Showing 24001 words to 27000 words out of 178317 words

Chapter 9 - LU'ULU'U COMPLETE

Daga qasan qafafunta daya daga cikin hadimanta ne ke zaune sanye da kayan aikinsu,daga gefanta wasu irin plastic robber ne guda biyu. Dayan wani ruwa ne da momma din ta cire qafafunta daga ciki me launin kore,dayan kuma wasu ganyayyaki ne shimfide a ciki masu dumi sosai,dumin da ko daga gefe kake kana iya fahimtar hakan,wani qamshi na daban suka hadu suka bayar,ruwan da kuma ganyayyakin.

Gangar jikinta ce kawai zaune a wajen,amma dukka wani hakali nata da nutsuwarta basa wajen. Tun daga daren jiya sanda take fitowa daga sassan sultane bayan ta tabbatar sunyi magana ta fahimta tsakaninta dashi,take takowa ita daya zuwa sirrintacciyar hanyar da zata dawo da ita zuwa sassanta. Gilmawar wani abu ta gani wanda inuwarsa ta gifta ta gabanta sakamakon hasken qawayayen dake a bayanta suka cillo inuwar zuwa gabanta.

"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" Ta furta tana qoqarin danne tsoron daya taso mata. Tana da halittar tsoro a cikin zuciyarta kamar kowacce halitta ta dan adam,saidai kuma macace me wani irin dakiyar zuciya jarumta da kuma juriya ainun,wannan ya bata qarfin gwiwar juyawa don ganin meye haka me fadi ya gifta ta bayanta nesa kadan da ita.

Taku uku tayi baya tana komawa zuwa inda tafi tsammanin ta nan abun ya wuce. Sannu a hankali ta hangi rigar dake bayyana mata daya daga cikin hadiman dake aiki sassan mammina ne. Koda ta sake matsawa sosai sai idanunta suka soma dauko mata fuskar tamim wanda yake sake turata cikin hular qarfen dake saman kansa.

Cak ta tsaya tana dubansa daga tsakanin wasu shukoki da suka kerewa tsahonta sanda yake yunqurin fita daga hanyar zuwa qofar da zata sadashi da ainihin harabar sassan nasu daga nan kuma ya bulla zuwa makekiyar farfajiyar jakadunsu dama jakadun sarki.

Cak ya tsaya ya kuma waiwaya bayansa,yayi 'yan dube dubensa na wasu sakanni sannan ya sanya kansa da sassarfa yana ficewa.

Kimanin sakanni talatin cif tayi a wajen kafin ta motsa ta koma zuwa hanyar da zata sadata da ainihin sassanta.

"Me tamim yakeyi a shingen da ba wanda yake da hurumin shiga idan ba JININ sultane ba?......shiyyar data zama kebantacciya kuma mallakar iyalin sarki?.

Gabanta taji ya fadi sanda wani tunani ya yanko mata. Hankalinta taji yana neman tashi saboda tuna yadda wancan watan akayi shari'a tsakanin bayin dake aiki a sassan mammina da kuma bayi maza dake wata shiyya daban ta gidan. An samu case na alfasha tsanin baiwar mammina guda daya.....wanda har takai ga samun ciki a tsakaninsu.

Ba sultane kawai ba da baya qasar a sannan.......hatta ita hankalinta yayi mummunar tashin da sai datakai ta tara dukkan hadimanta tayi kafa musu mafi girman gargadin cewa.

"Duk wadda ke da buqatar aure a cikin ku ta sanarmin,ko a ina ta samu miji kuwa ni zan aurar da ita kamar yadda ake aurar da kowacce 'yantacciyar diya.........bazan daga qafa ba bazan kuma lamunci aikin alfasha a shiyyata ba......ina tsoron zunubin da zai jawo qin amsa addu'o'ina........duk wadda na sameta da wani abu makamancin haka.......bazanyi qasa a gwiwa ba wajen miqata kotun musulunci ta cikin gidannan ta yanke mata hukuncin da shari'a ta tana ba". Maganarta tayi amfani,don cikin watan mutum uku ta aurar,ta kuma basu daman ci gaba da aiki da ita ko tafiya?,dukkansu suka zabi suci gaba da aiki da ita,don babu abinda zaka rasa muddin kana tare da ita.

Can wani saqo dake kebance a zuciyarta kuma sai taji ta kasa gasgata haka......haka kawai taji ta gaza gamsuwa da wannan tunanin.......a jikinta takejin wani abu na daban,abinda ta kasa gane ko hasaso meye.......wannan tuna in kuma shine yaqi barinta yake bibiyarta har a wannan safiyar.

Idanunta zube saman fuskar akhnan dake shigowa da takun da sarauta da izza suka mallaka mata shi. Sanye take cikin wata irin doguwar riga da bazaka kirata baya kai tsaye ba. Don 'yar cikin tana da dogon hannu da wani irin ado daga hannun zuwa qasan rigar daga sama,yayi data saman ta kasance kamar alkyabba maras nauyi,budaddiya sosai da,wadda hannuwanta suka kasance kamar na top riga,aka cika dukka jikin rigar da wani irin ado,adon da idan ka baza fadinta sosai daga baya zai fi maka kama da adon zanen jikin dawisu,hatta da igiyar da akayi ta musamman saboda daure gaban rigar cike yake da ado da wasu irin stones masu daraja......sai wani qaramin hijab na musamman da rigar ke zuwa dashi,wanda itakacinsa wuya,wannan shi ya qarasa suturce jikinta gaba daya sai kewayayyar fuskarta data bayyana ta tsakiyar qaramin hijab din.

Idan akwai wani abu guda daya dake burge morsa safiyya akan akhnan shine SHIGAR SUTURCE jiki. Ta sani,tana suturce jikinta bawai don tasan darajar alfanu da girman abinda takeyi ba,aah.......tana suturceshi ne saboda girman kai taqama da alfahari da takeyi da jikin nata.

Tana kishi.......tana kuma alfahari da kanta...... Tana martaba jikinta tare da ganin cewa.....jikinta wata kadarace me tsada da tafi qarfin kowanne kare da doki ya samu damar ganin ta a raha haka,wannan ya sanya mafi yawan suturuntu irin rigunan ne da musamman wani kebantaccen kamfani dan qasar dubai ke fidda mata su iri daban daban,sai kuma lafiyayyu lafayu masu asalin tsada da daraja.

Tanason qananun kaya sosai......bata damu kuma da hijab ba bare dan kwali,amma dukka irin wannan shigar cikin gida takeyi. Sam momma ma bata tunanin akhnan din ta mallaki hijab,bare dankwali da yake zama aikin banza cikin dukkan kayanta.

Duk da batasan ma'anar suturta jiki ba cikin addininta........amma ta zame mata dabi'a saboda ALFAHARINTA DA IZZARTA.......wannan din yana yiwa momma dadi......tasan kuma wani abune daga Allah wanda yake iya kimsawa bawa kyakkyawar dabi'a koda shi bawan bai kalleta a mizanin komai ba.

"Barka da safiya" Akhnan din ta fada tana zama saman kilishin dake gaban momma din gami da dauke idanunta daga kan robobin da qafar momma din ke ciki.

Wani abune da tun batasan ma'anarsa da muhimmancinsa ba taga momma din tanayi,har kawo yau data mallaki hankalin kanta. Ita din wata irin mutum ce da bata bari kanta yayi murfi sam......mutum ce me yawan bincike game da duk abinda zata gani wanda batasan mene shi ba. Bata yarda da jahilci ba......bata kuma yarda da rashin sani ba,bata laminci kuma kowa ya kalleta a matsayin wadda bata sani ba.......saidai kash......tana tare da wani RASHIN SANI mafi muni da batasan dashi ba.

"Barka da asuba biftu,kin tashi lafiya?" Momma ta amsa da wani sassauqar murya. Baki akhnan ta tabe qasan ranta,tana dauko hoton abinda ya faru jiya tana kawoshi kusa da ranta.

Kamar ba itace matar nan ba data gaggaya mata maganganu mafiya muni cikin rayuwarta ba a jiyan.....tammar ba ita bace a jiyan takeyi kaman zata qonata da ruwan zafi ba......kamar ba itace ke jifanta da mummunar fata ba?,waisai gashi a safiyar yau ta juye kamar wata hawainiya?.

Sam bata jin zata ga hasken matar nan a rayuwarta kaf........kalamanta na jiya sun sake nesanta ruhinta da fatan wataqila watarana zasu fahimci inda kowannensu ya dosa.

"Na tashi lafiya......zan wuce Niamey......saina dawo" Ta fadi duka a tare da sauran maganarta tana miqewa.




*Zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*


*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261


*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽

💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎


*H U G U M A*


PAGE 10
____________________________
https://wa.link/l1gcz8
ASSALAMU ALAIKUM
Mutanen Zuzeam ventures
Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku
Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k
1. Rabin kazar mallaka 4500
2. ⁠married femfresh wash 2k
3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k
4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500
5. ⁠Tsimin mallaka 2500
6. ⁠maganin infection 1500
7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k
Duka kayan 19k za a baki akan 7500
Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k
Matsin maida tsohuwa yarinya 1k
Gumbar emergency 1k
Turaren mallaka 2k
Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼
Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki
____________________________




Da kallo morsa safiyya ta bita,tana jin wani abu yana taba zuciyarta sosai,wani irin qaqqarfan abu me matuqar tasiri a zuciya.

"Allah ya tsare hanya......ya bada sa'a,ki kula da kanki,ki kula da mutuncinki..........ki kuma tsare martabar gidanku data mahafinki" Kusan kowanne lokaci wadannan sune kalamanta kuma maganganunta a kanta a duk sanda ta samu sukunin yi mata sallama. Bata ce komai da ita ba taci gaba da takawa tana fita......hakan kuma bai hana morsa safiyya binta da idanuwa ba har sai data bacewa ganinta.

Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana jin sassan jikinta suna yin wani irin sanyi. Koda wasa akace mata irin haka zai taba gwada faruwa tsakaninta da jinin safeena ba shakka zata qaryata. Da gaske rayuwa wani mafarki ne na daban. Wani mafarki ne da zuciyoyi da ruhi keyi ba tare da samun yaqinin tabbatuwarsu a sanda ake kan ginasu ba. Safeenarta.......halitta mafi soyuwa a ruhinta dama kafatanin rayuwarta gaba daya......yanzun dama akwai sanda lokaci zaizo da irin wannan yanayin tsakaninta da jinin SAFEENA?.

Taja siririn tsaki aqalla ya kusa sau biyar kafin ta isa sassan mammina. Tarin hadiman dake sassan suka shiga marabtarta cikin matsanancin ban girma,saidai ba wanda ta samu amsawa. Hakan ba baqon abu bane a wajensu,musamman idan tana jin 'yan izzarta a kusa,ko kuma 'yan miskilancin suka motsa mata. Ko baya ga haka kuma dama ita din muryarta kamar wani abune me daraja a tare da ita da ba kowanne guri take sakinta ba.

"Ki gafarceni.......uwar daki tana cikin muhimmiyar ganawa......bata kuma bada izinin shigar kowa ba har sai bayan ta kammala" . Bayanan tafisu ta yiwa akhnan kenan,wadda ta isa direct ga qofar kebantaccen parlor din hajiya zaitun da tasan a lokaci irin wannan anfi samunta a can.

Wani irin kallo akhnan ta dago ta watsawa tafisu,tana mata wani duba na qanqanci da kuma zallar mamaki.

"Hala wani abunne a kanki?.......kinsan dawa kike magana kuwa?" Akhnan ta furta cikin izzar nan tata dake bayyana cikin kowanne motsi nata.

Rawa jikin tafisu ya dauka,kwarjinin akhnan din sosai ya daketa,ya kuma tarwatsa duk wata juriya da takejin tana da ita na tsaida akhnan din.

"Zaki fuskanci hukunci.......tabbas zaki fuskanci hukuncin tsaidani da kuma batamin lokaci da kikayi" Ta qarasa maganar tana tura qofar,daidai sanda tafisu ta zube muryarta da jikinta dukka suna rawa.

"Tuba nake.......afuwa nake nema ki yafeni......kiyimin rai".

Bata ko saurareta ba ta sanya kai cikin parlor dake da qofofi biyu na musamman,ta cikin gidan da kuma wata qofar daban ta bayan ainihin ginin.

"Yaya sunanshi?......." Kalaman mammina kenan da taji wanda bata ko ta kansu ba ta motsa bakinta a izzace ta saki siririyar sallama tana sauke idanunta ga faffadan mutumin dake duqe a gabanta kamar me neman gafara.

"Sunan......." Ya buda baki da nufin bada amsa tambayar da akayi masa,saidai amsa sallamar da yaji mammina tana yi ya dakatar dashi,ya kuma daga kansa da hanzari yana duban me shigowar. Sam baiji motsi ko sallamar kowa ba......don haka baisan da shigowar kowa din ba.

Idanu mammina ta kafeta dashi na sakannin da suka kusa biyar kafin ta sakar mata murmushi.

"Karkicemin sai tafiya?" Ta fadi tana marabtarta da hannayenta,abinda ya sanyata qarasowa cikin hanzari ta zauna jikin mammina din sosai tana aza kanta saman kafadarta.

"Maraba da isowa........tuba nake.... .Allah ya qara miki nisan kwana......ubangiji ya kauda maqiyanki daga duniyarn......"

"Ya isa haka" Mammina ta dakatar dashi tana sanya hannunta cikin na akhnan.

"Ka bamu guri haka nan......zan gana da diyata......zan nemaka wani lokaci"

"An gama Allah shi biya miki" Ya furta yana miqewa da dukka tsahonsa,sannan ya sanya kai yana fita ta qofar da zata fitar dashi ta bayan sassan mammina din.

Sai data tabbatar da gushewarsa a wajen,ba tare da wani motsi nasa ba sannan ta dubi akhnan.

"Tun daga yanzu na fara kewar wannan diyar tawa,daya daga cikin abinda ke jefani tunanin yadda rayuwa zata kasancemin bayan na kaita gidan mijinta". Wani murmushi ya subuce ma akhnan din,murmushi nan nata me tsadar da zai wahala kayi mu'amala da ita na wasu taqaitattun lokuta ka samu ganinsa. Koda yaushe fuskarta a tsuke take,zaka dauka kaf rayuwarta batasan wani abu waishi farinciki ba.

Hannunta ta zura ta bayan mammina ta rungumeta sosai.

"Kune kuka takura......ku kuka matsa mammina......me nake da buqata a rayuwata bayan kun yimin komai.....kun gama min komai......sannan kun mallakamin komai". Kai ta girgiza a hankali.

"Yaro yaro ne......yaro man kaza......baa nan gizo ke saqar ba.......amma na gaba kadan zaki fahimta......akwai wani abun da kike buqatar ki tafi dashi Niamey?.....bayi hadimai ma'aikata ko wani abu na buqatar rayuwa?". Manyan idanunta ta lumshe,tana jin dadin yadda take nuna damuwa da komai daya shafi rayuwarta,tana jin dadin yadda take kula da dukka buqatunta.......tasha banban da nisan tazara me tarin yawa tsakaninta da momma safiyya.........tazarar da bata jin a nan kusa akwai wani abu da zatayi wanda zai sanya ta taddota.

"Babu......babu komai mammina.......saidai zanyi kewarku" Ta qarasa fada tana sake dora kanta saman kafadarta.

"Muma zamuyi kewarki biftu.......amma zamu kasance ta cikin waya.........dole ne ya zame miki nauyi da kuma wajibi bawa kamfani kulawar da dukka ta dace........shine zuciyar duk wata kadara da dukiyarki akhnan........bake kadai ba.......hatta da me martaba ma". Kai ta jinjina,sannan a hankali ta zame kanta daga kafadar mammina din sannan ta miqe.

Da kanta ta bude mata seat din baya,mazauni na musamman dake gareta cikin lafiyayyar motar qirar BMW X5 fara qal wadda tasha banban da kalolin sauran motoci ukun dake dauke da masu tsaronta da kanyi mata rakiya zuwa Niamey,wasu su zauna a can,nacan din kuma su dawo nan agadez sai tayi wani zuwan sai a sake canza mata da wasu cikin amintattun hadiman da masarautar agadez ta aminta dasu.

"Allah ya tsaremin ke......ya kawar da dukkan wani abunqi"

"Ameen mammina". Ta fada a narke kaman yarinyar qarama. Matsawa mammina din tayi tayi kissing hannun akhnan din,sannan ta maida dubanta ga aisa.

" Aisa" Ta kirata kai tsaye da yanayin daba kasafai ta fiya kiranta ba.

"Naam mammina"

"Ki kulamin da diyata" Ta furta da yanayin dake nuna mata da gaske take. Kai kawai ta jinjinawa mammina din tana dauke kanta zuwa wani sashe na daban,kafin mammina ta matsa da baya ta rufe musu motar,suka fara motsawa kuma suna fara fita daga masarautar agadez. Duk inda zasu gifta da motocin tun daga cikin gidan har zuwa wajen gidan sai kowa ya bada hankalinsa,ya kuma matsa baya cikin girmamawa yana yi mata addu'ar sauka lafiya da wani irin ladabi tamkar tana ganinsu.

Shuru motar ta dauka sanda suke nufar mano dayak international airport(AJY),inda ta saba tashi a nan,sauran hadimanta kuma su juya subi ta hanya zuwa Niamey din.

Kowa da tunanin da yakeyi a ransa,saidai duk da haka waya ce a hannun aisa tana danne dannenta,wanda fiye da rabi chart takeyi ita da shehinaz da take bata tabbacin yau din ko gobe itama zata baro zinder ta shigo Niamey din. Akhnan kuwa idanunta nakan hanyoyi da shimfidaddun tituna kyawawa da suke wucewa. Cikin ranta take sake jinjinawa mahaifinta da mulkinsa,ya jawowa qasar agadez ci gaba masu tarin yawa,irin ci gaban da koda wadanda suka jima saman karagar mulkin basu samar da koda rabin rabin hakan ba.

Duk da wannan nazarin da takeyi hakan bai hana zuciyarta fadawa cikin tunani ba.....abubuwa da dama dake cunkushe a kwanyarta,tana kuma tunanin hanyar warwaresu.

Qaramin tsaki taja ciki ciki,a yanzu tana jin energy dinta dukka na aikinta......bata buqatar sulalar dashi da kwaranyar dashi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login