Showing 165001 words to 168000 words out of 184731 words

Chapter 56 - AMIR DA AMIRA complete

27 Aug 2026

13

har mukayi itama

tace saboda tashiga musulinci iyayen ta suka koreta daga Enugu cen ne garinsu , tace ku inane garinku

Shareef yace mu a cikin daji muke sosai sunan garinmu mai daji saboda bamuda makotan gari shiyasa suna saka mish

i suna mai daji ,

Ma tace to ku kwantar da hankalin ku nice maman ku kunji muje mu kwanta

Nan muka tashi kowa yanufo daki muka kwanta

Sosai mukejin dadin zama da ma dinmu dan da haka muke kiranta ma



Shareef yasamu ma yakai mata kudinsa yace yanason soma sana'a yagaji da zama haka gashi bashida takardun sa na school dasaiya nemi aiki ma to babu su

Ma tayi murna sosai daya zo mata da wannan shawarar shago

tabude mishi ta kara mishi kari ya ringa siyar da kayan masarufi hakan ba karamin dadi mukajiba

Ni kuma kullin ina gida idan nagaji da zaman gidan naje wajan ma na tayata siyar da abinci , taso ta maidani mak

aranta amma na nace mata kawai zanke tayata siyar da abinci ,, haka ta hakura ta kyaleni , naci gaba da siyar mata da abinci dan yanzu komai ni nakeyi kuma muna kara samun sabbin costumes hakan ba karamin dadi yayi

wa ma ba she saka mana albarka takeyi mu kuma muna jin dadin zama da ita

Wani lokacin nakanyi kukan rabuwata da ahalina ,, idan natunasu sainayi ta kuka ina tunanin ashe iyaye zasu iya rabuwa da diyansu akan wani

ra'ayin banza da wofi ,, shesu zabi gunki akan mu yaransu ,, ganin ina neman sakawa kaina damuwa yasa nayi watsi da tunanin su papa nace , insha Allah bazan sake tunani akan su papa ba ,, tinda ba kaunar mu sukeyi ba

harda zasu zabi wani abu akanmu

Haka mukaci gaba da rayuwa a wajan ma sosai shareef yake samun kudi , hakan yasa yabude account bank na soma tara kudi

Ma tace ya tara kudi yasiyo min kayan lefe sai yakawo

sadaki a daura mana aure

Shareef yaji dadi sosai nan yakara kaiminsa yana tara kudi

Ranar da muka cika shekara a wajan ma shareef yahadamin lefe yakawo kudin sadakina dubu talatin , sosai ma tayi farin ciki nan

,,ya kaiwa wani malamin anguwar mu sadakin aka daura mana aure nida shareef

Ranar munyi farin ciki sosai marar musaltuwa ma ta gaiyato kawayenta da abokan kasuwancin ta tace ,, tana yiwa yaranta biki

Sosai mutane ke

mamaki to ina tasamu yara bayan sun jima da sanin batada kowa ita kadai take

Wata kawar ta ta tambayeta mu suwaye ,, sai ma tace ai mu yaranta ne da haka sukabar maganar

Bayan ansha biki , ma da kanta tak

aine dakin shareef ,ta hadamu tamana nasiha mai ratsa zuciya tukun ta tafi

Tana fita shareef ya matso kusana yace maryam kinga ikon Allah ko ashe iyayenmu bazata ga aurenmu ba ,, Allah Allah yasaka wa ma da gidan aljan

na

Na amsa da ameen nan mukayi sallar miga godiya ga Allah daya mallaka ,, mana juna tukun muka kwanta

Haka mukaci gaba da rayuwar mu mai cike da farin ciki da jin dadi ,

Wata rana wadda bazan taba manta

wa ba a cikin tarishin rayuwar mu ,,,,wani mutum yazo wajan ma yaci abinci ,, amma yahana ta kudi

Aikuwa ma tace batasan ,zancen ba kullin saiyazo yaci abinci amma saiya gudu yau tace bai isaba saiya biyata kudinta



Ganin tana neman tara mishi jama'a ya kwance rigarsa ta tafi aguje

Ma tace kaci wuta bal bal nan tadawo kan abincin ta taci gaba da siyar wa

Bayan mundawo gida mun kwanta cen cikin dare aka diro mana

ta katanga ,, bamu ankara ba mukaji muryan ma tana basu hakuri

Da gudu tayo dakinmu tana huce ta dauko card din bankinta ,, ta jefowa shareef tace maza kubi wannan kofar tabaya ku tsere banason su tabaku ,, ninas

an kwanana yakare tana kuka

Da sauri muka rungume ta muna kuka nace ma ina zamuje kece uwarmu kece ubanmu yanzu idan muka barki ina zamuje ,, kawai muma su kashemu

Da sauri ta dagomu ta kalle mu tace wannan car

d dinane na banki idan kun tashi kuje kucire kudin duka dama bamai yawa bane na dauko jiya , tana fadin haka ta turamu ta wani kofa mai lungu ta kullemu

Haka munaji muna gani suka kashe ma dan kurma ihu shareef

yarufemun baki yana matseni ajikinsa ,, saida suka tafi tukun muka fito daga inda ma ta tura mu

Ina ganinta cikin jini na fadi sumanmiya sosai hankalin shareef yatashi ganin wannan mugun aiki

Baiyi wata wataba

ya kira nember police ya fada musu yan fashi sunzo gidanmu sun kashe mana mahaifiya

Yana kashewa ya dauko ruwa yazuba min ,, bayan na farfado , naringa kuka sainaje zan taba ma ,,sai shareef yace karna taba ta , idan

akaga shatin hannu na zaace nina kasheta ,, inajin hakan na hakura

Police suka kira shareef wacce anguwa suke nan yatura musu address din gidan ,,babu mata lokaci suka karaso

Inda ma take suka nufa nan aka s

oma bincike munsha tambaya dan wani ma cewa yayi mune muka akshe ta

Sosai naji tsoro saida akaga babu shatin hannun mu ajikinta tukun suka yadda bamu bane ,muka kashe ma ,, ga kukan da mukeyi nan akayi station damu



Gari na wayewa aka kai ma gidanta na gaskiya nayi kuka tamkar ruwan idona zai kare kullin ina dakinta ina kuka ,

Anyi ta bincike amma ankasa gano wannan yan fashin hakan yasa shareef yace kawai abar magana

r Allah zai isar mana

Kullin ina cikin damuwa da kuka duk na rame nafita hayyacina ,,haka yasa shima yashiga damuwar halin danake ciki

Ganin yashiga damuwa saina rage tawa ina danne ta haka mukaci gaba da ray

uwa agidan ma har Allah ya azirtamu da samun ciki sosai mukayi murna ,

Shareef ko kullin hirarshi babyn dake cikina hakan ba karamin dadi yaminba muma zamu karu nace idan na haifi mace zan saka mata sunan ma ,

Shareef yace to nan mukaci gaba da renon cikin

Cikina yanada wata biyar cikin dare wannan yan fashin suka sake dawowa gidanmu

Inda ma ta boyemu nan muka shiga muka kulle daga ciki kamar ba kowa

Shigowa dak

inmu sukayi sunata dibe dibe

Daya daga cikinsu yace oga nan gidan fa ba mutane nafada maka

Ogan yace injiwa akwai yaran ta shiyasa taki bamu kudin ta duka kila sun tafi wani wajan mukoma falo mujira zuwansu ,,

nan suka koma falo suka zauna kamar sun samu gidansu

Shareef yafito yadauko wayarshi yakoma inda nake ina kyerma rikeni yayi ya kiran police ,, yace inda suka kashe ma sunzo zasu kashemu nan sukace gasunan zuwa

Babu jimawa saiga kiransu yashigo wayar shareef , sukace kada mufito zasu shigo ahankali shesu kamasu ,, mukace to nan ya kashe wayar

Muna nan cen sai muji ana harbe harben bindigu sosai na tsorata , bayan wan

i lokaci muka ji shuru bude kofar dakinmu dan sandan yayi ya kira wayar shareef ,, nan muka fito yana rike dani

Barayin ankamasu nan nayi arba da wannan wanda sukayi fada da ma da sauri nace shine azzalimi ya ka

shemin mahaifiya ta dama kullin saiyazo yaci abinci yahanata kudi nan nabasu labarin fadansu ,, aka tasa keyarsu zuwa mota ,,ni kuma aka kaini asibiti saboda tsoron dana ji

Wasa wasa saida nayi sati a asibiti , ina

jinya nice harda karin jini

Bayan an sallamemu ne ,, mukaje zaman kotu saida akayi sati ana shari'a tukun aka gama yanke musu hukuncin kisa ta hanyar harbi

Sosai mukaji dadin wannan hukuncin ,, bayan mun fito m

ukaje mukawa loyanmu godiya shareef yabiyashi kudinsa amma yaki karba ,, yace ma tana da kima a wajan sa dan haka bazai amshi kudinmu ba nan muka mishi godiya zamu tafi

Yace am shareef dazakuji shawara ta dakun s

iyar da gidan nan kubarma garin gaba daya saboda ,,wannan mutanen suna da diya zasu iya koma muku

Godiya muka sake mishi nan muka dawo gida

Bayan kwana biyu muka samu malamin anguwar mu muka cemishi zamu siya

r da gidan , shima yace zai tashine yakoma kauyensu nan mukace zamu bishi cen kauyensu

Sosai yaji dadi yace muje inda ake siyar da gidaje , nan suka tafi da shareef ni kuma nakoma gida

Bayan kwana uku aka si

yar da gidan million daya saboda wulakanci a haka ma wai mai siyan yace sai an rage mishi ,, mlm yace sam kawai yasiya ahaka , tukun yabda milion daya

Haka muka tattara kayanmu na siyarwa muka siyar wanda zamu i

ya dauka muka dauko nan muka hau mutar katsina

Musha tafiya sosai nagaji kafin azo katsina tinda sassafe muke tafiya har dare tukun mukazo katsina

Shareef yakama bama dakin biyu a hotel din garin muka kwana

Da safe yabiya kudin mukaci abinci tukun muka kama hayar k'ankara babu dadewa mukaje garin mai kyau da tsari

Gidan malam Ahmed muka je matarshi ta tarbemu da murna ,,sosai ta nuna mana karamci ,hakan yamana dad

i harda malam kanshi

Ana mukaci gaba da renon cikin jikina har na haifi namiji sosai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login