Showing 39001 words to 42000 words out of 178317 words

Chapter 14 - LU'ULU'U COMPLETE

na yanzu da yakeyi personally ba tare da kowa yasan wayeshi din ba. Yanayin yadda naseeb yayi maganar yasan me yake nufi,ina ya dosa. A cikinsu shidan naseeb yayi aure bada jimawa ba.......mutallab......khadeem.....maleek......amjaad......dukka suna da tsayayya.......shine har yanzu da babu koda wannan tsarin a gabansa,sau tari koda conference call sukeyi a tsakaninsu mutallab din kan tsokaneshi da cewa.

"Don Allah ku nema masa tsayayya wannan.......wannan an rasa me tsaya masa". Omari ne kanyu murmushi......saboda shi daya ne yafi kowa a cikinsu sanin wayeshi.......yafisu saninsu rufaffen sirri me girma dake cikin rayuwarsa.

Cikin qasa da mintuna talatin tawagarsu ta soma fita daga masallacin zuwa inda kowannensu abun hawansa da guards dinsa ke jiransa. Cikin wannan hirar da barkwancin gami da qaunar junansu,kamar ba zasu rabu ba haisam din daya kasance me masaukin baqi ya takawa kowa zuwa bakin motarsa cikin musabahar bankwana suka rabu.

Ya rage dagashi sai omari da suke takawa a nutse zuwa sirrantacciyar hanyar da yakejin kamar nan ne kawai yafi dacewa suyi magana da omari,bayan masu tsaron qofar sun bude masa cikin rusunawa bayan ya wuce suka maidata suka rufe.

"Omari......" Ya kira sunansa da tsinkakkiyar muryar nan tasa dake da wani irin amo......amon da hatta maza 'yan uwansa tana musu dadi ballantana diya mace.

"Wani lokacin sai na dinga jin kamar wannan matsayin......wannan girman da ake bamu kaman yana neman wuce gona da iri.......kamar akwai sabawa mahalicci a cikinsa" Ya fada calmly kyawawan idanunsan nan dake da wani irin haske suna motsawa wajen rufe kansu da budesu a lokaci guda yana duban tsahon hanyar da suke takawa cikin nutsuwa.

Murmushi omari ya saki......shi dinma daga gidan sarauta ya fito,da akwai banbancin yare tsakaninsa da haisam.....shi din yaren amheric ne......amma yanayin aikinsu ya sanya shida haisam din sukejin yaruka masu tarin yawa,harda yaren da ba na qasarsu bama,ciki kuwa harda yaren turanci bayan na larabci daya zame musu kamar yarensu na haihuwa. Sun iya hausa kasancewarta cikin yare mafiya girma da fadada cikin yarukan yankin africa,hakanan sun iya French......yarukan da suke cikin qasarsu kuwa kusan kowannensu saida suka iya shi,a qalla idan aka lissafa yare kusan goma suke ji,saidai ba kowa ne yasan da wannan ba.

A yadda omari yake kallon komai,duk wani motsi na gidan sarautar abba jifar yana cike ne da zallar ilimin addini dake magana. Hatta da shigar bayi hadimai da dogaran gidan yasha banbam dana masarautu da dama. Tsarin aurar da hadimai da bayi......gidajensu prison dinsu da makarantunsu.......komai nasu yasha banbam dana sarakunan qasar da dama. Omari bai samu damar cewa dashi komai ba.......babban saqon da yake qunshewa a cikinsa tun dazun ya fado masa

"Shugaba yayi kira.........yace kuma lallai gobe mu sauka addis ababa". A nutse haisam ya waiwaya yana duban omari,saidai mamaki ya bayyana sosai saman fuskarsa.

"Da gaggawa haka?". Kai omari ya gyada yana dubansa shima.

" Yace bai sameka ta kowanne platform ba.....shi yasa ya ajemin saqon......ajemin saqon da ganin da nayi kuma dole ya sakani cikin operation din.......dama wannan shine burina,addu'ata ce ta karbu" Omari ya qarasa maganar murmushi yana subuce masa. Dauke dubansa haisam yayi daga kan omari fuskarsa na nuna alamun qaramin murmushi ta yankin rawanin da har yanzu bai saukeshi qasan fuskarsa ba.

"Inaji a jikina kamar lokaci yayi......kamar wani abu ya bayyana game da abba *AJANI AHMED*" Yayi maganar da dukka yaqininsa.

"Ka duba mana tickets da suke available daga jimma zuwa addis ababa......idan baka samu available ba ka sanarmin mu tafi a mota....."

"Dama kafison hakan ai" Omari ya fada yana dan tsuke girarsa. Haisam bai waiwayo ya kalleshi ba......saboda yasan hade rai omari din yayi,sai wani lafiyayyan murmushi abinsa daya sake cikin rawaninsa.

"Kuyi duba izuwa tasirin rahamar Allah yadda yake rayar da qasa bayan mutuwarta............haqiqa cikin halittar sama da qasa da sassabawar dare da rana akwai ayoyi ga ma'abota hankali......omari ka manta da wadannan ayoyin?". Kai ya jinjina omari din yana sakin murmushi alamun aah.

"Akwai abubuwan lura da tunani da yawa akai kan ayoyin ubangiji......baka taba sanin hakan sai kayi yawo a duniya......ka keta dazuzzuga da tsaunuka......ka hadu da hadura masu yawa......abubuwan firgitarwa masu tsananin girma......ka tuna cewa duka mallakar madaukakin sarki ne......iya wannan kadai ya isheka ka qara imani da yarda da ubangiji" Kai sosai omari ya jinjina......shi kansa akwai surori cikin qur'ani da idan yana karantasu yakan tafi ne zuwa wata duniya ta daban ta zurafafa cikin lamarin ubangiji.

08187255862

A cikin jini da dabi'ar haisam suke........yana da bala'in son binciken boyayyun abubuwa irin wannan da suka shafi hikima da qudira ta ubangiji.......yana son nature sosai.......yana da son zuwa baqin gurabe muhalli da qasashen da baisan komai a kansu......qasashen da zai zama baqo da gasken gaske akan komai nasu.......baya da tsoro ko digo dis a ransa........baya tsoron shiga risk da hatsari kowanne iri ne......wannan shine ya zame masa sanadin shiga aikin masu bincike na farin kaya cikin sauqi wato Dss. Cikin qanqanin lokaci da fara aikinsa sai ya zamana kamar da experience dinsa ya shigo aikin gaba daya......wanda halitta ce a jininsa data zame masa dalilin samun qarin matsayi nan da nan......cikin shekaru kadan ya zama babba cikin NATIONAL INTELLIGENCE AND SECURITY SERVICE(NISS). Yakai matakin da zai zama shine na daya a wajen.......amma zuzzurfan tunani da kaifin hankali irin nasa ya sanya hangensa yakai kan abubuwa guda biyu.

Na farko shi wanda yake akai a sannan ya fishi shekaru nasa ba kusa ba......sannan babban aboki ne ga mahaifinsa me martaba abba jifar.......ya riga ya sani,komai iliminka......komai wayewarka da saninka......akwai wasu dabaru da wasu hange hange da sai wanda ya baka shekaru zai iya hangensu........yana kunyar abba muhammad dawuud ya sauka a matsayi shi yahau kai.....duk da lokacin retired dinsa yayi.....amma ya nema alfarmar a barshi cikin office din yaci gaba da zama......shi zai zama a madadin mabiyinsa.

Dalili na biyu......yakan ware wasu watanni a shekarar da qasar Ethiopia ke dashi da suka saba da namu watannin goma sha biyu......su din suna da watanni sha uku ne.....a ciki yana daukan wata daya yayi hutu,hutun da ba inda yake qarar dashi sai yin visa ya sayi ticket na wata qasar dake nesa da yankinsu da al'ummarsu.....masu babancin halaye dabi'u al'adu dama halitta irin tasu...... Wani lokacine da yake na musamman a rayuwarsa.......wani lokaci da yake jinsa na musamman shi kansa.




zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*


*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer ๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ช*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261


*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA๐Ÿ‘‘*

*HUGUMANKU CE*โœ๐Ÿฝ

๐Ÿ’Ž *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*๐Ÿ’Ž


*H U G U M A*


PAGE 17


Yana samun wani 'yanci......yana jinsa cikin tarin sukuni da sakewa.......babu wadannan hadiman a tare dashi........ba wadannan masu kula dashi din,hadiman da mooti ko sau daya baya yarda haisam ya motsa ba tare da ko mutum daya ba......illa idan zai shiga NISS,kasancewar wani sirrintaccen abune da ba kowa yasa ma'aikacin hukumar bane......daga shi sai karan kansa a irin wannan yanayin da yakeyin nesa da qasarsa da mutanensa. Yakan yi tilawar qur'ani sosai fiye da yadda ya saba saboda samun sakewa da sukunin zuciya. To muddin ya karbi wannan matsayin zai rasa wannan damar,dole ya zauna ya dinga bada umarni.......shi kuwa yana ganin kamar hakan koma bayansa ne kuma koma baya ga baiwar fikira da basirar da Allah ya bashi ce.

Kafin wani a cikinsu ya sake cewa komai idanunsu sun hange musu ita. Cikin hanyar data kadaita ga kowa. Sanye cikin wani wadataccen hijabi daya sauka ya lullube har saman qafafunta. Matashiya ce da shekarunta gaba daya ba zasu haura sha tara ba........lullube da wannan kebantacce kuma sirrintaccen kyan na 'yan asalin Ethiopia kuma 'yan qabilar Oromo.......wannan kyan da aka bar musu kayansu,hannunta dauke da wani madaidaicin kwali,idanunta kuma manne akan fuskar haisam din.

"Saami" Omari ya fada qasa qasa,abinda ya sanya idanun haisam qiftawa yana saukesu daga kansa. Daga randa suka zauna sukayi sharhi da fashin baqi akan ayar da Allah yake magana akan LOWERING GAZE cikin qur'ani da suka yiwa take da yaren oromo da *Ilaalcha gadi buusuun* cikin qur'ani Allah yana cewa

"Ka gayawa muminai su kame ganinsu kuma su kula da farjinansu......wannan shine yafi tsarkaka a garesu" Sai ya sake zama me tsantseni da kulawa sosai akan wannan din. Komai Allah yayi jan kunne gargadi umarni ko hani akai ba shakka akwai babban lamari da kuna batu akai......daga ranar da bincikensa yakai kai kuwa baya sake kusantar wannan abun.

Ko kafin sannan mutum ne shi me tsantseni ta wannan bangaren......tun daha sanda ya mallaki hankalin kansa ya kuma fahimci irin halittarsa sai ya zamana ya dauki matakin kame ganinsa.......sake nesanta kansa daga dukkan wani jinsi da ba nasa jinsin ba......bai sha wahala ba,don dama dabi'arsa daban take.......tun asali kuma shi din mutum ne me kiyaye hakan,sai komai yazo masa da sauqi,har wani lokacin suna tsokanarsa da MR LOWERING GAZE. Wani lokaci su fada da turancin da dukkan su sun iyashi......wani lokaci kuma da yaren oromo din *Mr ilaalcha gadi buusuun*

Qasa tayi da kanta,hakan kuma bai hanata takowa zuwa inda suke din ba,saidai ta rage saurinta sosai.

Ta sanshi,sannan ta karanci abubuwa da yawa daga halayensa......wannan ya sanya dab da zasu isa ga junansu ta buda bakinta cikin nutsuwa.

"Assalamu alaikum" Ta fada da cikakkiyar sallama.

"Wa'alaikumussalam" Omari ya amsa yana niyyar wucewa,saidai tuni haisam ya riqe yatsunsa ya kuma dawo dashi baya.

"Barka da warhaka" Saami din ta fada tana dan duban sashen da omari yake. Fuska yadan sake mata,a iya shigowarsa gidan yasan saami.......da fari bai dauki wani abu game da samee din ba da yadda take girmama haisam da damuwa da lamuransa ba.......sannu a hankali ya fahimci akwai wani babban al'amari a game da haisam din a zuciyar yarinyar.

Tana da wata irin nutsuwa da kuma kamun kai..... Irin wadda ya jima bai ganta game da wata yarinya matashiyar budurwa me irin shekarunta ba.....wannan ya sanya shi kansa yake girmamata da kalar girmamawar da yaga haisam din yanayi mata.

"Barka da dare" Ta fada tana dan rusunawa haisam din ba tare data iya kallon fuskarsa ba.

"Barka.......ina zaki haka da daren nan a hanyar da ba jama'a?". Har tsakiyar zuciyarta taji tambayar da yayi matan.......yanayin yadda yayi tambayar da mamaki cikin muryarsa dake nuna da gaske baisan me ha fiddota zuwa ga hanyar ba a irin wannan lokacin.......bai fahimci ta fito bane kawai don ta samu ta ganshi ko yaya.......ta fito ne don ta kebanta dashi koda na daqiqa ashirinne.

Bata iya ce masa komai ba,saita miqa masa kwalin hannunta,duk kuwa da yadda kunya ke dawainiya da ita. Kwalin yabi da kallo a nutse kafin ya maida dubanshi ga fuskarsa. Yanaso yayi tambaya ne game da kwalin amma sai omari yayi masa riga malam masallaci ta hanyar sanya hannu ya dauke kwalin daga tafukan hannayenta.......hakan ya bata damar juyawa ta basu baya sannan tace.

"Saqo ne daga wata baiwar Allah" Daga haka ta soma takawa da hanzari tana bacewa ganinsu ta tsakanin wasu qananun bishiyoyi.

"Wani lokacin sai naga kamar ta bangaren aikinka da karatunka kawai kanka yake kawo wuta..... Kamar ta fanninsu kawai kake gane komai". Fararen manyan idanunsa dake tsakiyar rawaninsa ya zubawa omari.........kamar zaice wani abu sai kuma ya fasa.

"Tana buqatar ke kebe ne da ita fa.......kai kuma kayi kaman baka fahimta ba?......."

"Na fahimta mana omari.....na fahimta" Ya amsa masa yana soma takawa yana yin gaba ba tare daya damu da sanin meye a kwalin ba.

"Ba inda musulunci ya bamu daman kebewa nida ita irin hakan......ka manta ne omari?" Kai ya jinjina yana takowa don cin masa,duk da cewa hankalinsa yana kan kwalin daya dan budashi kadan yana leqa cikinsa.

"Amma ya kamata ka fahimta.......ya kamata ka gane me yarinyar nan ke nufi......ko baka fahimta ba har yanzu sai anyi maka fashin baqi?". Kansa ya girgiza yana kafe hanya da ido kamar meson gano wani abu.

" Na fahimta omari.......sameera sona takeyi.......so takemin irin na aure.....amma ni kuma........"

"Karka soma cemin samee batayi ba......zanyi abinda ban taba yi maka ba wato qaryataka......kamar yadda nasan kaima kayi abinda baka taba yi ba wato qarya" Miskilin murmushin nan nasa ya saki,yana ci gaba da takawa ba tare daya dubi omari ba. Sai da yaja fasali sosai sannan ya maida masa amsa.

"Tako ina samee tayi.......kamilar mace ma'abociyar addini.......mahaddaciya sittin da tafsir......wadda ta haddace litattafan addini masu tarin yawa,ba inda ta sani,daga gidansu sai makaranta.......sai nan gidan.......idanma akwai wani abu da samee bata cikashi ba......saidai cikar nan da ake cewa duk dan adam tara yake bai cika goma ba.......matsalar kawai ni dinne". Ya fada calmly har hakan na bayyana cikin maganarsa.

Dakatawa omari yayi cikin mamakinsa. Ya dauka dukka daya jero wadannan maganganun zai gaya masa cewa ya jima shima da fara son samee ko accepting nata.

"Kai din me?".

" Ban shirya soyayya ba......ban kuma taba jin son samee a zuciyata ba so irin na soyayya......donme zan bata mata lokacinta?" Ya qarashe maganar da sigar tambaya yana kuma waiwayowa gaba dayansa hannayensa zube a aljihunsa yana zubewa omari su.

Kallon kallo suka fara yi a tsakaninsu. Mamaki yana kashe omari.......yayin da haisam ke jiran ko zaiji wani qwaqwaran dalili da zai sanyashi bawa samee lokacinsa ko hankalinsa.

Gaba daya ya gama gogewa omari hadda,sai yaja jikinsa kadan ya zauna saman kujerun concrete dake kusa dashi.

"Sai yaushe kenan zaka shirya yin soyayyar......ka shirya kuma accepting wata?". Wannan boyayyen murmushin nasa dake cikin rawaninsa ya saki,ya kuma yi qas da kansa yana zubawa qananun fararen duwatsun da aka qawata wajen dasu idanu kamar yanason qididdige lokacin da zai jarrabawa wata macen ko ya bata dama a rayuwarsa.

"Not now omari......ba yanzu ba,ina da sauren abubuwa masu muhimmanci daya kamata na gama dasu omari".

"Haisam....." Omari ya kirashi a sanyaye yana aza dukka hannayensa saman kwalin..

"Ina jiye maka haqqin 'dubban 'yammatan da wannan shu'umin murmushin naka kadai ya jefa zuciyarsu kogin soyayya......ka kasa kuma taimaka musu da komai". Dole wannan karon murmushinsa ya fito da wani irin sauti.

" Laifina ne omari?......" Kasa bashi amsa omari yayi......dondai da gaske kai tsaye bazaice laifin haisam bane.......hasalima dukka cikinsu yafi kowa takatsantsan da lamarin mata,banda jaruma kuma tsayayyar zuciyar da sukasan yana da ita tabbas ba abinda zai hanashi soma kiransa da ME TSORON MATA.

Wani irin magnet ne cikin halittarsa dake fusgar hankalin 'yammata a kanshi........kusan dukkansu suna da irin wannan baiwar,amma nasa kaman yafi nasu zafi da yawa.

"Karkayi kwantai ko kayi zaben tumun dare fa?......" Omari ya fada yana fidda idanunsa waje. Kai kawai haisam keta girgizawa kaman dariya nason qwace masa,fararen jerarrun haqoransa da haskensu ya fita harta qyallen bakinsa suka bayyana.......a wannan karon sai da yakai hannun nasa ya zame qyallen zuwa wuyansa don ya bawa dariyarsa damar fitowa sosai.......wannan ya sanya qarashen cikamakin kaykkyawar fuskarsa damar bayyana gaba dayanta.

Wani lafiyayyen ajiyayyar baqa sidik din suma ce ta bayyana data gewaye habarsa da kumatunsa da wani iri qawataccen shape da zai gaya maka zallar qwarewa da sanin haqqin qasumba name askinsa. Kyawawan jajayen lips dinsa dake qyalli kamar an shafa musu man labba suka bayyana suna kuma sake zama ado ga jerarrun fararen haqoransa.

"Ba damuwa.......sai na jira sanda d'iyarka ta farko zata isa aure saika bani ita". Wani harara omari ya watsa masa.

"Ina ma ace akwai wani lafiyayyen abun bugu a nan?".

"Kana da hannu fa omari?......abun bugun me kake nema?" Ya tambayeshi yana dage masa girarsa dukka biyun,amsar bayarwa omari ya rasa,daya tabbatar da haka sai ya zare hannayensa daga aljihunsa ya hardesu a qirjinsa yaci gaba da tafiya zuwa ciki hankali kwance.

"Ko haka na zauna ba aure......Allah bazai tambayeni dalili ba.........muddin zan kare dokokinsa zan kuma tsare kaina......"

"Ba zaka iya ba.......na rantse da girman Allah kana cikin sahun mutanen da aure ya zame musu wajibi" Omari daya miqe da sauri ya fada yana kuma bin sahunsa. Dariyar mamaki ta sake kama haisam,amma saidai bai juyo ba.

"Zakayi kaffara omari......ka manta akwai manyan malaman da har suka rasu basuyi aure ba?......manya manyan malaman musulunci........ciki harda malamin mazhabar malikiyya imamu maalik?".

"Na sani......inajin kusan lokaci guda muka karanta littafin daya kawo sunayensu gaba daya......malaman da suka fifita karatu akan aure........amma sam baka sahunsu fa" Dif haisam din yayi masa ganin suna dab da fara shiga gurin jama'a,kuma zuwa sannan haisam yana jin bazai iya ci gaba da musayar magana da omari din ba.......don yana cikin abinda ke burge omari dama can suyita musayar ra'ayi.



zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*


*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer ๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ช*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261


*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA๐Ÿ‘‘*

*HUGUMANKU CE*โœ๐Ÿฝ

๐Ÿ’Ž *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*๐Ÿ’Ž


*H U G U M A*


PAGE 18



โ˜…โ˜…โ˜…Idan kaga yadda take shawagi cikin dokunan zaka rantse harda Allah ba diya mace bace,ba wasu alamu da zai nuna

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login