Showing 90001 words to 93000 words out of 176330 words
san sun gama da mami,bata da ikon hanasu komai sa
i abunda suka shomfida,babu wani abu da zasu iya yi mata,addu'a zamu bita da ahi kafin mu samu nutsuwa mu zauna mu samar da mafita,don tabbas akwai abinda ke faruwa,na tabbatar mummunan qulli ne a binne a qasa wanda bamusan inda yake ba sai Allah''
Ci
kin nishadi nene ta sake dawowa bakin get din zuciyarta na sake kururta mata ita mai nasarq ce,korar hisham da maryam daga rayuwar abdallah cikin lokacin da take qoqarin kau da shi ba qaramar nasara bace don a idonta maryam ta fita,sake tambayarsu tayi don
tabbatarwa suka amsa musu eh itace
''goo,itama bana son ta sake shigowa cikin gidan nan ko ita ko wani nata har abada''kallon juma suka shiga yi don dukkansu sunsan wace maryam cikin gian sun san matsayinta,ganin suna son saka tantama cimin ranau yasa ta
daka musu tsawa
''ko baku jina ne,wallahi zan iya yiwa mutim kowanne irin hikunci matiqar ya saba umarni na,kubar ganinku garada''ta musu wani kallo na izgili,da sauri suka amsa suna bata haquri,juya watayi tana fadin Allah yasa daya daga cikinsu ya saba
wa umarnin ta
sai da ta dubi bangaren abdallah ta qyaqyace da dariya
''Allah ya jiqanka abdallah,taka kuma ta qare,wataqila kafin gove azo gamawa da kai yunwa da qiahirwa sun zama ajalinka''ta wuce sashenta tqna wani irin taku cike da nishadi da jiyo
qamshin nasara
*mrs muhammad ce*
π
πππ
β
π½
β
π½
β
π½
ππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
πΊ
*ABADAN*
πΊ
ππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
ππΊππΊ
ππΊπ
πΊπ
π
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πΊππΊππΊπ
πΊππΊπ
πΊππΊ
ππΊ
π
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*
π‘
*_home of expert and perfect writers_*
βΆ
4
β£
4
β£
*_An karbo daga abu hurairah R A yace:Manzan Allah S A W yace:babu wata rana da gari zai waye face
sai mala'iku biyu sun sauko,sai daya daga cikinsu biyun yace ''YA UBANGIJI KA BAWA WANDA YAKE CIYAR DA DUKIYAR SA NINKIN ABINDA YAKE DA SHI'',dayan kuma sai yace''YA UBANGIJI KA BAWA WANDA YAKE QIN CIYAR DA DUKIYARSA ASARA A CIKIN DUKIYAR (WANDA YAKE ROWA
BAYA CIYAR DA ITA GA MABUQATA DA MASU NEMAN TAIMAKO)_*
πππ
*ina taya daukacin al'ummar musulmi murnar shigowar sabuwar shekarar musulunci,dukkan wani alkhairi na duniya da lahira dake cikin shekarar ka
hadamu da shi,ka kare mu da dukk
an wani musulmi da sharrin dake cikinta,ka bamu lafiya da zama lafiya da kwanciyar hankali da yalwar arziqi ameen*
Daf da zata qarasa bangaren nasu tana ci gaba da babaka dariyarta suka ci karo da baaba uwani,wata uwar tsawa ta daka mata
''in
a zaki je uwar kinibibi
οΌ
''
jikin baaba uwani na rawa tace
''ah....ummm...zani mi gaisa da hajiya ne
οΌ
''
tsatstsareta nene tayi da idanu
''me nace dake tsohuwar banza
οΌ
''
''ahh...kince....kince ne kada ki sake ganina bangaren ku indai ba inaso ma rasa ai
ki na ba'' gyara tsaiwarta tayi
''kin shirya rasa aikin naki kenan
οΌ
''
girgiza kai ta shiga yi
''a'ah,don Allah hajiya nene kiyimin afuwa''
''kinsan me nakeao dake
οΌ
,matuqar bakison rasa aikinki cikin gidan nan kada na sake ganin qafarki a harabar gidan
nan,daga yau ziwa gobe jibi ke har gata ma,kina jina ko
οΌ
''
da sauri take gyada kanta ,kana ta bata umarnin ta koma inda ta fito
hawaye ne kawai ke zuba daga idon nene tana sharewa,idan banda darajar mami da take tausayawa babu abinda zai zaunar da it
a a gidan,abubuwa marasa dadi da idanunta ke gane mata wanda ke faruwa shine ummul aba'isin zamanta cikin gidan badon wani abu ba
πππππ
babu wanda ya sake cewa komai har suka qarasa gidan hisham din,gida ne madaidai ci mai kyau wanda ke dauke da
makeken falo kitchen dining area sai dakunan bacci guda hudu
A falo suka tadda abdallah kan kujera,gwiwarta a sanyaye ta qarasa gurinshi kanshi na duqe a qasa,a gabanshi ta durqusa ta sanya hannunta cikin nashi tana kallonshi,sam yaqi daga idanunahi
ya kalleta,hakan na nuna mata cikin tsananin bacin rai yake,ta leqa fuskanahi idanunahi biyu don tana iya ganin qiftawar idanunshi,sai zuciyarta ta karya ta tura kanta tsakanin cinyoyinsa da fuskarsa sai a sannan suka hada idanu,ya zuba matq idanun naahi d
a suke har yanzu kalar ja
shigowar hisham falon ya sata miqewa,ya taimaka suka shiga da abdallah daya cikin dakunan dake falon,dakine mayalwaci mai hade da toilet,gado madubi side bed sai cupboard da kujera doguwa qwaya daya da carfet da ya malale qas
an dakin da shi a maimakon tiles
''zan fita amma bazan jima ba zan dawo''
ya qarasa gaban abdallah yace
''abokin sai na dawo mintina kadan zan dawo''kai kawai ya gyada masa ya miqa masa hannunshi sukayi musabaha
π²ππ²ππ²π
Qarfe goma na daren ra
nar suka fito daga maboyar da nene tayi musu cikin dakunan barcinta,gaba dayansu baqaqen kaya ne ajikinsu hatta da mask din da suka sanya,kowannensu wuqa ce boye a jikinsa
taku daya biyu nene tayi ta tsaya a gabansu,dukkansu sun fita tsawo nesa ba kus
a ba,ta dubesu daya bayan daya
''banason a samu kuskure ko sabani cikin aikin nan,shekaru na kwashe masu yawa ina neman wannan damar,saboda haka ku tabbatar komai ya tafi yadda ake so''
dqya daga cikinsu wanda da alama shine oga ya buda hanci ya shaqi is
ka
''haj,sanin kanki ne munsan aikin mu dalilin da yasa kema kika neme mu kenan''
gyada kai tayi
''haka ne kam''
da daya da daya suka dinga fita har suka isa sashen abdallah,jijjiga qofan suka yi suka jita gam hakan ne ya tabbatar musu a kulle tak
e,don haka kansu tsaye ba tare da wani tsoro ko shayi ba tunda sun san cewa babu security ko daya cikin gidan bare su jisu duka nenen ta bawa kowa aikin da har su gama abinda zasuyin ba zasu riskesu ba,take suka hau lallauya qofan da wani shegen qarfe suka
ajjiyeta saahe guda kana suka kutsa ciki
Sau uku yama luma wuqa kan tarin filallukan dake tare a kan gadon ganin qamas babu alamun jini ya sanya su yaye bargon,a mamakance suka kalli juna kana daya daga cikinsu ya ciro waya ya kira nene,da zumudinta
ta daga kiran ga tsammaninta sun cika aikinsu
cikin mamaki da fushi take fadin
''wanne irin babu kowa
οΌ
kada ku gauamin maganar banza mana,yaron da ko motai bai iyayi ina zaije
οΌ
,kuma tun jiya babu kowa a tare da shi balle ace ya fidda shi
οΌ
''
cikin ciccije
wa ya maida mata amsa
''kinga hajiya duk ke kika san wannan,kizo kawai idonki ya gane miki''
da azama tq fito ita da zahariyya da danan suka bazamo bangaren abdallan,surutai take tayi kamar wadda ta samu matsala a qwaqwalwarta don bata taba sawa cikin li
ssafinta cewa wannan karon akwai cikas din da zasu samu ba
cirko cirko sukayi cikin dakin bayan kammala duba ko ina na cikin gidan ciki har uwar dakin mami wadda batasan me ake nema ba,ta dai ga nenwn kai tsaye ta ahige mata daki tana dube dube daga b
isani ta fito
''taya ya abdallah ya fita daga cikin gidan nan''
''ke za'a tambaya hajiya''cewar ogansu yana maida locker da tasa ya balle ta dakin abdallan wadda basuyi katarin samun komai ba sai rafar din dubu hamsin
''miqo min wadan nan kudaden,ya
nzu hatta da takardun kadarorinsa ma ace babu su cikin dakin nan,anya wani baisan abinda muka shirya ba kuwa cikin gidan nan,anya banu mai,mana labe da leqen asiri
οΌ
''ta fada tana zare ido kamar wata zautacciya
kudin ya kalla kana ya dubeta
''ban fajimci
me kike fada ba,wannna kidi ai namu ne ladan zaunar damy da kika yi nuka kwana cikin gidanki,ai lissafi zamuyi kawai ki cika mana sauran miliyan dayan da mukayi da ke zaki cika mana''
''idan aiki yayi kyau ba,ana ta kai wa yake ta kaya,kwananku kuma cikin
gida na ai ku kuka qaru da ni bani na qaru da ku ba asara ce ma ta hauni goma da goma,tunda har 'yata na baka ta tayaka kwana ko
οΌ
baya ga haka ma ni a yanzu bani da miliyan daya bani da dalilinta,da aiki yayi kyau ne ma na tabbata cikin dukiyar da zamu sam
u ba komai bane cire miliyan daya daga ciki ''ta fada tana matsowa gabansa tare da zazzare idanuwa,don ji take su suka ma ja mata duk wata asara da ta fada matan
Dariya ya sheqe da ita
''haba hajiya,kinci qarya kin kwana da yunwa,muba qananan makasa
bane ba irinnu akewa haka ba''ya sake matsowa inda take har tana jin warin wiwinshi na dukan hancinta,yatsunshi ya daga guda uku
''kwana uku kacal na baki ki turo mana ragowar kudinmu,wlh wlh wlh ko ke kikayo naqudata matuqar baki turo da sauran kudin nan
ba ke da 'ya'yanki ki tabbatar kuna cikin masifa,domin duk ranar dana waiwayeku sai kun buraci mutuwarku akan rayuwarku,na baku dama ku gaggauta warware harqallar da kuka qulla dani''
ya juya zai wuce adnan yasha gabansa cike da taurin kai da jin shi
ma karansa ya kai tsaiko yana ciccije lebe cikin son nuna shima jan wuya nebayan shi kansa yasan fanko ne lamba daya,kafin yace komai yasa kan wuqar hannunshi ya daki kanshi saiga adnan din a qasa,ihu nene ta saka tayo kansu,da tsinin wuqar ya juna ta ta k
oma baya tayi luf sai da suka kammala ficewa ta saka kururuwa ta biyo bayansu ko Allah zaisa taci sa'a wani daga cikin security din sun dawo suyi ram da su,saidai ina,babu wanda ta samu bakin get din kamar yadda ta watsa su don gabatar da aikinta
πππ
πππ
ta kai ta kawo tayi hakan ya kusa sau goma sha biyar,ji take kamar zata hau bori ko hauka kafin ta samu guri ta iya tsugunnawa,ta dubi adnan da kanshi yasha dauri da bandeji da zaharkyya wadda ke zaune tana faman hade fuska,babu wanda take ganin
laifi sama da nene,don ita kam ta gaji da wanna jeka ka dawo din,ta riga da ta yanke ma kanta hukuncin abinda zata aikata matuqar wannan karon haqarsu bata cimma ruwa ba kamar sauran lokutan baya
''babu shakka cikin hisham da maryam akwai wanda ya fidda a
bdallah daga cikin gidan nan,ko kuma daya daga cikinsun ya aikata hakan,kuma nafi zargin wanna shaidaniyar ce marya,tabbas kuwa''ta fada tana guada kai hadesake tabbatarwa kanta
''qwarai kuwa nene,nima na zargi haka tunda kinga fitarsu ana gobe za'a gudan
ar da aikin,cikinsu akwai wanda yake da hannu kan tsirar abdallah''inji zahariyya,shikam adnan ya kasa magana ta kanahi yake,tsanin ciwo yake masa kamar zai tsage gida biyu har
zumbur nene ta miqe tana fadin
''wallahi basu isa ba dukkansu,duk wanda yaci
tuwo da ni miya yasha''
ππππππ
Tana cikin kitchen tana qoqarin hada masu abincin rana ta jiyo hisham na qwalla mata kira,cike da mamaki ta ajjiye abinda take yi din ta fito don bata taba jin ya mata makamancin irin wanna kiran ba
tashin hanka
li ta gano qarara cikin idanunshi
''dauko duk abinda kika san kina da buqata ki sameni a mota na riga da na kai andallah ciki,babu lokacin bayani na miki shi a hanya''
bata tsaya tambayar ba kuwa,ta koma kitchen din a gurguje ta kashe gas din ta ahiga da
kinsu da suka sauka ta dauki iya abinda take jin zata iya buqata ta fito ta taddasu cikin mota
Tafiya yayi ta kusan mintina hamsin har suka fara barin ainihin qwaryar birnin kano sanna yayi parking a nutse ya dubeta
''maryam,na samu bayanan sirri dag
a daya daha cikin security din gidansu abdallah wanda nake biyanshi bayan barinmu yake samin ido kan duk wani motsi da yanayi da gidan ke ciki,don na tsammaci dama lallai wani abu na iya faruwa kan barinmu gidan da abdallah da mukaui,hasashena kuwa ya tab
bata ya zama gaske iya,suna na ne ma farko cikin jerin mutanen da nene ke tuhuma,don ta saka amata bincike kan inda nake,yanzu haka mutanen na kan hanyarsu ta zuwa gidana,dalilin barowarmu gidan kenan''
kuka ne ya qwacewa maruam,wannan wace iriyar mac
e ce nene
οΌ
me ta dauki rayuwar duniya,baza'a mutu ba
οΌ
dawwama kowa zaiyi yana abinda yaga dama
οΌ
,me take nema ne cikin duniyar da dukkanta bata kai qima da darajar fika fikin sauro ba agun Allah,wanne jin dadi ne a ginta ta kashe ran mumini wanda qimatsa tafi
ka'aba agun Allah
οΌ
,tana tsammanin idan ta aikata hakan taci bulus ne ko kuwa,zata taira daga hisabi da zabar Allah ne
οΌ
dukkan amsar itace a'ah,babu
''a halin da muke ciki maryam kuka babu amfanin da zai mana,ki tsaida kukan mu nemi mafita''
tabbas ma
ganar hisham haka take,ba bata lokaci ta ciro wayarta ta sake kiran mama wadda basu yi awa biyu da yin waya ba,magan sukayi ta kimanin minti talatin da ita kana ta kashe wayar ta dubi hisham kasancewar handsfree ta saka yaji komai
kansa ya gyada
''magana
r mama gaskiya ce,kuma tsarin nata yayi,nima da mun isa gobe zan wuce katsina hometown namu''ya fada yana mai gamsuwa da bayanin maman
yana kuma sawa motar key,ta juya ta sake kallon abdallah har yanzu idanunshi a lumshe yake,babu baki balle ya bayyana abi
nda ke cin ransa,ta tabbata ba magana daya ke dawainiya da zuciyar abdallah ba,suna da dama,koda bao jude idonsa ba,koda baiyi,magana ba tana ki a jikinta zuciyar abdallan a quntace take,takan tashi kokawa afili da boye duk da shi din tsananin jarumtarsa b
ai taba barinta taga hawayensa ba
Da taimakon bayanin da mama ke masu a waya suka kai ga isa qauyen NI'IMA dake cikin qauyen gaya,tun daga shigowarka garin zaka bawa kanka amsa,tabbas qauyen yaci sunanshi ni'ima,qauye ne da Allah ya wadata su da yawai
tar korayen shuke shuke qoramu dabbobi da lullumi ma'ana rashin haske da zafin rana
duk da haka sai da sukayi tambaya kafin su kai ga isa ainihin gidan da suke nema,gaya garin kakanninta ne tana zuwa lokaci bayan lokaci saidai qauyen ni'ima din zata iya i
rga iya adadin zuwanta tunda bata da wani shaqiqin da zata zo gunsa face wannan tsoho qwaya daya da yake qanin kakanta
*mrs muhammad ce*
π
πππ
β
π½
β
π½
β
π½
[6:27pm, 9/22/2017] Huguma
π
:
ππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
πΊ
*ABADAN*
πΊ
πππππ
π
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
ππΊππΊ
ππΊπ
πΊπ
π
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πΊππΊππΊπ
πΊππΊπ
πΊππΊ
ππΊ
π
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*
π‘
*_home of expert and perfect
writers_*
βΆ
4
β£
5
β£
*_Mazan Allah S A W yace:ku umarci 'ya'yanku da yin sallah suna da shekaru bakwai,sannan ku dakesu saboda ita idan suka kai shekaru
goma,kuma ku rarraba musu gurin kwanciya(ma'ana ya zama gurin kwanan maza daban gurin kwana
n matan daban yayin da suka cika shekaru goma)_*
Gida ne ginin qasa kamar yadda yake kasancewa ginin gidajen qauyuka,saidai wannan ya dan banbanta da nasu damin uasha shafe da ruwan makuba,hakanan ginin sumul sumul yake sakamakon fulastar kar
qasa da aka yi masa da kuma makubar da akabi aka shafe ginin da ita.
Maryam ce ta fara shiga,kamar yadda muka sani yan uwanmu na karkara basa gini quntatacce hakan ce ta kasance ga wannan gida,babban tsakar gida ne mai girma wanda babu sumunti a qasan
sa,turbaya ce saidai ta sha shara fes da ita,ga alamun shatin tsintsoya ne,daga can quryar katangar gidan garkene na dabbobi dake a tsaftace shima,sai rijiya daura da shi wanda lema ce duk a bakinta da tukwanen qasa da aka kikkife da alamu wanke wanke aka
gama agun babu jimawa.
ta sake yin sallama kin shiru ba'a amsa ba karo na uku,cikin daya daga dakuna hudin dake jere taji muryar matashiya na amsa mata,ta fito sanye da roga da zani na atamfa wadan da suka danyi haske saboda dan jimawar da sukayi a d
uniya,maryam ta duba itama ta kalleta
''don Allah inna wuro fa
οΌ
''maryam ta tambaha,sai ta juya ta kalli dakin kana ta kalli maryam
''tana ciki salla take amma yanzu zata....'''
''wake sallama ne mero,a shigo mana''
muryar inna wuro ta katsesu
''inna w
uro baqi kikayi''
''kaddai ace su meramu ne har sun iso haka da wuri''ta fada tana yunqurin fitowa,kasancewar ta san zasu zo din mama ta kirata awaya ta mata bayanin zasu zo din ta wayar mustafa jikan gidan.
hannunta dauke da tabarmar kaba sabuwa dal
ta fito,dattijuwa ce wadda aqiyasce zata doshi shekaru sittin,tsaf da ita cikin cikin atamfar itama da hijabi ruwan madara,fuskarta ta fadada da fara'ar ganin maryam din
''to kuma ya na ganki ke daya''itama murmushin ne afuskarta
''inna suna qofar gida'
'
''to yi maza kice musu su shigo daga ciki mana''ta fada yayin da take shimfida tabarmar.
Tare suka shigo hisham na tura abdallah kan wheelchair
''hukumullahu min zalika,Allah mai yadda yaso da bayinshi''inna wuro ta fada tama kallonsu
''sannu dam
nan sannu''ta qara fada tana kuma gyarq musu gun zama
matashiyar da inna wuro ta kira da mero dazu ta qaraso dauke da kwanonsha cike da ruwan tulu mai sanyi fari tas ta ajjiye gabansu,kanq ta