Showing 183001 words to 184731 words out of 184731 words

Chapter 62 - AMIR DA AMIRA complete

27 Aug 2026

34

gidansu khadija

Baban khadija ya tarbesu da farin ciki ya shimfida musu taburma suka zauna aka gaisa sosai

Daddy ne yafada

mishi abinda yake tafe dasu ya nuna mishi alhaji hashim shine baban yaron da auri khadija

Sosai baban khadija yanuna farin cikin sa yace to inbanda abinka muhammed ai khadija yarka ce dagacen ma dasaiku bashi basai kun

zo neman izina ba khadija zatama jininku dama mu baki daya munzama yan uwan juna ba komai nabashi Khadija

Sosai su daddy sukayi farin ciki daddy yace za'a hada bikin dana hajara , Baban khadija yace bashida damuwa hakan ya

yi nan suka mishi sallama sukayo gidan basuko zauna fa suka juya zuwa kano

Suna zuwa gida bayan yahuta yafadawa su mommy komai itama ameera yakira yafada mata yadda sukayi

Ameera da daddy yafada mata har sujjadar g

odiya ga Allah Allah tayi ,shidai ameer kallon ta yayi yana jin yadda sonta da kaunarta ya mamaye dukkan sassan jikinsa , shima yataya farin ciki

Alhaji hashim na zuwa gida shima yafadawa mom din aliyu sosai tacika da

farin ciki itada aliyu

Yaune jamila tagama wanka ameera da fatima sukazo daukarta basu jimaba aka hada musu kayansu suka tafo gida baba direba yakawosu gida

Ameera da fatima suka tayata gyaran gida jamila ta shirya

kayansu ko ina suka gyara tsaf tukun suka mata sallama kowa yashiga part din sa

Akwana a tashi yau ne bikin su hajara

Ameera ce tafito da wani kofi a hannunta tana hade rai ta nufi dakin da amare suke

Ka

llon su tayi tace kunsandai bana wasa da yaro ko to kowacce ta amsa tashanye tinkafin na kira inna tazo

Da sauri khadija ta amsa tace nidai zansha aminiya ta basai kin kira inna ba ta kafa maganin abaki ta shanye tas



Wurgawa Hajara harara ameera tayi tace uwar yan taurin kai ki karba kisha anjima za'a yi diner so kike ana miki shiri wanda bazaiyi kyau ba

Kamar hajara zatayi kuka ta amsa tana runtse ido tashanye ta mikawa am

eera kofin , murmishi ameera tayi tace ko kufa wannan fa gata nake muku amma kuna min wulakanci irin na amare , dariya sukayi tukun tafita ta rufo musu kofar

Da misalin karfe 2:00 pm na ranar asabar aka daura auren *haja

ra ahmed da muhammed usama sai na khadija hambali da aliyu alhaji hashim* akan sadaki naira dubu dari biyu biyu , sosai anguwar tacika da mutane

Anan aka fadawa yan gidan an daura auren hajara ko kuka takama yi , ita

kuma khadija tagumi tayi tana kallon ta tace kefa garace hajara maimakon kiyi addu'a sai kike kuka

Hajara tace kukan farin ciki ne nakeyi ,Khadija tace kinga ni banyi kukanba

Hajara tace zakiyi aiba sosai kukayiba sh

iyasa bakiyi kukaba

Shuru khadija tayi tana jin maganar hajara

Da yamma aka shirya amare sunsha ado ga kyau kamar kasacesu ka gudu , fitowa sukayi a aka soma daukar kawayen amarya

Ni kuma ina tsaye ina dube

dube naga wata mota zan shiga sai naga tawagar *fans din ameer da ameera* ansha anko kowacce takashe nan aka shiga mota sai wajan diner

Sai kusan magarib aka tashi kowa yayo gida

Washe gari akayi walima da da da

re aka kai amare gidansu nasiha sosai aka musu tukun kowacce aka barta da mijinta (to hajara da khadija Allah yabada zaman lfy)

Bayan biki ameera da ameer hadda su umma duka dai family sukaje garinsu inna sosai ameera

taga canji duk sun musulinta anyi masallaci da

islamiya kowa kagani a garin abin burgewa hakan yakara faranta ran ameera da family ta

Kwana su goma tukun suka dawo gida aka cigaba da rayuwa mai dadi

BAYAN SHEKAR

A GOMA SHA BIYAR

Wata na gano tana saurin fitowa daga wani part da bulala a hannun ta tana bin wata karamar yarinya

Ita kuma yarinya taki tsayawa sai gudu takeyi

Shigowa akayi da gidan ya tifo da sauri ya t

areta ta dauke yace haba wifey wai ummin nawace zaki daka har kika sauri haka kuna tsare , hararar shi tayi tana fadin dama aikai kake daure mata gindi tana rashin ji to bazan daukaba

Tajuya tashiga ciki binta yayi

a falo yasameta tana kwashe kayan wasan data tara

Sunkuyawa yayi suka kwashe kafin yazauna yace mamana mai kikawa mommy naki

Yarinyar tace daddy wannan abun ne fa na zubar shine zata dakeni

Shafa kanta yayi

yace to shikenan kidena kinji ,da to ta amsa yace ina yayanki yake tace yana gidan granny dukansu dai kadai ce banje ba ,Ameer yace to jekiyi wasa zanyi wanka idan nadawo saimuje cen din ko

Tana fadin ameer ya ja

nyo ameera jikinsa yace duk fushin ne wifey na kefa yanzu kinzama babba kidena fushi

Dukan wasa takai mishi tace amma ai duk girmana a wajan ka ni yarinya ce

Kuncinta yaja yace hakane baby na muje kiyimin wanka

ko , tasukayi , sukayi daki zan shiga ameer yace koma ki huta maman nusy

Nace to

Tammat bihamdulillah anan na kawo karshen littafin *ameer da ameera* Allah yasa muyi anfani da darasin dake cikinsa , kuskuren dan

a yi Allah ka yafemin

Shin acikin wannan littafin wani guri yafi baki dariya

Wani waje yafi burgeki

Wani waje yafi baki haushi

Wani waje yafi baki tuasayi

Ina jiran amsar ku fans

πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

Muhadu daku a sabon novel dina mai sunan *hafsat*

*Takuce har kullin maman nusaiba

✍

🏻

*

*Nan zan tsaya*

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login