu ikhlasi
Sai data sake wanka tayi sallah tana kan abun sallar ta dau wayarta ta kira daya cikin qannenta sa'a
diyya sukayi magana kan saukar qur'ani da aka raba makarantu makarantu,ko dq can lokacin marigayi alhj abdul-kareem mai nasara an musu,bayan mutuwarshi ne daga baya ta watsar,a yanzu kam ta dauki dambar ci gaba da sawa ana mata don ta fuskanci duk yadda ka
kai ga kirkinka kamun kai da kayuatatawa mutane wani yana nan duk duniya babu wanda yaqi jini sama da kai koda naman mahaifiyarka zaka dinga yanka kana dafawa kana bashi yana ci tsabar so,sadiyyan ta gaya mata an kammala kaso na farko gobe zasu dora kana s
ukayi sallama
cikin 'yan uwan nenen mami ta nemo matar babanta tace suzo su kwashe duk wani abu da ya danganci nene daga gidan don tuni kowa ya sani alfarma karamci sa darajar zaman tare yasa mami ta bar nenen a gidan,matar baban nata cewa tayi gaskiy
a babu abinda ya shagesu da kayan nenen,don bata manta irin cin mutuncin da tayi musu kan gadon mijinta na farko,hatta da mahaifinta ya dade da zare hannunsa cikin lamuranta
mamin tace dole kam su debe don sun gama zama tare da nene
matar baban nata ma y
aba mata sukayi zaman datayi da ita don sunga namijin qoqarinta ma data zauna da ita ba dangin iya babu na baaba tsawon shekarun nan
Da qyar suka zo suka debe komai na natan suka loda a kodi kura,part din ya koma wayam babu ko tsinke nata bare na 'ya'
yanta,sai a lokacin mamin ta fara jin sanyi cikin zuciyarta
''na barki da Allah nene,ko iya haka ma ya ishi yan baya ishara''abinda mamin tace kenan
ππππππ
Qal gidan yake a share kamar kowanne lokaci,rairayin filin gidan tas kamar an zauna a
n tsince dattin cikin,banda shati shati na tsintsiya da alamun yayyafar ruwa da suka sa qasar ta danyi danshi da qamshi babu komai
gidan shiru yake kasancewar babu kowa sai ita da abdallan kawai,inna wuro ta je cikin garin gaya bikin sunan wata jikart
a,tsoho alhaji kuwa kano ya tafi karbo jakarsa a hajj camp da yake kayan sun dan samu tsaiko sai ranar suka iso,ya dauki mustafa suka tafi tare don yafi jin dadin tafiyar
qasan rumfar yake a zaune kan wheelchair dinsa sanye da baqar t.shirt da red din
trouser mai sulbi da kyau,yayin da maryam keta kai kawo na hada abincin dare
idan ka dubeshi a haka sai ka zaci tabbas karatunsa yake tuquru saidai ina zaman sa'ido yayi don da zarar ta kuya zqi zuba mata ido har sai ya fuskanci tana shirin sake waiwayo