Showing 33001 words to 36000 words out of 108953 words
da marwa fa'di yake am sorry Auntyna........
By Hajju
[20/03, 17:09] 80k: [2:09PM, 29/11/2016] Rahamat Nalele
👯
: [12:18PM, 29/11/2016] Rahamat Nalele
👯
:
👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*
👯
BANAH*
👯👯👯👯
*
👯
TA
SU SALAN SOYAYYAR*
👯
*Na Rahamat Muh'md Rufa'i Nalele*
*Bismillahir-*
*rahmanurrahim*
*PART 81*
Abin da RAMADAN yake ta fa'di kenan yana ciga da safa-marwa
FAWAS yashigo yana fa'din ka shanyamu fah
Ya kallesa Yace baxan iya xuwa ba k
uje kawai
FAWAS Yace me yasa Yace yanxu Auntyna ta kirani........
Da sauri FAWAS ya katseshi da kar6i wayan nashi da murna yake cewa Aunty LUUVAH
Yace eh
Yace nayi missing 'dinta ina number na kirata pls.
RAMADAN ya dafa FAWAS Yace akwai matsala
Jikin FAWAS a sanyaye Yace wacce irin matsala. Kar dai fatanka ya bita
Yace nasan xai bita Amma ba kamar yanda na xata ba
Kashare kawai xan gyarota.....
FAWAS yayi shuru Yace Allah Sarki Auntynmu......
KHAMIS ya shigo ganin yana yinsu Yace lpy
FAWA
S Yace hmmm fatanshi ne yake san bin Aunty LUUVAH
KHAMIS ya waro ido Yace what
Tana ina yanxu
RAMADAN yayi Murmushi Yace tana gidanta mana
Fahimtar dani pls Naji gabana ya fa'di am serious.
RAMADAN Yace kirana tayi yanxu muka gaisa daga yanayin mur
yarta ya nuna min akwai matsala.
KHAMIS ya xauna kan kujera cikin sanyi Yace wayyo Allah Aunty LUUVAH Allah ya kareki
Amiien FAWAS Yace
RAMADAN Yace karku damu xan gyarota cikin sauqi. Inaga mah gobe xanje Abujan in ban ganta bah hankalina baxai kwant
a ba
FAWAS Yace amma tare xamu ko
RAMADAN yayi Murmushi Yace kadinga cika alqawari a rayuwarka hakan xai qara maka daraja da kima ako kake
Nasan yau ka fasa xuwa ga HAMEEDA inaso gobe kaje gareta pls
KHAMIS Yace saimu tafi tare
RAMADAN ya qara yin
Murmushi Yace kaima kagare man.
Kasan Aunty XEE da ru'dewa bana San tasan wani abu pls
Kubarni naje. akwai waya ai nadinga muku bayani
Yanxu dai muje ga Aunty XEE tayi min bayanin inda gidan nata yake......
Sun sami XEE a harabar gidan tana wa
nke gyalinlikanta sai surutu takeyi ita 'daya cikin damuwa
Duk suka fito daga motar ta sakar musu Murmushi Tace kaga *SAMAREEN BANAH* Na Aunty Rahamat daga ina haka kuma xuwa ina
KHAMIS ya saka hannunshi cikin wankin yana tayata da jefah mata wani k
allo irin na tuhuman nan
FAWAS Yace daga gida Aunty...
RAMADAN ya xauna kusa da ita Yace Aunty XEE bayani xakimin akan inda gidan Auntyna yake
Ta kallesa da sauri tace aha.....
Yanxu kuma kana buqata ne
Yace Sosai mah dan xuwa xanyi gobe
Tace hmm
yanxu nake magana kamar wata ta6a66iya akan na rasata awaya kuma gabana sai fa'duwa yake Sosai akanta. Tafa'da da damuwa akan fuskarta...
RAMADAN Yace hmm Karki damu insha Allah ba wani Abu.
Tace Allah yasa
Yace AmEEn
Nan tayi mishi bayanin gidan. Y
ako fahimceta Sosai dan bayau yasaba xuwa Abujah ba dan Qanin Dadyn shi acan yake
Tace kushiga falo mana
RAMADAN ya tashi Yana cewa aa
Ya maida kallansa ga KHAMIS daya xage yana tayata wankin. Yace muna jiranka a waje
Yace OK. Suka fitta
XEE ta
kalli KHAMIS Tace my Luv baka iya wankin nan ba pls bar shin kawai
Ya kalleta yayi Murmushi Yace dama ke kike wanki ina injin 'dinku
Tace aa yau dai nayi niya ne bakaga bashi da yawa ba kuma dan ba wutta ne
Yace toh kidena bana so
Me yasa
Hakka
dai
Fa'di dai dalilinka
Jiya na barki kina mura. Har yau bata canja xani ba. Kin wani kama wanki da yamman nan. Kalan Ki jaxa min tashin hankali ciwan yafi haka muni ko.
Tayi Murmushi da kallansa yanda ya 'daure fuska shine abunda ya burgeta
Tac
e nayi lefi
Ya harareta
Tace toh am Sowie
Yace daga yau......
Tayi saurin katse shi da cewa. Baxan sake bah
Yace Promise.....
Tace Aha promise
Yace gashi mun gama a ina Xan shanya miki
Tace xan busar a injin naga sun kawo wutta kalli
Yace b
asu burge bah
Tace yanxu ina xaku Yace da wai qauye Amman mun fasa Tace mexa kujeyi can
Yace xance
Wajan wah
Wajan wata kyakkyawa
Miye ha'dinka da ita
Yace ha'a
SO mana
Tatashi cikin maseefa Tace toh tashi kaje sai ka dawo
Shima tashin ya
yi yana murmushi Yace ki temaken Ki Kawar da wannan fushin naki ko nasamu nutsuwa
Ta gallamai harara fuska 'daure Tace kafita kafin raina yafi hakan 6aci
Yace kwantar da hankalinki my luv Ki sakarmin mara dan da gaske kin sani jin futsari...
Na rants
e miki da Allah ba budurwata bace
Tayi Murmushi da cewa ban yarda ba
Yace ki yarda pls
ina tare dake baxan ta6a ganin kyawun wata 'ya mace bah
Tace har kasa hankalina ya kwanta. Je kayi futsarin karya dameka
Ya harareta da cewa hmm gidan suruk
ai fa nake rufamin asiri kar wani yaji
Tace dan kayi futsari
Ya shafi gefan fuskarta da murmushi Yace Ki kulamin da kanki bye
Tayi Murmushi Tace bah bye my baby
Yafita yana Murmushi da 'daga mata hannu
XEE ta 'dauki butikin wankinta tayi ciki xuciy
ata cike da qaunar masoyin nata
.
[2:08PM, 29/11/2016] Rahamat Nalele
👯
: Misalin qarfe takwas ne 8:00pm ne na dare RAMADAN yasami mahaifan nasa a falo Suna hira cikin kwanciyar hankali
Ya xauna kusa da Dadyn nashi bayan ya gaidasu Yace ina San
xuwa Abujah dad
Dadyn nashi ya waro ido Yace me yasa
Yace xanga Auntyna Sannan na da'de banga Dadyn Yusra ba
Dadyn shi yayi shuru Yace skull fah
Yace akwai sauran lokaci ba damuwa
Dadyn ya gyara xama cikin damuwa Yace yaxo garin Abujah yau kwana
nsa uku bana San Su ha'du
Momy tayi saurin cewa bafah ni ka'dai bace
Cikin sauri Dadyn yanemi gyara kansa da cewa Nace wani abu ko
RAMADAN ya kallesa da mamaki Yace kace mana dad
Waye shi da bakasan na ha'du dashi
Dadyn Yace ba dakai nake nufi ba
RAMADAN ya ta6e baki Yace Owkie yanxu dai afara min shiri dad
Dadyn ya kalli momy Yace afara mishi shiri
Cikin damuwa Momy Tace toh
RAMADAN Yace ina buqatan ku'di dad na hannuna sun qare Yace kaje 'dakina ka 'dauka
RAMADAN ya manna mishi kiss
a goshi Yace tnx my Dady. Yayi shashin Dadyn da murna
Momy ta gya'da kai Tace akwai matsala Dadyn RAMADAN
Yace babbama kuwa
Washe gari RAMADAN ya cale garin na Abujah dake jirgi yabi
Baiyi mamakin ganin direban Su Yusra yana xaune xaman saukar
shi ba
Dan haka suka tafah da Adam direba Yace mutumina ka ha'du fah. Kaga yanda ka girma
RAMADAN yayi Murmushi Yace Yaya Adam kenan har yanxu kananan da barkwancin ka
Yace toh yaxanyi RAMADAN bayan gaskiya nake fa'da
RAMADAN Yace kaga Malam muje
daga nan ka 'dorani akan inda katsaya
Da dariya Adam ya tada motar
Ayanda RAMADAN ya fuskanta gidan Auntyn nashi bayi da wani nisa da gidan kawun nasa
Sun isa gidan babban gida murna ta cika gidan Wlcm Ya RAMADAN Wlcm
Baiyi mamakin farin cikin
su ba dan yasan masu qaunarsa ne
Su uku ne yaran gidan
Amar shine saran RAMADAN watanni RAMADAN ya bashi
Sai Yusra wacce take maseefar son RAMADAN tun tana qarama take sanshi sai Ameer qaraminsu yaro me hankali
Cikin Murmushi Amar Yace sannu da
i brother.
RAMADAN yayi Murmushi Yace Yauwa na sameku lafiya
Yace lpy lau Wlhi
Toh Madallah. RAMADAN ya fa'da da maida kallansa ga Yusra Yace qanwata yadai rufe bakin mana Tace Ya RAMADAN kenan nayi farin ciki Sosai da wannan xuwan baxatan da kamana
Yace naji da'di da kika ji da'din hakan
Dady da momynsu sai Murmushi suke dan Allah ya 'dora musu san RAMADAN Suna sanshi Sosai
Dady Yace jiya ai Dadyn naka yake gayamin wai haka kawai kace kanasan xuwa garemu
Yace eh Dady kuma inasan Ganin Aunty
na mah
Momy Tace SAILUBAH ko
Yace eh Momy ita
Yusra Tace xan rakaka in xakaje gareta
Yayi Murmushi Yace ai kuma tunda naxo shikenan fah na shiga uku agunki
Duk sukayi dariya ya tashi yana kallan Amar Yace toh brother muje inyi wanka in huta...
D
ady Yace badai har ka qoshi ba
Yace ai naci da yawa
Yusra tayi dariya Tace nifah na dafa maka
Yace hmm ban yarda ba dan nasan baki iya girki bah
Tace Allah nice nayi Yace na yarda dama nasan qanwar tawa ta iya girki wasa nakeyi
tayi dariya....
Ya
tasa Amar agaba sukayi shashinsa
Bayan RAMADAN yayi wanka ya miqe a gado yana san yin tunanin Auntyn tashi da yanda xaije gareta gobe. Kiran wayan shi ya katseshi
Yana dubawa yaga shahuda.....
Da jan tsaki ya picking da Alo
Tace haba RAMADAN lefin
menayi kadena 'daukar wayata
Yace wane ke da lefi ai bakya lefi
'Dan jini ka'dan kiji
Tace ina ji
Yace kwana biyu ban riqe wayar bane shi yasa naketa kar6ar hukunci agun mutane pls kar kema Ki hukuntani dan Allah
Tace wane ni
Kana ina ne yanxu
Yace bu'de kunanki kiji dakyau
Tace aha na bu'de
Yace ina garinku kuma inda yake shashinku
Tace dan Allah fah
Yace fa'di abinda xan miki ya tabbatar miki da hakan
Tace yanxu naganka
Yace wa'yanda nake gidansu baxa su barni fitta yau ba
Tace
toh gobe na ganka Yace Allah ya karmu
Tace bara na barka ka huta gajiya ko
Yace Saidai ban gaji da jin dad'dar muryarki bah
Tace hmm baka da dama Wlhi
Yace Gaskiya
👯
wata sabowa inji 'yan caca
👯
Al'amarin tafaru ne a ranar
Misalin qarfe
goma na dare
'Yan fashin suka shiga gidansu shahuda bayan sun buge kawukan masu tsaran gidan da ma'aikata suka shiga cikin babban falan gidan.
Duk Suna falan Suna hira
Shahuda. Dadynta da momynta sai wani 'dan uwanta 'dan Qanin Dadyn nata
'Yan
Fashin nan suka musu dirar makiya Su biyar
Nan suka kwanta da tashin hankali
'Daya daga cikinsu Yace ku'di ko rai
Shahuda ta kalli Wanda yayi maganar cikin sauri jikinta na rawa Tace RAMADAN
😳
Saurayin ya kalleta da mamaki Yace a ina kika sanni
Ta
ce nice shahuda da mukayi magana 'daxo dakai
Ya 'dauke kallansa daga kanta xuwa ga mahaifinta cikin 6acin rai Yace bakaji me Nace bah
Yace Naji samarii ku'din Suna cikin 'daki. Yafa'da cikin matuqar tsoro..
Saurayin da shahuda takira da RAMADAN ya ka
lli Wasu maxaje biyu yayi musu nuni da 'dakin
Nan suka shiga cikin gaggawa suka binkico ku'din suka fitoh da direwa a gabansa
Saurayin yayi Murmushi Yace ba wa'yannan bane
Cikin tashin hankali Dadyn shahuda yanuna wani 'daki Yace Suna can
Saurayin
Yace kaqara yin kuskuran nan Wlhi saina 'dauke ka
Cikin sauri mutane Biyun nan sukayi 'dakin da yayi nuni
Aiko saigasu da kinki memiyar jaka
Saurayin Yace dakyau Alhaji. Katara da yawa ka qara Tarawa sufi haka xai qara turomu muqara amshewa mun bar
ka lpy
Har sun kai qofa.....
Shahuda Tace Allah ya isa tsakanina dakai RAMADAN
Duk samarin suka juyo da sauri
Saurayin ya dawo kusa da ita Yace mai maita abinda kikace.....
Xatayi magana Dadyn nata Yace ina neman mata afuwa
Saurayin ya 'daga mis
hi hannu Yace ke agidan uban wah ma kika san sunana
Shahuda tayi shuru.....
Yako daka mata tsawa.
Cikin rikicewa Tace a supermarket 'din jifatu na garin Kano mana. Har kayimin 6ari kaban hakuri nabaka number na kaban taka.
Ko 'daxo ma ai munyi waya ka
cemin kana cikin garin nan xakaxo gareni gobe Ashe kaxo yashe mahaifina ne.
Ya durqusa ya kama fuskarta yakai bakinsa cikin nata yabata wani make
✔
kiss me tsayawa arai
Yace shegiya Kinga 'dan saurayi ko.
Nafi qarfinki Wlhi
Haka kawai kin shirya ma
gana dan kinaso nayi kissing 'dinki ko
Ta girgixa kai cikin matuqar 6acin ran abunda yayi mata
Yace sunana RAMADAN kamar yanda kika fa'da Amma ni ban ha'du dake bah. Dan ban ta6a xuwa wani gari waishi Kano ba
Dan haka ki kula idan muka sake ha'duwa
kika nuna kin sanni Wlhi saina bundige kanki
Yana fa'din haka suka bar falan. Iyayanta suka fashe da kuka danjin tashin motar SAMAREEN......
Tofah
😳
.
By Hajju
[2:11PM, 29/11/2016] Rahamat Nalele
👯
: RAHA
â“‚
🅰
T
[20/03, 17:09] 80k:
👯👯👯👯👯
*SAM
AREEN*
*
👯
BANAH*
👯👯👯👯
*
👯
TASU SALAN SOYAYYAR*
👯
*Na Rahamat Muh'md Rufa'i Nalele*
*Bismillahir*-
*rahmanurrahim*
*PART 83*
Senior RAMADAN ko mamaki ne fal Cikin ransa.
Me yayima shahuda da Dadynta da xaisa Su qaqaba mishi
bindigogi haka
Ya kalli shahuda Cikin wani hali Yace wai me nayima Dad 'dinki ne daxai qaqabamin bindigogi haka
Ta qura mishi ido takasa bashi amsa dan rasama me xatace mishi tayi....
Bata idda tunaninta ba taji Dadyn nata yana bashi amsa
Yace Lal
le kacika 'dan iska xahiri
Ko Mantawa kayi in tuna maka
Kuxo jiya kumin fashi yanxu kafara tambayar me kayi
RAMADAN Yace fashi
😳
.....
Wlhi bani bane. Yafa'da cike da tsoro da kallan shahuda
Tayaya Xanyi fashi
Me nake nema haka dana rasa dahar xan
yi fashi.....
Cikin fusata shahuda Tace Amma kai dai kacika 'dan rainin hankali....
Dadynta ya amshe da cewa bar 'dan iska yaudai qaryarka taqare kai da uban naka
Wlhi kaji narantse indan har uban naka bai dawomin da ku'dina ba na rantse saina kasheka
natura mishi da gawarka kuma........
Bai qarasa furucinsa ba
Saiga wasu samari biyu sun shigo gidan da manya manyan jakunkuna sun dire agabansa da fa'din wai xaka iya qirgawa ko daidai suke
Dadyn shahuda ya washare baki da murmushin jin da'di Ganin ku'
dinsa sun dawo
Yace shege Jibiril yaji anta6o farin cikinsa
Ya fa'da yana mai bu'de jakunkunan. Aiko saiga ku'dinsa nan muraran
Ayanda yalura ko 'daya baiyi ciwan kai ba.
Ya kalli wa'yanda suka takura RAMADAN da bindigogi Yace kusake shi ya tafi.
Nan ko suka bar gun.
RAMADAN yajah numfashi yana kallan ikwan Allah da mamakin abin....
Cikin sanyin yanayi ya shige motarsa shahuda tabishi da kallan harara
Shidai ya fitta yana hamdala ga Allah daya ku6urar dashi
Da wannan tunanin ya iso gidan
kawun nasa
Wanka yayi yayo alwala yayi sallah dake lokacin La'asar ta gabatoh
Saiya kwanta yana tuna lamarin
Har bacci ya 'dauke shi bai gane me lamarin yake nufi ba.
Junior RAMADAN ko bajewa yayi agadansa da niyar karantawa
Sai kuma ya ts
aya tunanin 'dan uwan nasa. dan tunda yagansa yaji qaunarsa aransa Sosai
Yaji yanasan ya qara ganinsa
Yasan tunda yacema Dad 'din nasa yasan yanda xaiyi tabbas xaisan yanda xaiyin ya ku6utar mai da 'dan uwan nasa.
Yin tunanin nan dayayi shine yabashi
qarfin gwiwar fara karanta diaries 'din......
*Asaninsu*
Malam habibu wani shahararran malamine acikin garin kano awata unguwa da ake kira bacirawa
Yana da mata biyu Hauwa da Asabe.
Hauwa itace wacce ta Haifa mishi yara uku wato Jibiril
da Naziru da Auwal
Sai Asabe ta Haifa mishi Jabiru
Yaransa sun kama hu'du kenan
Jibiril shine Babba sai Naziru sai Auwal sai autansu Jabiru
Bayan sun girma sun mallaki hankalin kansu Allah yayima iyayan nasu rasuwa
Farko Asabe mahaifitar Jabi
ru CE tafara rasuwa sai Hauwa tabi bayanta sai megidan nasu Malam Habibu
Haka suka taso gurin kawunsu wato qanin mahaifinsu Wanda yayi musu rikwan tsakani da Allah yabasu tarbiya da ilimi
Duk cikinsu jabiru yafisu ku'di nesa ba kusa ba
Ga shi yan
ada NASIBI dan duk abinda ya ta6a daniyar kasuwanci sai kaga Allah yasamai albarka aciki
Mahaifinsu Malam Habibu ya mutu yabar musu dukiya me tarin yawa
Dan haka aka raba musu gado dan kowa yaje ya juya kayansa dan sun mallaki hankalin kansu
Jabiru
yana ma Yayun nasa ladabi da biyayya Sosai
Kowa ya shaida hakan
Sam jabiru bayasan 6acin ran 'yan uwansa Sam
Lamarin yafarune lokacin daya farayin ku'di duk saiya doke yayun nasa aku'di
Abinda yasa Jibiril kenan yafara mishi hassada da Baqin c
iki
Tun baya ganewa har yaxo yafara ganewa
Yaje ga sauran yayun nasa yana nuna musu baidace yaya Jibiril yadinga nuna masa Hakka ba
Ha'kuri suka bashi dan dukkansu tsoran shi Jibiril 'din suke
Ahaka Naziru yayi Aure yatare da amaryarsa nan ci
kin Fage
Haka ma Auwalu shima yayi Auransa yatare da matarsa a garin Abujah dake shi yana ha'dawa da aikin gwannati
Jibiril ko San mata yasa agaba damuwar shi ya aikata xina da 'Yar mutane ya biyata
Anan duk ku'din da yake samu suke qarewa yaqiyi
n Aure sam
Jabiru ko neman ku'di kawai yasa agaba
Shine siyan filaye gidaje da dai sauransu gashi dasan yasaka hannun jari a garuruwa