Showing 33001 words to 36000 words out of 129261 words
ko ka bari na jibgeshi ko
kuma na tsine masa, ya tashi yaja shegiyar y'arsa su fice min daga g
ida na tsani ganinsa." Kafin su yi aune suka ga Hammad ya mik'e idanunsa sun kad'a sun yi jazur dai-dai lokacin kuma suka ji ihun Khairi tana fad'in Anty Hamda Anty Hamda, Ali yayi saurin shiga corridor d'in sai dai kafin yaje ya tarar numfashinta ya d'auk
e ya dawo da sauri yana fad'in "Yaya ka bi abin nan a hankali kada azo ana kisan rai ga yarinyar can ta fad'i." A zafafe ya ce "Ta mutu mana burina ai mutuwarta idan bai janye ahalinsa sun bar min gidana ba wallahi sai na tsine masa."
Da sauri Ali ya juya
gurin Didi don yayi mata magana jin bata saka baki ba, sai dai me?daga Didi har Mahmah kamar basa cikin hankalinsu. Yayi saurin kama Didi yana kiran sunanta amma sai yaga ta fad'o jikinsa bata ko motsi da sauri ya hau jijjiga ta hankali tashe yake kiran "S
hikkenan wannan masifa tasa mun rasa Didi, yanzu Lauratu kin kyauta da kika kawo wannan zancen Allah wadaran wanda ya fara tono b'aragurbin k'wannan." Ammi ta zubawa Lauratu ido tana mamakin yarda Lauratu ta san maganar ita duk a zatonta Hammad ya kawo ida
n kuwa haka ne bai kamata ta tona wa kanta asiri ba, da sai ta kafe akan ba haka bane, tabbas tayi b'aranb'arama. Ita kuwa Sadiya sai a lokacin ta ja wani doguwar ajiyar zuciya a kuma lokacin ta samu damar kwararar da hawaye, sai dai ko da ta juya babu Ham
mad ba alamarsa a falon. Hankalinsu su kuma gaba d'aya yayi kan Didi sun kinkimeta don kaita asibiti. Gadanga yana ta fad'in a had'a da Hamda da take yashe amma Abbu yace "Wallahi Gadanga zan raba jiha da kai ka sake shiga hurumin Hammad da iyalinsa da gas
ke nake na rabu da shi har abada tunda har zai iya shiga gonata." Ras gaban Mahmah ya buga ta juya da sauri don komawa itama a sama ta ji maganar Abbu "Kema kina shiga huruminsa a bakin igiyar aurenki daga rana mai kama ta yau na zare shi daga sahun yarana
." A karo na farko Mahmah ta jiyo ta watsa masa wani kallo abinda bata tab'a yi ba a rayuwarta sai cewa tayi "Sai me don ka sake ni ba zan fasa shiga hurumin yaro na ba, aurennaka da sam ba adalci a cikinsa, ka sake ni mana Ummaru kawai saboda rashin adalc
i ba zaka tsaya kaji ta bakinsa sai kawai ka gasgata ta kai tsaye, sabida ita bata laifi." Da sauri Lauratu ta jata jikinta "Kiyi hak'uri Anty Sadiya, kada kiyi haka bari muje asibitin mu dawo na tabbatar Hammad yaron kirki ne wallahi sharrin hatsabibiyar
matar can ne, amma yanzu ya d'au zafi da yawa bai zama lallai ya gane yaren ba, idan muka dawo sai ayi zancen a nutse." Da kyar ta lallab'ata ta yarda ta bisu.
✍
🏽
✍
🏽
𝔍𝖎𝖐𝖆𝖗
𝕹𝖆𝖘𝖍𝖊
Zuciyarsa a zafafe ya sake komawa Falon Didin har a lokacin ta
na nan yashe a k'asa babu wanda ya sake bi ta kanta, k'wafa yayi ya shiga toilet ya d'ebo ruwa da sauri yazo ya watsa mata, ta kuwa farka idanunta cikin nasa tana sakin wata nauyayyiyar ajiyar zuciya. Kuka take shirin sakar masa ya zabga tsaki had'e da b'a
ta rai ya ce "Kada ma ki fara ba lokacin kuka bane yanzu, lokacin kuka ya wuce tunda kin riga kin fahimci wacece ke, ki mik'e ki tarkato duk wani shirginki da takardun makarantarki ki fito mu tafi." Ganin yarda fuskarsa take ta tabbatar ba wasa a lamarins
a ya sata ta mik'e ba shiri don ta lura sarai zai iya kai mata duka idan ta kuskurewa umarninsa. Sai dai ina taku biyu tayi ya jita a kansa ta fad'o tsaki ya saka ya tabbatar da gaske ba zata iya takawaba tsam ya mik'e da ita a jikinsa ya shimfid'eta a kuj
era da kansa ya fad'a cikin bedroom d'inta shi da Khairi suka had'a mata takardunta da litattafanta ko ta kan kayan sawa bai bi ba ya fito har su Kamlan ya tasa a gaba ita kuma ya mik'ar da ita yana rik'e da ita suka nufi mota. Dole ya kaita
asibiti kafin
aiwatar da duk wani shirinsa.
Da mugun speed yake jan motar bai kaita asibitin da suke zuwa ba wani can daban ya kaita, Khairi ya bari a wajenta bayan likitan ya sake tabbatar masa tana buk'atar nutsuwa sosai don jininta yayi mugun hawa. Ya kalleta a zafa
fe ya ce "Wallahi idan baki daina kuka da sakawa kanki damuwa ba, tsaf zan tattara in tafi in barki idan yaso ko kasheki ne su yi ni ba ruwana, an gaya miki suna da asara ne idan zuciyarki ta buga kika mutu, kina kallo dai suka yi watsi da lamarinki ta tso
huwar uwarsu kawai suke, dama idan na dawo kina kukan nan sai na murje bakinki, ga waya nan Khairi ki kira ni idan tayi kuka, haba fin mutane idon kukan kika yi?" K'asa kawai tayi da idanunta bayan ta d'auke sautin kukan tsaf. Ta bi bayansa da kallo bayan
ya tasa Kamla da Abulkhairi a gaba yana fad'in "Muje na kaiku gurin uwarku."
08033748387.ALKALAMIN JIKAR NASHE
YA ABIN YAKE?
Nazeefah Sabo Nashe
08033748387
16..
____________________________________
Tunda ya isa k'ofar gidan surikansa ya
yi parking kansa kawai ya d'ora akan sitiyarin mota yana jin yarda zuciyarsa ke bugawa da tsananin b'acin rai gami da tururin bak'in ciki. Me yasa Abbu zai yanke hukunci cikin fushi ba tare da shi ya ji ta bakinsa ba, ko a kotu ake kafin zartar da hukunci
dole sai an ji ta bakin mutane guda biyu. Amma zai bawa Sakina mamaki zai nuna mata shi ma ya iya rashin mutunci kamar ko wane d'an zamani. Ya runtse idonsa gami da cije leb'ensa da k'arfin gaske tamkar zai huda shi, sai kuma ya saki yana furzar da tururi
n b'acin rai, da gaske sai ya rama yayi alk'awarin yin ramuwar gayya a lokacin da bata yi tsammani ba, sai ya tozartata gaban kowa sai ya kuma fito da ainahin b'oyayyiyan halinta kowa ya gani an kuma yi Allah wadarai da ita. Duka wad'annan zai yi su ne a l
okacin da
Ta sakankance ta manta da batun
Shi kuma zai bayyanar mata a matsayin ramuwar gayya.
Wayar hannunsa ya shiga dialing
Bayan da yaji Abulkhairi na kiran Dad Dad mun zo ba. Cike da takaici ya d'an shafa kansa.
Nanna da take zaune kusa da Mamanta t
a d'aga wayar "Ki fito ina waje." Shine kawai abinda ya ce ya katse wayar, Nanna ta tab'e baki don tuni ta saba da halinsa in dai wannan ne. Mayafinta ta yafa ta fice da sauri don ta ji dalilinsa na zuwa shi da ya ce sai dare zai zo d'aukar ta.
Turus ta y
i ganin yarda fuskarsa take a matuk'ar d'aure zata iya cewa tun bayan aurensu bata tab'a ganin fuskarsa a wannan yanayin ba. Ko lokacin da yake shiga wancan yanayin idan an b'ata masa rai bata tab'a ganin fuskar sa ta koma haka ba.
Ba tare da ya yi magana
ba ya bud'ewa yaran k'ofa yana dubanta cikin yanayi na bada umarni ya ce "Ban amince ko da wasa ki je Gidan mu ba, kuma ku shirya nan da 1 week za mu koma inda muka fito." Idanunsa cikin nata tana k'ok'arin samo kalmar da zata furta masa, tambayarsa take s
on yi amma kafin furucin ya fito ya ja motar da mugun speed. Nanna ta saki ajiyar zuciya had'e da furta Allah ya kyauta ya kuma saukeke lafiya. Amma wannan jaraba har ina ayi mutum sai kace mai shafar Aljanni.
Jikinta a sanyaye ta shiga gidan nasu, Ummant
a na ganinta ta ce "Lafiya? Ko k'in zama suka yi ya rakito su nan?" Nanna ta girgiza kai "Ko d'aya, kawo su ma ya yi ya kuma ce ko da wasa kada na sake na koma gidansu, ban san dalili ba." Umman ta girgiza kai had'e da
Lalubo wayarta ta shiga kiran Yayarta
.
Sai da tayi ringing sosai kafin Sadiya ta d'aga zuciyarta na harbawa dafatan Allah yasa ba wannan labarin mara dad'in ji bane ya je kunnen K'anwarta da wani ido zata kalli y'an uwanta ta ce "Eeh, hakane Hammad ya yiwa matar ubansa fyad'e har ta haifa mas
a y'a da kunya ai, duk da tana tantama idan har hakan ya faru da gaske. Jin k'anwarta ta Dida na ta fad'in hello Yaya ba kya ji nane? Na ce me ke faruwa a can gidan ne Hammad ya kawo yara har kuma yana gargad'in Nanna da kada ta sake ta sake zuwa ko k'ofar
nan gidan." Sadiya ta saki ajiyar zuciya, murya a dashe ta ce "Wallahi d'an sab'ani aka samu Dida, ta bi umarninsa kada ta zo d'in har muga abinda hali yayi, yanzu haka muna asibiti da Didi bata uhm ba ta uhm-uhm har yanzu kuma likitocin ba su ce da mu ko
mai ba." Dida ta saki salati kafin ta ce "To Allah ya kyauta, ya yi mana maganin koma menene, ita kuma Didin wani asibiti ta ke sai mu zo ai yanzu." Kamar ba zata gaya mata sunan asibitin ba sai kuma ta daure murya a cunkushe ta sanar mata, had'e da kashe
wayar, tana sake lalaubar numberr Hammad amma still bai kunna wayar ba. Gabanta ne yake fad'uwa bata son Hammad d'in ya je ya aiwatar da wani abu cikin fushi, sai dai ta san bata da halin tafiya ta bar Didi da iyalinta a cikin wannan yanayin.
********
Babu b'ata lokaci Drivern Hajiya Dida ya sauke su a asibiti ita da Nanna da su Kamla da tun bayan
faruwar lamarin jikinta ya saki duk da bata da wayon gane komai amma ta tabbatar abin da ya Farun ba mai kyau bane, musamman ganin yarda aka doki Daddynta, ba
ta san me yayi ba abu d'aya ta rik'e da ta ji ana cewa Hamda y'ar Daddy ce. Sun duba Didin zuwa lokacin an kai ta d'akin hutu tun bayan da aka samu nasarar numfashinta ya daidaita, sai dai ba su samu fuskar da za su tambayi kowa komai ba, ganin yarda fusko
kin nasu suka bayyana matuk'ar tashin hankali.
Sai da Sadiya ta rakosu sannan Nanna ba tayi k'auran baki ba ta ce "Mahmah ina Khairi ne, na ga kowa anan d'in ban ganta ba ko tana gida gurin Hamda" "Bata gida tana asibiti gurin Anty Hamda Dad ne ya kaimu
aka yiwa Anty Hamdan allura." Abulkhair ya fad'a. Nanna bata kawo komai a ranta ba ta ce "Allah sarki me ya sami Antyn ta ku?" "Fad'uwa tayi da ta ji Amma ta ce Daddy ne Babanta, wai Daddy ne ya haifeta..."
Wannan karan Kamala ce ta fad'a itama idanunta na
zubar da hawaye ta cigaba da cewa "Shine Granny ya Zane Daddy ya doke shi..." Tsoro da firgici ne ya bayyana a fuskokinsu gaba d'aya. Sadiya ba bakin magana sai sunkuyar da kai da ta yi kawai idanunta na zubar da wasu hawaye masu zafi, duk da bata so fita
r maganar ba Ta san dole wata rana zata fita, tunda ance zancen duniya ba ya b'uya. Sam basu lura Da Nanna ba sai da suka ga ta yi zaman y'an bori tana shirin rusa ihu Dida Ta zabga mata tsawa "Ki ka fara ihun nan sai ranki yayi masifar b'aci, asiri kike s
o ki tona mana, Innalillahi wa inna ilaihirrajiuna, Yaya Sadiya abin da nake ji a bakunan yaran nan gaskiya ne?" Sadiya da kanta ke k'asa ta d'aga kai murya a dashe ta ce "Duk da ban ji ta bakinsa ba amma alamu da dama sun nuna haka d'in ne. Wallahi saboda
tsananin b'acin rai ji nake dama na mutu na huta." Dida ta jingina da motar ta bayan ta nad'e hannayenta a k'irji, ta rasa ma me zata ce sai can ta busar da iskar bakinta ta ce "Yaya ya kamata mu ga Hammad ta kowane hali ko da
Kuwa a gidana ne." "A ina za
n gan shi, kiran duniya na yiwa wayarsa ta k'i shiga, shi kuma ubansa ya kore shi daga gidan gaba d'aya ba tare da ya tsaya ya ji ta bakinsa ba." Nanna ce ta mik'e fuskarta a had'e ta ce "Ni na yarda, na yarda jininsa ce sabida a kamanninta da Kamla ya isa
ya tabbatar da hakan." Ta fad'a wasu hawaye na gangaro mata. Sannan ta juya ta kalli Kamla ta ce "Ke ya sunan asibitin da kuka kai waccan shegiyar Antyn ta ku?" Kamla da ta diririce ganin yanayin Mommyn nata da sauri ta ce Standard" Mota kawai suka ga ta
fad'a da sauri. Dida cikin masifa ta ce "Ke Nanna bana son hauka bud'e motar nan kafin ranki ya b'aci, hauka ki ke?" Ta san sarai mahaifiyarta kaifi d'aya ce kuma bata da wasa hakan yasa jikinta a sanyaye ta bud'e motar. Ta koma baya had'e da bawa driver d
a yake can gefe key d'in suka shiga motar gaba d'aya har Sadiya. Nanna sai sake b'ata rai take, tana sake danna kiransa amma bata shiga. Har Driver ya ja motar don isa asibitin Standard d'in.
____________
Daidai lokacin Hammad ya fito daga hotel d'in d
a ya kama d'aki, zuwa lokacin da zai bar garin, don baya son zuwa gidan ko wane aboki balle aji dad'in tambayarsa dalilin barinsa gida.
Sanye ya ke tsaf cikin shigar k'ananan kaya fuskarsa ta yi wasai ya samu nutsuwa sosai, tun bayan da zuciyarsa ta amint
a da shawara d'aya da ya yanke. Sai baza k'amshin turarensa ya ke Hugo Boss, duk inda ya bi kuma idanun mutane a kansa saboda yarda yake taku, duk da da alamun b'acin rai a fuskarsa hakan bai b'oye Sirrintaccen kyan da yake da shi ba.
Ya bud'e motarsa k'i
rar Mercedes Benz bak'a wuluk ya shiga. Sai da ya tsaya a eatery d'in hotel d'in ya karb'a musu abinci mara nauyi da drinks sannan ya finciki motar da mugun speed, haka nan yake tuk'insa ko don ya saba da driving d'in Birmingham ne yana mantawa a Nigeria y
ake musamman Kano garin taron cunkoso.
________
Ko da ya shiga d'akin Khairi kawai ya tarar a zaune da wayar Hamdan a hannunta tana dannawa. Ita kuwa Hamda tana kwance a saman bed d'in idanunta a lumshe, daga yanayin yarda yaga hawaye
na zuba a idonsa
ya tabbatarwa kansa ba barci take ba. Khairi ta masa sannu da zuwa kafin ta amshi ledar hannunsa don dama yunwa take ji.
A bakin Gadon ya tsaya yana k'are mata kallo kamar ranar ya fara ganinta, gaba d'aya ta sake zubewa ta rame lokaci guda. Ya saki siri
rin tsaki a fili kafin ya bubbuga gefen katifar gadon murya a tsaurare ya ce "Ta shi malama na san kina ji na." Idanunta da suka jirkita launi daga farare tas zuwa jajaye ta bud'e da kyar ta saukesu a kansa, gabanta na fad'uwa da ta tuna shine wai a matsay
in mahaifinta. Tana k'ok'arin bud'e baki tayi magana ya dakatar da ita don ya san ba abu mai dad'i zata furta ba. "Ki rik'e duk wasu tambayoyinki bana son jin su, don ba zaki samu amsa ko d'aya ba." Ta had'iye wani abu a mak'ogoronta mai d'akin gaske tana
mamakin halayyarsa tamkar mai gani har hanji. Ya sake kakkafe ta da ido "Ki mik'e ki ci abinci Malama, zan kai ki wajen passport suna jira na." Babu alamun wasa a tattare da shi, ta tabbatar a yanayin da take bata isa ta ce masa ta k'oshi ba, don haka ta j
a kwanon take away d'in ta d'au cokali kenan aka danno k'ofar aka shigo. Gaba d'aya suka d'aga kai don ganin su waye, Nanna ce a gaba sai Dida da Mahmah da suka shigo sun bar su Kamla a motar.
Wannan karan Nanna da gaske take don sam fuskarta ba annurin r
ahma ta saukesu akan Khairi, had'e da nuna mata k'ofa "Fita Malama, ban ga dalilin da zaki zauna jinyar shegiya ba.." Da sauri mahaifiyarta ta mata wani kallo ganin Hammad ya d'ago a fusace yana wurga mata wani irin kallo mai cike da gargad'i Dida ta ce "K
e Nanna saurara mana, bana son hauka uban wa ya ce miki shegiya ce?" "Idan ba shegiya ba me kike so a kirata Dida? Ni na tabbatar ko Hammad ne yayi cikin ta to uwarta ce ta ribaceshi, bisa son zuciyarta na son haihuwar d'a namiji, don haka Hammad a matsayi
na na uwarka ya zama dole ka sanar da ni yarda abin yake, kafin ka saka zuciyata ta buga ka yiwa sauran y'an uwanka a sara, don na lura kai baka d'aukeni da muhimmanci ban da haka ai da tun lokacin ka sanar da ni gaskiyar abinda yake k'udundune, yanzu ga s
hi ita ta wanke kanta kai ta saka ka a bala'i.
Gaba d'aya Hamda ji tayi kamar duka sassan jikinta ya daina aiki, kanta kuwa jinsa take kamar ya tsage biyu saboda masifar da take ciki, ina ma rabbi ya agajeta ya d'auke ranta ta huta.
A zafafe Nanna ta ce
"Kin ga yayi shiru ba zai fad'a bane, sannan
Kuma yazo ya tare a gaban shegiyar y'arsa ya nunawa duniya da gaske shi yayi cikinta, to wallahi muddin yace zai dinga shiga huruminta sai dai ya sawwak'a min."
"Saki nawa ki ke so?" Suka ji ya fad'a muryarsa a
kaurare ba tare kuma da ya kalli kowa ba, kamar yarda suka tarar da shi idanunsa akan waya har a lokacin hakan yake. Tsoro da razani suka shigesu gaba d'aya, ba su sake firgita ba sai da suka ji ya ce "Ina sauraranki, saboda ina tabbatar muku mahaifiyata c
e kawai ba zan iya rabuwa da ita