Showing 207001 words to 210000 words out of 237425 words
kai cire mata kodar kuma ya akai kika tabbatar cewar bata da koda?”
A
take na fara zana musu yadda komai ya faru. Har suka fara tambayana kamaninsa na bayyana musu da kuma inda asibitinsa take. Namijin ya nuna min hoton group din mutane a guri daya ya ce na nuna masa shi sai na nuna fuskarsa.
“Za mu mika wannan statement
din aga kungiyar likitoci reahen jiyar sokoto, su fara na su bincike kamin ya iso zuwa nan, and After that za mu dauki ke mu kai ki asibiti a sake miki hoto domin tabbatarwa”
Ta karasa tana kallon Nana. Sai ta gyada mata kai. Sannan ta juya sukai magan
a da sunan su sai kuma suka mana sallama suka fice tare da Abbah ni sai a lokacin ma na ke lura da Nasir ashe har da shi yana zaune a falo har ma dayan jikan Mai Martaba wanda suka zo da shi. Aliyu da Nasir suka bi bayan Abbah, aka bar mu ni da Mama murmus
hi na gani a fuskarta na san ba zai wuce na jindadi ba kamar yadda nima na na jidadin ganin cewar za a kwato mata hakkinta, na yi zaton maganar zata fara min sai na ji ta ce.
“Mai Martaba ya ce mu shirya duk abunda ya kamata a yau, gobe da safe za mu w
uce Lagos daga can za mu tafi gida”
“Waya fada wa”
“Yusuf ya fada min lokacin da suka shigo, kuma ina fatar kin fadawa mijinki”
“Eh na fada masa amman yanzu zan kara masa maganar”
“Ina jindadi sosai zan ki ga iyalina ni ma kuma zan sadu da su d
a kuma mahaifiyata bayan tsawon lokaci, na jidadi sosai, na jidadi marar misaltuwa kuma ina cikin jindadin”
Ta fada ya yaren buzanci idon na cika da kwalla.
RAHMA POV.
A hankali numfashinta yake shiga jikinta, idonta kulle hancinta kuma manne
da oxygen, ga wani katon tukuyar shakar numfashi da ke aje gefenta tare da wata nu'urar da ke taimaka mata tai numfashin, idonta a rufe suke amman hawaye masu zafi ne suke gangarowa daga cikin idonta da ke rufe zuwa gefen ko wane kuncin fuskarta.
Mommynta
tana zaune gefenta idonta ya sumbura sosai saboda kuka gaba daya ta fita daga hayyacinta kamar ita ce marar lafiyar ba Rahma ba. Samun koda yanzu abu ne mai wahala, domin sun saka nema har yanzu ba a dace ba, balle kuma yanzu da likitocin suka tabbatar mu
su da samun ta a dole matukar suna son yar su a raye cikin koshin lafiya.
Ba zata iya kallon yarta ta mutu ba, bayan tsawon lokacin data dauka tana jinya kuma tana son Rahma a cikin yayanta fiye da kowa, matukar aka kwana biyu ba a samu ba zata yarda a c
ire nata daya a dasawa Rahma ko da ko ita zata rasa ranta ne ko kuma lafiyarta, ba zata iya kallon Rahma ta bar duniya ba saboda rashin abunda zata iya samar mata ba, tunaninta da bakincikin mutuwar Rahma idan har ta Allah ta kasance ta san ita ma ba zai b
arta ta rayu ba. Da wannan kara kawai ta bata kodarta daya idan har zai yi, ita kanta ta san abubuwa sun yi ma Rahma yawa a yanzu, samun cikin Ataa, barinta da Aliyu yai ya auri wata, ga Kuma bullowar wannan lamarin na kakanta Ataa wanda ya zama karkashin
inuwarsa dukansu suke rayuwa, ta alfahari da bugun gaba ta kare.
*Ina mata son rage kiba? Ina mazan da kiba ta hana su sukuni? Ina masu jikin yai kyau kamar na yarinya? Ina masu fama da kujera ko wani ta bo a fuska? Ina masu fama da hawan jini? Ma
su diabetic? Ag cera an gwada yayi an tantance ingancin babu shakku ko kadan. AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake
rusa garkuwan jikin ita kanta.*
*Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun
hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon
mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://a
gnutritioninternational.com.*
*******
55
Ba mu koma gida ba sai dare, Nana ta yi ta nanata min lokacin da za mu tafi kamar yadda Mai Martaba ya fada mata, a hanya Aliyu ya tsaya ya siya mana ayaba kankana sannan muka isa gida. Sai ya ya faka motarsa
sannan na saki hannunsa na bude motar kamin na fito har ya zagoyo gefen da na ke ya karasa bude min ganbun motar. A hankali na sauko ina takawa yana rike da hannuna dayan hannunsa kuma rike da ledar da muka siyo ayaba.
“Mama ta ce nai tuna maka zancen
tafiyar mu fa”
Be ce min komai ba, har muka shiga falon sai ya zauna saman kujera ya janyo hannun na zauna saman jikinsa ya rumgume.
“Na sani ai, tare za mu tafi”
“Da gaske?”
Na fada cike da jindadi ina wara ido sai ya gyada min kai, rumgume s
hi nai na lafe a jikinsa kamar wata kyanwa yana shafa bayana a hankali. Mun dade a haka kamin mu koma daki, duk wani abu daya san zamu bukace shi a cikin daren ya hada mana shi, jaka daya ya hada mana kayanmu kamar yadda yai mana a wacan karon da za mu taf
i Las Vegas, misalin tara da rabi Nasir ya kawo masa maganin da aka rubutu asibiti, sun dade suna magana waje kamin su yi sallama ya dawo ciki.
A gado daya muka kwana kamar yadda muka saba ina cikin kirjinsa har sai da yunwar da dare ta fara damuna na
fito kitchen na dora indomie a cikin daren nan domin duk wani abu da ke nan bana sha'awar cinsa ba, ciki kuwa har da kayan marmarin dana ci jiya. Ina cikin zuba magi Aliyu ya shigo kitchen din, hannayensa ya dora a kafata taya ta tayani duba indomie a haka
har ta dafu muka ci tare sai ya fini cin ma.
“Ashe kai ma kana jin yunwar”
“Ba dole na ji yunwa ba”
“Ba ka ci abinci ba a gidan Mama Fulani?”
“Na ci”
Bayan mun gama ya kai plate din a kitchen, ni kuma na nufo dakin domin a falo muka ci abi
ncin indomie. Bathroom na shiga na yi fitsari ko da na fito yana rike da wayarsa da alama kira yake ko kuma karanta sako domin screen din wayar kawai yake kallo na tsawon lokaci sannan ya aje wayar ya zo bayana ya kwanta.
Washe gari da wuri na tashi f
iye da ko yaushe saboda marmarin tafiyar da za mu yi, Aliyu ne ya hada mana abun karyawa muka karya tare a dinning sannan na shiga bathroom din dakina nai wanka, na saka farin material marar nauyi kamar yadda ya umarce ni, na saka sarka da abun hannu na ma
nta rabon da nai kwallaiya da sarka tun ina karama a lokacin da Mahaifina yake raya ya siya min wata sarka a lokacin karamar sallah, sai kuma lokacin bikina da aka min kwaliya aka saka min sarka, sai kuma yau wani kwarji da kyau sarkar ta kara min kasancew
ar mai tsada har wani haske ba, kumatuna ya dan kumboro kamar ba nawa ba, mayan idanuwa sun kara fitowa sakamakon cikar da naman idona nai fari na karu sosai har wani shining na ke, ban tana lura da haka ba sai yau da nake kallon kaina a madubi. Murmushi m
ai wanda ya kara min kyau madaidaicin bakina ya kwanta dan jan bakina da na shafa ya kara fitowa, hannuna na kai na janyo gashina da nai parking a baya zuwa saman wuyana, sannan na dauki wayata ina daukar kaina hoto. Ta cikim madubi na hango Aliyu wanda ya
saka wani boyal sky blue kamar na nawa sai dai nawa yadi ne kalar ce kawai daya. Zuwa yai gabana ya tsuna tana ta kallon fuskata ni ko ina aika masa da murmushi mai kyau da saukar da natsuwa.
“Kalle ki Babyna kamar ba ke ba”
Wannan karon dariya nai
ya lumshe idona na bude, ni kaina ina jin cewar kamar ba ni ba ce, ta wani bangaren duk wani abu da ke ta yar min da hankali a yanzu babu shi, na samu rayuwar da ban taba mafarkin samu ba, kuma a cikin sauki ciki kuwa har da saduwar da Mama za tai yau da
iyala wanda shi yafi komai faranta min rai a yanzu, da kuma muhunta Asim da za ayi, ga kuma auren Aliyu wanda na san shi ma babban nasara ce a rayuwata domin har ga Allah ina jindadin yadda yake kula da ni yana nuna min kauna, babban abun fargaba ko damuwa
a rayuwar aure shi ne samun miji da baya baka kulawa ko kuma baya kaunarka, amman ni ina jin cewar na yi wannan dacen duk kuwa da ban san mi gaba zata haifa ba amman ina jin cewar Aliyu zai iya tsaya min a ko wane hali na samu kaina. Ta dayan bangarem kum
a ida na tuna yadda Allah ya daukaka daraja da martabata a take ta ba kuma ta hanyar kowa ba sai ta hanyar mahaifiyata wacce kowa ke gani a wulakance yana raina mu. Lallai bayan tsananni akwai dadi a tafe wani a kusa wani kuma a nesa, a duk inda duhu yake
a akwai haske, a tsoro na da rashin gatana na samu kwarin guiwa da gatan da ban yi tsammani ba. Idan na tuna farkon abunda nai ma Aliyu na fasa masa mota da ruwan da ya watsa min a tufafi sai abun ya bani mamaki kuma ya bani dariya, kamar ba mu ba, mutumen
da ke kyamar talaka yana ganin kamar ba su da raja yau shi ne a gabana a matsayin mijina har yake yabona ya fada min cewar yana kaunata.
Hannuna na ji an kama wanda hakam yasa na dawo daga duniyar tunanin da ke, agogon hannu ya saka min mai kyau sosai sa
nnan ya saka min wata tsarkar hannuna dake tare da agogon, sai yai ma hannun nawa kiss.
“I love you both”
Ya fada yana min wani lallausan murmushi mai kawata fuskarsa da siffar zatinsa. Goma saura muka fito tare da shi, ina rike da wani jakarta ta ra
yatawa shi kuma yana rike da karamin akwati kuma ya janyo babban, da kansa ya saka akwati bayan mota sannan ya bude min na shiga kamar yadda na sawa kaina a yanzu ko kuma na ce ya sabar min na bude min mota da kansa.
Tun kan yai horn ko yi ma motar ke
y mai gadin ya bude mana gate.
“Za mu tafiya zuwa Nijar yau, ban san tsawon yaushe za mu kai a can ba, amman dai ba za mu dade sosai ba, ka kula da gidan da komai, kuma karka bar kowa ya shiga ciki”
Ya fadawa mai gadin daidai lokacin daya tsayar da
motarsa a gurin da yake. Sannan ya bude wani guri a cikin motar ya dauko kudi masu dan dama ya mika masa.
“Ka siya abinci kuma ka yi wata lalurar idan ta taso”
Hannu biyu ya saka ya karba yana ta masa godiya sannan ya ja motar kuma nufi gidansu Mama
Fulani, kamin mu karasa har Mama Fulani ta kira shi a waya wai ana jiranmu.
A harabar gidan ya faka motarsa ta cikin motar ya miko hannu ya bude min kamin ya fita, muma fitowa muka nufi bangaren Mama Fulani tare da shi, a falo muka samu Maryam da Ruka
iya da Mama Fulani zaune, Aliyu ya fara sallama sannan ni ma nai, ta amsa mana ita da su Maryam sai dai bata kalli inda ake ba, na gaishe ta ban yi zaton zta amsa min ba na yi zaton yar jiya zata min sai na ji ta amsa min amman salaf da ita gishiri kamar b
a ita ba, ta wani sukuku kamar marar lafiya.
“Ya jikin naki Mama?”
“Al-hamdulillah, Tun dazun ake ta jiranku Ammy ta aiko sau biyu tana cewa na kira na fada maka wanda zai dauke ku ma ya zo”
“Okay, Ki yi Mama bankwana”
“Mama ina kike karanta b
ankwana sai mun dawo”
“Allah dawo da ku lafiya ya tsare”
Shine abunda kawai ta fada bayan an fada mata haka sannan ya mike tsaye ta nufi upstairs, Aliyu kuma ya kalli Maryam da Rukaiya dake zaune a saman kujera suna satar kallon mu.
“Allah ya kiy
aye ya tsare”
Ko wace su ta fada sannan muka fito daga bangarenta muka shiga bangaren Ammy, Mama da Ammy na zaune a falon da kuma Yusuf wato dan'uwana kuma jikan Mai Martaba wanda suka zo tare, Humaira ma na falon ita da Zee da ke ta aikin chatting. Mam
a na sanye da wata kamfala ja mai kyau sosai kana ganinta kasan mai tsada ce wacce na ke kyautata zaton Ammy ce ta bata domin bata zo da tufafin ba a lokacin da zata baro sokoto ta zo nan. Na gaisa da Ammy kamar yadda na saba Aliyu ma ya gaisa da ita sanna
n ya gaisa da Mama sai ya fita daga falon yana lasa waya, ni kuma na koma kusa da Mama na zauna.
“Ki gaishe shi mana”
Ta fada tana nuna min Yusuf da ke murmushi yana kallona, da yaren buzanci muka gaisa da shi yana amsa yana min wasar tabasai kamar d
aman can ya sani, ni dai ban rama ba domin ban san yadda na ke da shi. Tare da shi muka fito daga bangaren Ammy, hakan kuma be yi ma Aliyu dadi ba, na fahmcin hakan ne ta fuskarsa da na gani a daure yana ta aika min da harara kasa kasa. Kowa ya fito yana
mana Allah ya tsare sai mun dawo ciki kuwa har da Maryam da Rukaiya abun babu ko kunya, kuma babu sha'awar gani, ina kyautata zaton sun yi hakam ne saboda kar Aliyu ya ga laifinsu ko kuma Mama Fulani ce ta cilasta su domin ta san Yaran Ammay ma sai sun fit
o. Aliyu ya zauna gaba ni da Mama muka zauna baya, Yusuf yaja motar muka kama hanya, tsakanin ni da Mama aka rasa wane ya fi wani farinciki da zumudin ganin yan'uwan, ita da ta shekara ashirin rabonta da su ko kuwa ni da zan fara gaduwa da su a yau? Tun da
muka shiga motar ni da Mama da Yusuf ne kawai muke magana Mama da Yusuf na yi da yaren buzanci ni kuma sai na maida wata maganar da hausa saboda Aliyu, shi dai be ce uffan ba.
Da zahar muka isa lagos, wani kyakkyawan gida aka kai sauke mu, gida ne nada
idaicin mai kyau wanda aka kawata da shuke shuke gwanin sha'awa. A nan muka gaisa da Mai Martaba muka ci abinci muka huta sannan aka zo aka dauki mu aka tafi da mu wani gurin aka dauki hoton mu da tambarin yatsun mu akai wasu abubuwan da ban san ma'anarsu
ba sannan aka dawo da mu. Bayan mun dawo Aliyu ya kira Momy ya ba ni muka gaisa har ta ke ce min na kula da kaina kuma na gaishe da kowa da yake can, ya bawa Mama ita ma ta gaisa da ita sannan ya kira Daddynsa shi ma muka gaisa kamar yadda ya fara gaisawa
da shi, Abbah ya biyo baya shi da Mama Fulani sai a lokacin ya sanar musu mun iso lagos lafiya kalau.
Ba mu bar lagos ba sai da la'asar sannan muka shiga jirgin Mai martaba zuwa nijar, ni da Aliyu muna zaune a kujera daya daga can baya, Mama da Mai Martan
a kuma suna zaune a wata kujera mai kamar dinning wacce kowa ke iya kallon kowa ga wani dan karamin tebur a tsakani, bayan wadancan jikokin da ya zo da su wato Yusuf da kuma dayan da na ji Nana ta kira sunansa da Abdallah na ga su ma da ban san fuskarsu ba
sai yau. Ban san awa nawa ne daga nigeria to Nijar ba, mota balle kuma a jirgin sama, sai dai na yi bachi a cikin jirgin a kafadar Aliyu sau biyu ina farkawa sai kuma nai bachin, abincin da aka ba mu a jirgin kin ci nai duk kuwa da kasancewar na mu ne iri
n wanda na saba ci yau da kullum amman sai naji bana ma kaunar warin abinci. Aliyu ma Ginger tea kawai ya sha sai wani biscuit na alkama, ni dai ko ruwa da ban sakawa cikina ba har muka sauka. A nan ma akwai banbancin lokaci da can kamar dai yadda mukai wa
can tafiyar zuwa Las Vegas sai dai wannan ba tai nisa wacan ba ko kadar nisanta bata kamo ba, wata kila kuma saboda mun sauka da dare ne na ke ganin kamar lokacin da banbanci. Mama da Mai Martaba su suka fara fita daga jirgin tare da masu take masa baya wa
to fadawansa, sannan ni da Aliyu muka fito sai kuma sauran suka fito. Tun daga yanayin filin jirgin zaka fahimci ba a Nigeria kake ba, domin yawacan mutunen da suk can shigarsu